Sashe 55
Aalimah Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Sanda suka iso karfe goma sha biyu na dare Aboubacar na kofar gida. Kasa fitowa daga motar suka yi dukkansu duk da sanin da suke da shi na cewa Aboubacar zai iya hango su ta glass. Hannunsa ya dora a kan cikinta yana sauraron harbawar jaririn yana lumshe idanu ya ce, “Kin san wani abu?â€
Girgiza kai ta yi, haka kawai ta ji ranta ba dadi, kamar su koma gidan Basman su kwana tare. In ya tafi Niger ita da ganinsa sai nan da kwana goma in an gama bikin Khaleesat, sannan ne zai zo su koma. Ba lokaci daya za su tashi da ‘yan Massachusetts ba, su sai nan da sati biyu. Ko dai ta kyale Basma ne ta bi mijinta ga kyawawan ‘yammatan nan na zuri’arsu da ba ta san iyaka wadanda za su kalle mata shi ba? Wani bala’e’en kishi ya turnuke ta irin wanda ba ta taba sanin tana da shi ba. Sabida a inda suke rayuwa ba ruwansu da irin wadannan abubuwan kowa da life-partner dinshi ba mai shiga gonar wani. Ta girgiza kai, ba tare da ya fahimci tunanin da ta ke ba, ya ce, “In namiji ki ka haifa ‘MU’AZZAM zan sa masa, in mace ce, ‘AALIMAH’ (mai ilmi) yadda zan ji dadin gaya mata how sweet and loving her mum is, how helping and generous she is, how much I truly love her and the long time I spend waiting to marry her. Duka zan gaya mata Aalimah, idan kuma namiji ne zan gaya masa yadda na rayu cikin soyayyar dan uwana mai lalura, yadda nake sonsa da burin samun lafiyarsa. Yadda ya kyautata wa rayuwata, ya tsaya min against all odds. Ya mayar da ni abin da nake a yau; Aboulkhair mai rayuwa da tsayayyun kafafu mamallakin Aalimah. Har ga shi za ta samar da Da a gare mu ni da Mu’azzam…â€
A lokacin ya ankara Aalimah kuka ta ke yi.
“Mon Amour na fasa zama, tare za mu tafiâ€.
Dan tsayawa ya yi yana nazarinta gabadaya ta birkice kamar ba ita ba. Nazarin maganganun da ya furta yake yi, ko akwai na tashin hankali a ciki? Iyakar tunaninsa bai gani ba. Kuka ta ke yi shabe-shabe da hawaye da majina. Janyo ta ya yi jikinsa, ya ce, “Aalimahâ€. Sunanta na hakika.
“Nda’amâ€. Ta amsa cikin rishin kuka, don rabon da ta ji ya kira ta tun zamanin samartaka (‘yammatancinsu).
“me na fada wanda ya bata miki rai?â€
“Babu komaiâ€. Ta amsa da sauri.
“To me ya sa za ki canza shawara cewa sai kin je Niger? You are kidding. Kada ki dauka ban san halin da ki ke ciki ba, ko daga kumburarrun kafafunki. Kina wasa ne ma da ki ke tunanin zan barki ki shiga kujiba-kujibar bikin nan na Niger, ki je kina girkin roti da rawa a wajen cocktail, ki jawo min asarar da ban taba shirya mata ba! Don haka ki saki ranki kawai mu yi rabuwar arziki ko a yi ta tsiya-tsiyaâ€.
Ba ta san sanda murmushi ya kubuce mata ba, ga hawaye face-face a fuskarta. Ba ta yi aune ba ta ji Aboulkhair ya rungume ta, sai saukar harshensa a fuskarta yana dauke hawayen salla-salla daga kan fuskarta. Idanun kuwa har wani side su yake yi.
Aboubacar da ke gefe yana waya da Basma yana jiran Aboulkhair ya sallami Aalimah su tafi, gefen idanunsa ya dan hasko masa abin da ke faruwa. Da sauri ya yi cikin gida yana bai wa Basma labari, ta kai yatsunta ta rufe fuskarta wai tana ji masa kunyar abin da ya gano. Sai jinsa ta yi a nata kumatun yana fadin, “Bari in nuna miki yadda suke yiâ€.
Aboukhair da Aalimah ba su rabu ba sai karfe daya daidai na dare. Tana tafiya zuwa cikin gida tana waiwayonsa da murmushi, yana tsaye jikin motar Aboubacar shi ma murmushin ya ke mata. In ba ta yi kuskure ba ba ta taba ganin irin wannan kasaitaccen murmushin daga gare shi ba.
*****
Daddyn Aalimah, Daddyn Aboulkhair, Aboubacar da Aboulkhair afilin jirgin saman Malam Aminu Kano, fuskokinsu cike da takaici da bacin rai. Wai babu jirgi mai zuwa Niamey a yau sakamakon lalacewar jirgin da suka yi booking din a safiyar yau, yana can Niamey ma bai taso ba ana gyara shi.
