Sashe 41
Aalimah Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
******
Ya aka yi-ya-aka-yi? Cikin hira Aboubacar ya gaya wa Mahmoud zuwan Aalimah. Kwanansu bakwai sai ga shi a Kano. Gidansu na New site ya fara zuwa, inda aka gaya masa sun tashi. Ya kira Aboubacar a waya, shi ya kwatanta masa sabon gidansu da ke Sultan Road.
‘Yammatan biyu na zaune a falo sun dau wanka, kowacce da abin da ta ke yi. Basma tashar Arewa 24 ta ke kallo ana diramar Dadin Kowa, sosai abin ya dauki hankalinta yadda ake nuna typical Nigerian life da ba ta sani ba. Aalimah chatting suke yi da Abulkhair, wani abu da ya zame musu jiki tun zuwanta saboda ta roke shi kada ya kira ta ko sau daya, ba ta so Mama ta san akwai wani abu a tsakaninsu, za ta shiga damuwa a kan karatunta. Za ta yi tunanin ko ma ba karatu ta ke ba, tunda a gidansu ta ke.
Abulkhair ya fahimce ta, kuma shi ma yanzu ta kansa yake yi, ya shiga shekara ta biyun karshe a karatunsa, ko lokacin da yake chatting din da ita ma squeezing dinsa yake yi, saboda yana so ko me ta ke ciki ya sani, kada nisa ya nesanta shi da ita.
Aboubacar ya shigo, Mahmoud a bayansa, bayan sun yi sallama. Aalimah ta amsa ba tare da ta dago ba, komin canjin da rayuwa za ta kawo Mahmoud ba zai kasa gane Aalimah ba. Jikinta ne ya ba ta ana kallonta, kuma kamar yaya Aboubacar ba shi kadai ba ne ya shigo. Da sauri ta cira kai, suka yi ido hudu da Mahmoud. Sai da gabanta ya fadi, yana nan a yadda ta sanshi sai dan gogewa da ya yi. Yana sanye da shudiyar shadda kansa babu hula. Ajiyar zuciya ta yi ta janyo mayafinta a gefe ta lulluba, ya samu waje kusa da Aboubacar ya zauna, jikinsa a sanyaye. Yanzu ya kara tabbatarwa ya rasa Aalimah a bisa dalilai da dama.
Aboubacar da Basma sai kallon-kallo, kwana uku kenan bai shigo gidan ba sai yau a dalilin abokinsa ta ganshi. Aalimah ta rusuna ta gaida Mahmoud cike da jin wani irin nauyi domin har gobe Mahmoud mai kima ne a idanunta. Ba ta ji dadin abin da Abulkhair ya yi masa ba, wanda shine ya raba tsakaninsu, sannan bayan ya goge lambarsa daga wayarta ya yi masa kashedin sake kiranta ita din ba ta kara bi ta kansa ba, ko wajen Yaya Aboubacar ba ta karbi lambarsa ba. Idanunta sun rufe sun makance da soyayyar dan uwanta, wanda ya shigo cikin rayuwarta da wani irin karfin mulki, ya hana ta mallakar kowanne tunani sai nasa.
Hawaye ne suka ciko idanunta, “Ni mai laifi ce Mahmoud, ka yi hakuriâ€. Abin da ta iya furtawa gare shi kenan.
Murmushi Mahmoud ya yi, “I understand. Na dade da sanin haka za ta faru Aalimah. Shi ya sa na ce miki I’m scared da tafiyarki America. Da ni da ke duka babu mai iko da kansa ko zuciyarsa, sannan shi mijin aure rubutacce ne ga mace tun halittarta. Da ma ba ki yi min alkawarin ba za ki so kowa ba. Cewa ki ka yi you are hoping that destiny tied us together… to fatan bai karbu a wajen Ubangiji ba. Dan uwanki ya kira ni daga baya…â€
Da sauri Aalimah ta dago ta dube shi. Abulkhair wane irin mutum ne? Tsoronta Allah, tsoronta kada ya kasance zaginsa ya yi.
Mahmoud ya yi murmushi ganin yadda ta tsorata. Ya ce, “Abin da ki ke tunani ba shi ne ba. Rokona ya yi in sonki nake na yi masa alfarma na bar masa ke, don ya fi ni sonki. Sannan yana mai tabbatar min babu sauran muhallina a zuciyarkiâ€.
Aalimah ta dafe kai. Mahmoud ya ci gaba, fuskarsa dauke da murmushi.
