Sashe 64
Aalimah Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
“Daure ki sha, ko kurba uku ne kin ji?â€
Juyar da kai ta yi cikin son fashewa da kuka. Mama ta sake komawa barin da ta juyar da kan cike da damuwa da kofin mug na tangaran a hannunta mai cike da kunun kanwa.
“Kin san jikinki jikin jego ne Aalimah, ki dinga shan kunun nan ko da ba za ki ci komai ba bayan shi. A ce magana daya kullum sai an yi ta nanata ta kamar cin kwan makauniya?â€
Fuska ta sanya cikin tafukanta biyu ta fara wani irin kuka. Wanda ke tasowa tun daga karkashin zuciyar ta. Sautin sa na mai bayyana halin kunci da ragaita da zuciyarta ke ciki.
“Ni Mama ki rabu da ni, don Allah ki kyaleniâ€. Ta furta cikin wata murya mai ban tausayi.
Daidai lokacin da likitar da ke kula da ita ta bude kofa ta shigo da Nurse biye da ita. Cikin sakin fuska ta isa gaban gadon da Aalimahn ta ke, inda sabo sun saba da wannan kukan na Aalimah tun kwantar da ita a asibitin. Gata bata jin lallashi. Tausayi dattijuwar take bata sabida yadda ta damu da ‘yar tata. Ta karbi kofin daga hannun Mama, ta cire hannun Aalimah daga fuskarta, wanda tuni ya jike sharab da hawaye.
“Mrs. Aboulkhair ba sai na sake maimaitawa ba, jikinki yana bukatar sinadarin abinci mai gina jiki, kada ki manta ‘Da’ aka cire a jikinki ba karamin ciki ba. Ki rage wa Maman ki da ‘yar uwarki damuwa ki dinga cin abinci kin ji?
Allah ba ya dora wa rai abin da Ya san ba za ta iya dauka baâ€.
Ta kai kofin kunun bakinta. Aalimah ba ta da zabi ban da kurbar kunun. Tamkar koyaushe dandanon abinci ya fi dacin madaci daci a bakinta. Amma saboda wannan taron dangin da suka yi mata, Dr. Rayhanah na yi, Mama na yi, dole ta shanye kofin kunun nan tsaf. Nurse da Doctor na kara lallashi, Mama ma na yi da tattausan lafazi, yayin da Basma ke zaune daidai kafafun Aalimah tana shayar da jaririyarta, Hussainar na goye bayan Mama.
Halin da suke ciki kenan tun bayan rasuwar Aboulkhair da tafiyar Daddy 1 da Daddy 2 da Aboubacar kasar Amurka. Ba su da kowa da suke gani su ji dadi sai junansu. Wata irin kewa ke rarake zukatansu da ciwo mai tsanani. As a husband, ya kasance miji abin kwatance, kasaitacce a zuciyar matarsa wanda babu wanda zai iya tona zuciyarta ya ga halin da ta ke ciki, sai ita kanta. As a brother, shi dan uwa ne like a diamond a wajen kannensa, babu mai iya tona zuciyar Basma don hango zurfi da fadin wannan rashin da ta yi sai ita kanta. Amma sosai ta fi Aalimah juriya, domin ba a fada da ita a kan cin abinci ko don jariranta su samu nasu abincin da Allah ya halitta a jikinta. Sosai ta ke cin abinci, sai in abin ya ciyo ta ne ta ke dangwarawa Mama su ta kulle kanta a toilet ta yi ta kuka.
Yau likita ta ba su sallama, ba don zukata sun warke daga zogin da suke ba a’ah, sai don dukkaninsu suna da lafiya ta gangar jiki. Suka tattara suka koma gida, mama na ci gaba da gasa wa Aalimah da Basma jikinsu da tawul. Sun samu wayar Mummy da Aunty Gumsu inda suka yi musu sallama suka ce za su koma su ma don jinyar su Daddy, saboda Hamoud zai koma bakin aikinsa. Lokacin da suka bai wa Khaleesat wayar don ta yi sallama da su, domin tare da mijinta za ta wuce daga can ba su tsinana komai ba su duka ukun a handsfree sai kuka.
Mama ce ta kwace wayar. Tun daga ranar ba su kara ji daga su Mummy ba, suka ci gaba da jego karkashin kulawar Mama.
Ranar da Basma ta yada wanka aka yi arba’in din Aboulkhair a Yamai, sakon Malam Raazee ya isko su cewa, dukkansu su yi shiri su koma Niamey, zuwa har su Aboubacar su dawo gida. Mama ta soma yi musu shirin tafiya, an yi sa’a su Sabrina suna cikin hutun makaranta.