Aboubacar ya duba agogon hannunsa, ya ce, “Daddy, da wannan zaman cinye lokacin da muke gara mu je mu bi mota. Tafiyar awanni goma sha biyu cif nan gaba za ta kai mu Niamey. Yanzu karfe takwas na safe, in muka yi sauri muka dauki hanya zuwa tara na safe za mu isa Niamey nan da karfe tara na dare. Za kuma mu samu daurin aure a kan lokaciâ€.
Duk sun yi na’am da wannan shawarar, Daddyn Aboulkhair ya ce, “Aboulkhair is a very good driver, na tabbata kafin lokacin ma mun isaâ€.
A gurguje suka dawo gida suka yi wa Mama bayanin canjin da aka samu. Ba su bata lokaci ba suka dauki sabuwar motar Dr. Mansour kirar Jeep 2015 model, Aboulkhair ya tada ita suka shisshigar da kayansu, sannan Aboubacar ya shiga gaba, iyayen suna baya su biyu. Ko su Aalimah ba su san da wannan sauyin da aka samu ba, ba sa gidan dukkaninsu tun sassafe, ta raka Basma asibiti, Hassana (Zulaiha) na fama da mura, Hussainar sunan mama aka sa mata (Aseeya).
Sai da suka shiga gidan mai suka yi full tank, sannan suka dauki hanyar jamhuriyyar Niger.
******
Mummunan hadarin motar ya afku ne kafin a kai boarder din da ta raba iyakar kasar Najeriya da jamhuriyyar Nijar, bayan sun tsallake garin Jibiya sun shiga boarder din kasar Nijar.
Wasu gungun fulani ne makiyaya suka koro shanu a kan titin za su tsallaka. Ga direban Jeep din ya kwararo motar da gudu irin na neman biyan bukata. Burinsa su shiga Niger kawai kafin azahar a kalla ya san suna cikin kasar ainahinta, inyaso su yi sallah su ci abinci su durfafi Niamey ba tare da sun bata lokaci ba.
Shanun sun taho fal da gudunsu, shi ma ya shararo motar, sai ya ga bari ya dauke kan motar da azama tunda daya titin babu mota ko daya, ba tare da lura da cewa wata karamar mota ta taho ita ma a guje ta bayansa ba, kawai ta ga motar a kan nata titin ba tare da ta tsammata ko ta ankara ba. Kafin direban karamar motar ya yi tunanin abin yi, ya yi mugun taho-mu-gama da bakar Jeep din wanda hakan ya sanya duka motocin biyu fara katantanwa a tsakiyar babban titin kafin a karshe su duka biyun su hantsila wani katon rami a gefen titin. Ba ka jin komai sai hailala da salatin mutanen da ke cikin motocin cikin mika wuya ga hukuncin mahaliccinsu.
Girgiza kai ta yi, haka kawai ta ji ranta ba dadi, kamar su koma gidan Basman su kwana tare. In ya tafi Niger ita da ganinsa sai nan da kwana goma in an gama bikin Khaleesat, sannan ne zai zo su koma. Ba lokaci daya za su tashi da ‘yan Massachusetts ba, su sai nan da sati biyu. Ko dai ta kyale Basma ne ta bi mijinta ga kyawawan ‘yammatan nan na zuri’arsu da ba ta san iyaka wadanda za su kalle mata shi ba? Wani bala’e’en kishi ya turnuke ta irin wanda ba ta taba sanin tana da shi ba. Sabida a inda suke rayuwa ba ruwansu da irin wadannan abubuwan kowa da life-partner dinshi ba mai shiga gonar wani. Ta girgiza kai, ba tare da ya fahimci tunanin da ta ke ba, ya ce, “In namiji ki ka haifa ‘MU’AZZAM zan sa masa, in mace ce, ‘AALIMAH’ (mai ilmi) yadda zan ji dadin gaya mata how sweet and loving her mum is, how helping and generous she is, how much I truly love her and the long time I spend waiting to marry her. Duka zan gaya mata Aalimah, idan kuma namiji ne zan gaya masa yadda na rayu cikin soyayyar dan uwana mai lalura, yadda nake sonsa da burin samun lafiyarsa. Yadda ya kyautata wa rayuwata, ya tsaya min against all odds. Ya mayar da ni abin da nake a yau; Aboulkhair mai rayuwa da tsayayyun kafafu mamallakin Aalimah. Har ga shi za ta samar da Da a gare mu ni da Mu’azzam…â€
A lokacin ya ankara Aalimah kuka ta ke yi.
“Mon Amour na fasa zama, tare za mu tafiâ€.
Dan tsayawa ya yi yana nazarinta gabadaya ta birkice kamar ba ita ba. Nazarin maganganun da ya furta yake yi, ko akwai na tashin hankali a ciki? Iyakar tunaninsa bai gani ba. Kuka ta ke yi shabe-shabe da hawaye da majina. Janyo ta ya yi jikinsa, ya ce, “Aalimahâ€. Sunanta na hakika.
“Nda’amâ€. Ta amsa cikin rishin kuka, don rabon da ta ji ya kira ta tun zamanin samartaka (‘yammatancinsu).