“The guy is smart! Na kuma yi rantsuwa ni da kaina yana sonki. Na kuma yarda ya fi ni sonki. Na jinjina wa karfin zuciyarsa. Ina son mutum mai nuna kwanjinsa a kan macen da yake so. Ina yi muku fatan alheriâ€.
Aalimah sai ta ji hawaye sun sake ciko idonta. Mahmoud ya sanya hannu cikin aljihunsa ya fiddo abu cikin ambulan ya matsa ya mika wa Aalimah. Ta goge idonta ta karba, ta bude. Da sauri ta dube shi. Murmushi ya yi, “ni ma ‘yar uwata na nema. Na ga abin ya fi danko idan da alakar jini, kada in je wani waje in sake shan kaye a karo na biyuâ€.
Duk halin da ya sanya ta na tsananin tausayinsa, sai da ta yi murmushi. Katin daurin aurensa ne, sati biyu masu zuwa da cousin dinsa.
“Allah ya sanya alkhairi Mahmoud. Na gode, na gode. Ina kuma fatan hakan ba zai shafi tsakaninka da Yaya Aboubacar ba, ni kadai ce mai laifiâ€. Ta fada cikin sanyin murya.
Murmushi ya yi, ya ce, “Aboubacar ai ba ke ki ka hada mu ba, balle ki raba. Ki je ki ji da rigimammen saurayinki. Wannan in ya aure ki ki shirya shan kulle. Yana sonki fiye da kima, yana kishinki fiye da zatonki. Ni ma sakona gare shi ya gaggauta ya killace ki, in ba haka ba shi ma zai sha kaye, zai samu mai sonki fiye da shi. Saboda ke Aalimah daban ki ke. Soyayyarki ba ta yi wa maza sassaukan kamuâ€. Ya mike.
A zuciyar Aalimah ta ce, ‘ba amin ba, Abulkhair kawai nake so, daga nan har gaban abada!
Juyawar nan da za ta yi, Yaya Aboubacar ne da Basma, yana zaune a gabanta a kan kilishi, ita kuma tana kan kujera kamar dalibi gaban malaminsa. Maganganu suke yi kasa-kasa, wadanda daga su sai Ubangijinsu suka san me suke cewa. Mama ba ta gidan da ma, ta je asibitin Malam wanda ta ke zuwa duk karshen wata, su Sultana na makaranta.
“To kai yayan kwabo sai ka zo ka raka ni, zan tafiâ€. Mahmoud ya ce da Aboubacar yana kallon Basma cikin mamaki, sabida yadda idonsa ya rufe da ganin Aalimah bai ma lura da ko wace ce ba. Aalimah na da twin sister ne? Kai! That cannot be possible. Wannan ta fi ta aji, ta fi ta wankakken ido, me yiwuwa ‘yan uwan nasu ne na canâ€. Ya bai wa kansa amsa.
Aboubacar ya mike suka fita yana ce da Basma, “Ba doguwar rakiya zan yi masa ba, tasha zan kai shi ya hau motar Katsinaâ€.
Dariya Aalimah ta yi tana kallon Basma, wadda annuri kadai ke fita a fuskarta, da gani sun daidaita abin da suke ganin matsala ne a gare su. In wani ya gaya mata Aboubacar Mansour ne wannan a gaban mace ba za ta taba yarda ba. Hakika soyayya abu ce mai girma, mai birkita rayuwar ‘ya’ya maza fiye da mata.
Kafin hutunsu ya kare su koma U.S, hatta Daddyn su Aalimah ya san da soyayyar Aboubacar da Basma, ba Mama kadai ba. Sai dai cikin su duka babu wanda ya zura jiki cikin al’amarin a bisa dalilai kwarara da dama. Ido kawai suka zuba musu, suna ganin da ta koma shi kenan za su manta da juna.
Sun dawo Massachusetts ranar asabar, litinin suka koma makaranta.
6/28/21, 7:36 AM - Buhainat: â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©
💙💙💙💙💙â¤â¤â¤â¤â¤â¤â¤â¤â¤â¤ðŸ’›ðŸ’›ðŸ’›ðŸ’›ðŸ’›ðŸ’›ðŸ’›ðŸ’›ðŸ’›ðŸ’›ðŸ’›ðŸ’›ðŸ’•💕💕💕💕💕💕💕💕💕💕💕💕💕💕💓💓💓💓💓
Ya aka yi-ya-aka-yi? Cikin hira Aboubacar ya gaya wa Mahmoud zuwan Aalimah. Kwanansu bakwai sai ga shi a Kano. Gidansu na New site ya fara zuwa, inda aka gaya masa sun tashi. Ya kira Aboubacar a waya, shi ya kwatanta masa sabon gidansu da ke Sultan Road.