Basma ce ta saya musu tikiti, daga na Abuja har na Niamey. A washegarin ranar suka daga bakidayansu bayan Mama ta sallami masu aikinta Tabawa da Sabira da cewa inta dawo za ta neme su su dawo bakin aiki. Bilyaminu ya yi musu fatan alkhairi bayan Aalimah ta biya shi kudin aikinsa na gadi, har na wata uku masu zuwa a gaba.
A dakin inna Bintou suka sauka, Mama na dakin Inna Kasisi. Tunda suka zo Basma ba ta san kukan jariranta ba, kullum suna goye a bayan Bintou da Kasisi, idan Malam ya dawo zai ce a kai masa su su taya shi hira. Inna Bintou ba ta barinsu su zauna zugum-zugum din da suke zama, yanzu za ta dauke musu hankali da hira ko da ba za ta samu su tofa albarkacin bakinsu ba sukan yi murmushi. Ta ce Basma ce mai sa wa a yi kuka, don haka ta koma dakin ‘yammata ta bar mata Aalimah mai maida komai ga mahaliccinta.
Abin da ba ta sani ba har gara Basma na yin kuka ta ji dadi a zuciyarta, ita al’amarin da ta ke ji a tata zuciyar yanzu bayan dawowarsu Yamai ya fi karfin ta zubda hawaye. Baza ta gaji da cewa mutuwar Aboulkhair ta shammace ta ba; muguwar shammata. A daidai lokacin da take ganin babu diya macen data kaita sa’ar samun farin cikin dake cikin rayuwar aure. Rokon Allah ta ke yi ya dau ranta ta bi Aboulkhair a ko’ina yake, kuma cikin kowanne hali, a ganinta hakan shi ne kawai kwanciyar hankalinta da samun farin cikinta.
Ba ta son tuno komai na rayuwar da suka shimfida tare. Idan ta kai hannu ta shafa cikinta ta ji shi ma babu, zuciyarta neman fitowa ta ke daga allon kirjinta. Hakika an jarabci rayuwarta da mafi tsananin jarrabawa, tana rokon Allah cikin sujjadar kowacce sallar farillarta, ya kawo sanadin da za ta cinye wannan jarrabawa idan mai cinyuwa ce. Domin ta shafa a ko’ina ba ta ga ranar da za ta haye ta ba. Idan dawowar farin ciki cikin rayuwarta shi ne tsallake wannan siradin, tana da tabbacin har abada ba za ta tsallake shi ba. Ba mutane irin Aboulkhair ke shigowa cikin rayuwar dan Adam su fita da sauki ba. Ba mutane irinsa ke ajiye memories irin wadanda da za’a iya daina tunawa cikin rayuwar auratayya ba.
****
A LAS VEGAS
Watanni hudu kenan da faruwar wannan al’amari ga iyalan Raazee. Cikin wadannan watanni al’amura da yawa sun faru, majinyatan suna ta samun sauki cikin yardar Ubangiji. Dorin Daddy 1 da Daddy 2 na kafafu da hannaye duka ya yi kyau, an kuma kunce. Daddy 1 na tafiya da taimakon croches karafa guda biyu, yayin da Daddy 2 ana jiran raunin kafarsa ya karasa warkewa a makala masa plastic leg, wadda Mu’azzam ya saya masa. Aboubacar ya warware bakidaya sai dan sauran abin da ba’a rasa ba, don haka aka soma yi masa shirin tahowa gida don komawa cikin iyalinsa.
Duk tsawon zaman jinyar nan da Aboubacar ya yi ba su yi waya ba shi da Basma, asibitin ba sa barin majinyatansu rike waya don samun cikakkiyar nutsuwarsu. Haka Hamoud da ya wuce Japan shi da Khaleesat bai hada su sun gaisa ba ko sau daya. Mummy da Gumsu da ke yawan zuwa ganinsu, sai dai su fada masa lafiyar Basma data jikokinsu twins Don haka a yau da likitoci suka tabbatar masa da samun lafiyarsa suka kuma ba shi sallama, cike ya ke da dokin ganin iyalinsa.
Ba yadda Mummy Zulaiha ba ta yi da Aboubacar ba a kan ya kara sati daya ko ya kara murmurewa ya kara samun karfin jikinsa, amma Aboubacar ya ki. Yace Basma ta karasa jinyarsa. A daddafe ya kara kwana uku a gidan Mu’azzam bayan sallamarsa daga asibiti. Mummy ta saya masa tikiti mai zuwa Niamey kai tsaye daga Las Vegas babu transit.