“me na fada wanda ya bata miki rai?â€
“Babu komaiâ€. Ta amsa da sauri.
“To me ya sa za ki canza shawara cewa sai kin je Niger? You are kidding. Kada ki dauka ban san halin da ki ke ciki ba, ko daga kumburarrun kafafunki. Kina wasa ne ma da ki ke tunanin zan barki ki shiga kujiba-kujibar bikin nan na Niger, ki je kina girkin roti da rawa a wajen cocktail, ki jawo min asarar da ban taba shirya mata ba! Don haka ki saki ranki kawai mu yi rabuwar arziki ko a yi ta tsiya-tsiyaâ€.
Ba ta san sanda murmushi ya kubuce mata ba, ga hawaye face-face a fuskarta. Ba ta yi aune ba ta ji Aboulkhair ya rungume ta, sai saukar harshensa a fuskarta yana dauke hawayen salla-salla daga kan fuskarta. Idanun kuwa har wani side su yake yi.
Aboubacar da ke gefe yana waya da Basma yana jiran Aboulkhair ya sallami Aalimah su tafi, gefen idanunsa ya dan hasko masa abin da ke faruwa. Da sauri ya yi cikin gida yana bai wa Basma labari, ta kai yatsunta ta rufe fuskarta wai tana ji masa kunyar abin da ya gano. Sai jinsa ta yi a nata kumatun yana fadin, “Bari in nuna miki yadda suke yiâ€.
Aboukhair da Aalimah ba su rabu ba sai karfe daya daidai na dare. Tana tafiya zuwa cikin gida tana waiwayonsa da murmushi, yana tsaye jikin motar Aboubacar shi ma murmushin ya ke mata. In ba ta yi kuskure ba ba ta taba ganin irin wannan kasaitaccen murmushin daga gare shi ba.
*****
Daddyn Aalimah, Daddyn Aboulkhair, Aboubacar da Aboulkhair afilin jirgin saman Malam Aminu Kano, fuskokinsu cike da takaici da bacin rai. Wai babu jirgi mai zuwa Niamey a yau sakamakon lalacewar jirgin da suka yi booking din a safiyar yau, yana can Niamey ma bai taso ba ana gyara shi.
Aboubacar ya duba agogon hannunsa, ya ce, “Daddy, da wannan zaman cinye lokacin da muke gara mu je mu bi mota. Tafiyar awanni goma sha biyu cif nan gaba za ta kai mu Niamey. Yanzu karfe takwas na safe, in muka yi sauri muka dauki hanya zuwa tara na safe za mu isa Niamey nan da karfe tara na dare. Za kuma mu samu daurin aure a kan lokaciâ€.
Duk sun yi na’am da wannan shawarar, Daddyn Aboulkhair ya ce, “Aboulkhair is a very good driver, na tabbata kafin lokacin ma mun isaâ€.
A gurguje suka dawo gida suka yi wa Mama bayanin canjin da aka samu. Ba su bata lokaci ba suka dauki sabuwar motar Dr. Mansour kirar Jeep 2015 model, Aboulkhair ya tada ita suka shisshigar da kayansu, sannan Aboubacar ya shiga gaba, iyayen suna baya su biyu. Ko su Aalimah ba su san da wannan sauyin da aka samu ba, ba sa gidan dukkaninsu tun sassafe, ta raka Basma asibiti, Hassana (Zulaiha) na fama da mura, Hussainar sunan mama aka sa mata (Aseeya).
Sai da suka shiga gidan mai suka yi full tank, sannan suka dauki hanyar jamhuriyyar Niger.
******
Mummunan hadarin motar ya afku ne kafin a kai boarder din da ta raba iyakar kasar Najeriya da jamhuriyyar Nijar, bayan sun tsallake garin Jibiya sun shiga boarder din kasar Nijar.
Wasu gungun fulani ne makiyaya suka koro shanu a kan titin za su tsallaka. Ga direban Jeep din ya kwararo motar da gudu irin na neman biyan bukata. Burinsa su shiga Niger kawai kafin azahar a kalla ya san suna cikin kasar ainahinta, inyaso su yi sallah su ci abinci su durfafi Niamey ba tare da sun bata lokaci ba.
Shanun sun taho fal da gudunsu, shi ma ya shararo motar, sai ya ga bari ya dauke kan motar da azama tunda daya titin babu mota ko daya, ba tare da lura da cewa wata karamar mota ta taho ita ma a guje ta bayansa ba, kawai ta ga motar a kan nata titin ba tare da ta tsammata ko ta ankara ba. Kafin direban karamar motar ya yi tunanin abin yi, ya yi mugun taho-mu-gama da bakar Jeep din wanda hakan ya sanya duka motocin biyu fara katantanwa a tsakiyar babban titin kafin a karshe su duka biyun su hantsila wani katon rami a gefen titin. Ba ka jin komai sai hailala da salatin mutanen da ke cikin motocin cikin mika wuya ga hukuncin mahaliccinsu.