‘Yammatan biyu na zaune a falo sun dau wanka, kowacce da abin da ta ke yi. Basma tashar Arewa 24 ta ke kallo ana diramar Dadin Kowa, sosai abin ya dauki hankalinta yadda ake nuna typical Nigerian life da ba ta sani ba. Aalimah chatting suke yi da Abulkhair, wani abu da ya zame musu jiki tun zuwanta saboda ta roke shi kada ya kira ta ko sau daya, ba ta so Mama ta san akwai wani abu a tsakaninsu, za ta shiga damuwa a kan karatunta. Za ta yi tunanin ko ma ba karatu ta ke ba, tunda a gidansu ta ke.
Abulkhair ya fahimce ta, kuma shi ma yanzu ta kansa yake yi, ya shiga shekara ta biyun karshe a karatunsa, ko lokacin da yake chatting din da ita ma squeezing dinsa yake yi, saboda yana so ko me ta ke ciki ya sani, kada nisa ya nesanta shi da ita.
Aboubacar ya shigo, Mahmoud a bayansa, bayan sun yi sallama. Aalimah ta amsa ba tare da ta dago ba, komin canjin da rayuwa za ta kawo Mahmoud ba zai kasa gane Aalimah ba. Jikinta ne ya ba ta ana kallonta, kuma kamar yaya Aboubacar ba shi kadai ba ne ya shigo. Da sauri ta cira kai, suka yi ido hudu da Mahmoud. Sai da gabanta ya fadi, yana nan a yadda ta sanshi sai dan gogewa da ya yi. Yana sanye da shudiyar shadda kansa babu hula. Ajiyar zuciya ta yi ta janyo mayafinta a gefe ta lulluba, ya samu waje kusa da Aboubacar ya zauna, jikinsa a sanyaye. Yanzu ya kara tabbatarwa ya rasa Aalimah a bisa dalilai da dama.
Aboubacar da Basma sai kallon-kallo, kwana uku kenan bai shigo gidan ba sai yau a dalilin abokinsa ta ganshi. Aalimah ta rusuna ta gaida Mahmoud cike da jin wani irin nauyi domin har gobe Mahmoud mai kima ne a idanunta. Ba ta ji dadin abin da Abulkhair ya yi masa ba, wanda shine ya raba tsakaninsu, sannan bayan ya goge lambarsa daga wayarta ya yi masa kashedin sake kiranta ita din ba ta kara bi ta kansa ba, ko wajen Yaya Aboubacar ba ta karbi lambarsa ba. Idanunta sun rufe sun makance da soyayyar dan uwanta, wanda ya shigo cikin rayuwarta da wani irin karfin mulki, ya hana ta mallakar kowanne tunani sai nasa.
Hawaye ne suka ciko idanunta, “Ni mai laifi ce Mahmoud, ka yi hakuriâ€. Abin da ta iya furtawa gare shi kenan.
Murmushi Mahmoud ya yi, “I understand. Na dade da sanin haka za ta faru Aalimah. Shi ya sa na ce miki I’m scared da tafiyarki America. Da ni da ke duka babu mai iko da kansa ko zuciyarsa, sannan shi mijin aure rubutacce ne ga mace tun halittarta. Da ma ba ki yi min alkawarin ba za ki so kowa ba. Cewa ki ka yi you are hoping that destiny tied us together… to fatan bai karbu a wajen Ubangiji ba. Dan uwanki ya kira ni daga baya…â€
Da sauri Aalimah ta dago ta dube shi. Abulkhair wane irin mutum ne? Tsoronta Allah, tsoronta kada ya kasance zaginsa ya yi.
Mahmoud ya yi murmushi ganin yadda ta tsorata. Ya ce, “Abin da ki ke tunani ba shi ne ba. Rokona ya yi in sonki nake na yi masa alfarma na bar masa ke, don ya fi ni sonki. Sannan yana mai tabbatar min babu sauran muhallina a zuciyarkiâ€.
Aalimah ta dafe kai. Mahmoud ya ci gaba, fuskarsa dauke da murmushi.