Juyar da kai ta yi cikin son fashewa da kuka. Mama ta sake komawa barin da ta juyar da kan cike da damuwa da kofin mug na tangaran a hannunta mai cike da kunun kanwa.
“Kin san jikinki jikin jego ne Aalimah, ki dinga shan kunun nan ko da ba za ki ci komai ba bayan shi. A ce magana daya kullum sai an yi ta nanata ta kamar cin kwan makauniya?â€
Fuska ta sanya cikin tafukanta biyu ta fara wani irin kuka. Wanda ke tasowa tun daga karkashin zuciyar ta. Sautin sa na mai bayyana halin kunci da ragaita da zuciyarta ke ciki.
“Ni Mama ki rabu da ni, don Allah ki kyaleniâ€. Ta furta cikin wata murya mai ban tausayi.
Daidai lokacin da likitar da ke kula da ita ta bude kofa ta shigo da Nurse biye da ita. Cikin sakin fuska ta isa gaban gadon da Aalimahn ta ke, inda sabo sun saba da wannan kukan na Aalimah tun kwantar da ita a asibitin. Gata bata jin lallashi. Tausayi dattijuwar take bata sabida yadda ta damu da ‘yar tata. Ta karbi kofin daga hannun Mama, ta cire hannun Aalimah daga fuskarta, wanda tuni ya jike sharab da hawaye.
“Mrs. Aboulkhair ba sai na sake maimaitawa ba, jikinki yana bukatar sinadarin abinci mai gina jiki, kada ki manta ‘Da’ aka cire a jikinki ba karamin ciki ba. Ki rage wa Maman ki da ‘yar uwarki damuwa ki dinga cin abinci kin ji?
Allah ba ya dora wa rai abin da Ya san ba za ta iya dauka baâ€.
Ta kai kofin kunun bakinta. Aalimah ba ta da zabi ban da kurbar kunun. Tamkar koyaushe dandanon abinci ya fi dacin madaci daci a bakinta. Amma saboda wannan taron dangin da suka yi mata, Dr. Rayhanah na yi, Mama na yi, dole ta shanye kofin kunun nan tsaf. Nurse da Doctor na kara lallashi, Mama ma na yi da tattausan lafazi, yayin da Basma ke zaune daidai kafafun Aalimah tana shayar da jaririyarta, Hussainar na goye bayan Mama.
Halin da suke ciki kenan tun bayan rasuwar Aboulkhair da tafiyar Daddy 1 da Daddy 2 da Aboubacar kasar Amurka. Ba su da kowa da suke gani su ji dadi sai junansu. Wata irin kewa ke rarake zukatansu da ciwo mai tsanani. As a husband, ya kasance miji abin kwatance, kasaitacce a zuciyar matarsa wanda babu wanda zai iya tona zuciyarta ya ga halin da ta ke ciki, sai ita kanta. As a brother, shi dan uwa ne like a diamond a wajen kannensa, babu mai iya tona zuciyar Basma don hango zurfi da fadin wannan rashin da ta yi sai ita kanta. Amma sosai ta fi Aalimah juriya, domin ba a fada da ita a kan cin abinci ko don jariranta su samu nasu abincin da Allah ya halitta a jikinta. Sosai ta ke cin abinci, sai in abin ya ciyo ta ne ta ke dangwarawa Mama su ta kulle kanta a toilet ta yi ta kuka.
Yau likita ta ba su sallama, ba don zukata sun warke daga zogin da suke ba a’ah, sai don dukkaninsu suna da lafiya ta gangar jiki. Suka tattara suka koma gida, mama na ci gaba da gasa wa Aalimah da Basma jikinsu da tawul. Sun samu wayar Mummy da Aunty Gumsu inda suka yi musu sallama suka ce za su koma su ma don jinyar su Daddy, saboda Hamoud zai koma bakin aikinsa. Lokacin da suka bai wa Khaleesat wayar don ta yi sallama da su, domin tare da mijinta za ta wuce daga can ba su tsinana komai ba su duka ukun a handsfree sai kuka.
Mama ce ta kwace wayar. Tun daga ranar ba su kara ji daga su Mummy ba, suka ci gaba da jego karkashin kulawar Mama.
Ranar da Basma ta yada wanka aka yi arba’in din Aboulkhair a Yamai, sakon Malam Raazee ya isko su cewa, dukkansu su yi shiri su koma Niamey, zuwa har su Aboubacar su dawo gida. Mama ta soma yi musu shirin tafiya, an yi sa’a su Sabrina suna cikin hutun makaranta.