“The guy is smart! Na kuma yi rantsuwa ni da kaina yana sonki. Na kuma yarda ya fi ni sonki. Na jinjina wa karfin zuciyarsa. Ina son mutum mai nuna kwanjinsa a kan macen da yake so. Ina yi muku fatan alheriâ€.
Aalimah sai ta ji hawaye sun sake ciko idonta. Mahmoud ya sanya hannu cikin aljihunsa ya fiddo abu cikin ambulan ya matsa ya mika wa Aalimah. Ta goge idonta ta karba, ta bude. Da sauri ta dube shi. Murmushi ya yi, “ni ma ‘yar uwata na nema. Na ga abin ya fi danko idan da alakar jini, kada in je wani waje in sake shan kaye a karo na biyuâ€.
Duk halin da ya sanya ta na tsananin tausayinsa, sai da ta yi murmushi. Katin daurin aurensa ne, sati biyu masu zuwa da cousin dinsa.
“Allah ya sanya alkhairi Mahmoud. Na gode, na gode. Ina kuma fatan hakan ba zai shafi tsakaninka da Yaya Aboubacar ba, ni kadai ce mai laifiâ€. Ta fada cikin sanyin murya.
Murmushi ya yi, ya ce, “Aboubacar ai ba ke ki ka hada mu ba, balle ki raba. Ki je ki ji da rigimammen saurayinki. Wannan in ya aure ki ki shirya shan kulle. Yana sonki fiye da kima, yana kishinki fiye da zatonki. Ni ma sakona gare shi ya gaggauta ya killace ki, in ba haka ba shi ma zai sha kaye, zai samu mai sonki fiye da shi. Saboda ke Aalimah daban ki ke. Soyayyarki ba ta yi wa maza sassaukan kamuâ€. Ya mike.
A zuciyar Aalimah ta ce, ‘ba amin ba, Abulkhair kawai nake so, daga nan har gaban abada!
Juyawar nan da za ta yi, Yaya Aboubacar ne da Basma, yana zaune a gabanta a kan kilishi, ita kuma tana kan kujera kamar dalibi gaban malaminsa. Maganganu suke yi kasa-kasa, wadanda daga su sai Ubangijinsu suka san me suke cewa. Mama ba ta gidan da ma, ta je asibitin Malam wanda ta ke zuwa duk karshen wata, su Sultana na makaranta.
“To kai yayan kwabo sai ka zo ka raka ni, zan tafiâ€. Mahmoud ya ce da Aboubacar yana kallon Basma cikin mamaki, sabida yadda idonsa ya rufe da ganin Aalimah bai ma lura da ko wace ce ba. Aalimah na da twin sister ne? Kai! That cannot be possible. Wannan ta fi ta aji, ta fi ta wankakken ido, me yiwuwa ‘yan uwan nasu ne na canâ€. Ya bai wa kansa amsa.
Aboubacar ya mike suka fita yana ce da Basma, “Ba doguwar rakiya zan yi masa ba, tasha zan kai shi ya hau motar Katsinaâ€.
Dariya Aalimah ta yi tana kallon Basma, wadda annuri kadai ke fita a fuskarta, da gani sun daidaita abin da suke ganin matsala ne a gare su. In wani ya gaya mata Aboubacar Mansour ne wannan a gaban mace ba za ta taba yarda ba. Hakika soyayya abu ce mai girma, mai birkita rayuwar ‘ya’ya maza fiye da mata.
Kafin hutunsu ya kare su koma U.S, hatta Daddyn su Aalimah ya san da soyayyar Aboubacar da Basma, ba Mama kadai ba. Sai dai cikin su duka babu wanda ya zura jiki cikin al’amarin a bisa dalilai kwarara da dama. Ido kawai suka zuba musu, suna ganin da ta koma shi kenan za su manta da juna.
Sun dawo Massachusetts ranar asabar, litinin suka koma makaranta.
6/28/21, 7:36 AM - Buhainat: â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©â‚©
💙💙💙💙💙â¤â¤â¤â¤â¤â¤â¤â¤â¤â¤ðŸ’›ðŸ’›ðŸ’›ðŸ’›ðŸ’›ðŸ’›ðŸ’›ðŸ’›ðŸ’›ðŸ’›ðŸ’›ðŸ’›ðŸ’•💕💕💕💕💕💕💕💕💕💕💕💕💕💕💓💓💓💓💓