Basma ce ta saya musu tikiti, daga na Abuja har na Niamey. A washegarin ranar suka daga bakidayansu bayan Mama ta sallami masu aikinta Tabawa da Sabira da cewa inta dawo za ta neme su su dawo bakin aiki. Bilyaminu ya yi musu fatan alkhairi bayan Aalimah ta biya shi kudin aikinsa na gadi, har na wata uku masu zuwa a gaba.
A dakin inna Bintou suka sauka, Mama na dakin Inna Kasisi. Tunda suka zo Basma ba ta san kukan jariranta ba, kullum suna goye a bayan Bintou da Kasisi, idan Malam ya dawo zai ce a kai masa su su taya shi hira. Inna Bintou ba ta barinsu su zauna zugum-zugum din da suke zama, yanzu za ta dauke musu hankali da hira ko da ba za ta samu su tofa albarkacin bakinsu ba sukan yi murmushi. Ta ce Basma ce mai sa wa a yi kuka, don haka ta koma dakin ‘yammata ta bar mata Aalimah mai maida komai ga mahaliccinta.
Abin da ba ta sani ba har gara Basma na yin kuka ta ji dadi a zuciyarta, ita al’amarin da ta ke ji a tata zuciyar yanzu bayan dawowarsu Yamai ya fi karfin ta zubda hawaye. Baza ta gaji da cewa mutuwar Aboulkhair ta shammace ta ba; muguwar shammata. A daidai lokacin da take ganin babu diya macen data kaita sa’ar samun farin cikin dake cikin rayuwar aure. Rokon Allah ta ke yi ya dau ranta ta bi Aboulkhair a ko’ina yake, kuma cikin kowanne hali, a ganinta hakan shi ne kawai kwanciyar hankalinta da samun farin cikinta.
Ba ta son tuno komai na rayuwar da suka shimfida tare. Idan ta kai hannu ta shafa cikinta ta ji shi ma babu, zuciyarta neman fitowa ta ke daga allon kirjinta. Hakika an jarabci rayuwarta da mafi tsananin jarrabawa, tana rokon Allah cikin sujjadar kowacce sallar farillarta, ya kawo sanadin da za ta cinye wannan jarrabawa idan mai cinyuwa ce. Domin ta shafa a ko’ina ba ta ga ranar da za ta haye ta ba. Idan dawowar farin ciki cikin rayuwarta shi ne tsallake wannan siradin, tana da tabbacin har abada ba za ta tsallake shi ba. Ba mutane irin Aboulkhair ke shigowa cikin rayuwar dan Adam su fita da sauki ba. Ba mutane irinsa ke ajiye memories irin wadanda da za’a iya daina tunawa cikin rayuwar auratayya ba.
****
A LAS VEGAS
Watanni hudu kenan da faruwar wannan al’amari ga iyalan Raazee. Cikin wadannan watanni al’amura da yawa sun faru, majinyatan suna ta samun sauki cikin yardar Ubangiji. Dorin Daddy 1 da Daddy 2 na kafafu da hannaye duka ya yi kyau, an kuma kunce. Daddy 1 na tafiya da taimakon croches karafa guda biyu, yayin da Daddy 2 ana jiran raunin kafarsa ya karasa warkewa a makala masa plastic leg, wadda Mu’azzam ya saya masa. Aboubacar ya warware bakidaya sai dan sauran abin da ba’a rasa ba, don haka aka soma yi masa shirin tahowa gida don komawa cikin iyalinsa.
Duk tsawon zaman jinyar nan da Aboubacar ya yi ba su yi waya ba shi da Basma, asibitin ba sa barin majinyatansu rike waya don samun cikakkiyar nutsuwarsu. Haka Hamoud da ya wuce Japan shi da Khaleesat bai hada su sun gaisa ba ko sau daya. Mummy da Gumsu da ke yawan zuwa ganinsu, sai dai su fada masa lafiyar Basma data jikokinsu twins Don haka a yau da likitoci suka tabbatar masa da samun lafiyarsa suka kuma ba shi sallama, cike ya ke da dokin ganin iyalinsa.
Ba yadda Mummy Zulaiha ba ta yi da Aboubacar ba a kan ya kara sati daya ko ya kara murmurewa ya kara samun karfin jikinsa, amma Aboubacar ya ki. Yace Basma ta karasa jinyarsa. A daddafe ya kara kwana uku a gidan Mu’azzam bayan sallamarsa daga asibiti. Mummy ta saya masa tikiti mai zuwa Niamey kai tsaye daga Las Vegas babu transit.