Sashe 73
Aalimah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
******
Gumsu ce tsaye a kan Aalimah tana fama da ita a kan ta yi wanka, yayin da ita kuma ta ce ko da a ce za ta fi kowa wari a duniya ta daina wanka.
Gumsu ta yi dariya wadda ke kara qular da Aalimmah, ta ce, “To ni da ki ke yi wa tambotsai mene ne nawa a ciki? Inji dai ba ni na kar zomon ba balle a bani ratayar sa? In ba tsoro ba ki yi a gaban Inna Kasisi mana? Sai a bayan idonsu ki ishe ni da rashin mutunci kala-kala, kada Allah ya sa ki yi wankan, Basma na hanya, ta zo ta ga abin da ki ke yi, wai don ba ki son dan uwantaâ€.
Wata irin harara Aalimah ta zuba wa Gumsu.
“Idan ita Basman uwata ce ta sanya ni karbar sadakin nanâ€.
Gumsu ta ce, “I can relate. Ni wallahi kin fara sa min ciwon kai, wajen Inna zan maida ki. Don in zan shekara ina fada musu rashin kunyar da ki ke min ba yarda za su yi baâ€.
Ta jefa mata bath kit dinta ta bar wajen.
Waya ce ta iso wa Gumsu cewa Basma ta iso, tana dakin Inna Bintou, tana tambayar inda Aalimah ta ke. Basma ba ta san da sabon gidan da mahaifinta ya gina a nan Yamai ba, kamar yadda ba ta san da sakin da ya shiga tsakaninsa da mahaifiyarta ba. Ta dade da sanin Mummy na son zaman U.S kamar me. Ta gaya mata ita ta zabi zaman can, shi da Gumsunsa sun zabi dawowa don haka kowa ya kama hanyarsa.
Ba irin rarrashin da Basma ba ta yi wa Mummy ba kan ta bi sawun mijinta, ta ce sai ranar da Mu’azzam ya warke, bayan tana da masaniyar babu maganin da zai yi maganin lalurar Mu’azzam a dare daya, sai dai a bi alternative a gode wa Allah.
A ganin Basma, Mummy ta yi amfani da lalurar Mu’azzam ne kawai don ta ci gaba da zama a U.S, in ban da haka mutumin da ba gari daya suke ba, me za ta kulla wa rayuwarsa?
Hatta sayar da lodge dinsu na Boston da Daddy yayi Basma ba ta sani ba. Don haka bata san cewa Mummy a gidan Mu’azzam take zaune ba.
Isowar su Niamey kenan ita da tagwayen ‘ya’yanta, Daddy ne ya kira ta musamman don ta taya Gumsu lallashin Aalimah kasancewar ta wadda tafi kowa shaquwa da Aalimah din, su kuma raka ta dakin ta su biyu. Basma jin ta ta ke kamar a gajimare don farin ciki da kulla wannan aure da iyayensu suka yi. Koda Mu’azzam ba ya shiga rayuwarsu Allah ya sani tana matukar son dan uwanta. Kuma ta dade tana fargabar ranar da Aalimah zata yi aure a wani gidan daban ta bar hannun su, don haka ko ta’ina ita wannan hadin ya yi mata daidai.
Akwai wata magana da suka taba yi da Aboulkhair ta sirri gabanin rasuwarsa, wadda ta goge duk wani bacin rai da kullaci da ta ke da shi akan yayan nata Mu’azzam;
Ya gaya mata Mu’az ba shi da lafiya.
Ya gaya mata aggressive patient ne.
Alakar su ta nesa-nesa na da alaka da mental state dinsa.
Bayan haka bai gaya mata kowanne irin disorder yake fama da shi ba.
Basma a dakin Inna Kasisi, bayan sun gaisa ta karbi twins tana fadin,
“Masha Allah da ‘yan lukutaye, kun zo don ku amshe min miji, to kwalelenku duk jar fatarkuâ€.
Dariya Basma ta yi tana fadin, “Kai Inna akwai kishi, ta ga ‘yammata masu lafiyayyar fata duk ta gigiceâ€.
Inna ta ce, “Ke kuwa ai dole. Muna zaune da mijina lafiya, yana nan-nan da ni ya ga wadannan larabawan naki ai sunana ma mantawa zai yiâ€.
Basma ta sake kwashewa da dariya da ma gwanar dariya ce tun yarintar ta. Abin dariya bai da wuya a wajenta. Kullum fararen hakoranta a waje suke. Very jovial kamar Yayanta Aboulkhair Ta ce,
“Inna ina amaryar tamu ne? Na leka dakin Inna Bintou ba ta nanâ€.
Inna Kasisi wadda ke jin haushin Aalimah har iya wuya ta kyabe baki, ta ce,
“Tana gidan Gumsu, kafaffiyar yarinya mai zuciyar banza. Ni da Aalimah ai mun dade da raba jiha. Wanda duk ba ya son Mu’azzam ni ce ba ya so wallahiâ€.
Murmushi Basma ta yi ta ciro nono tana bai wa ‘yarta, ta ce, “Inna ku bi ta a sannu, ba son shi ne ba ta yi ba. Monsieur Aboulkhair ta ke tunawa da kusancin da ke tsakaninsu, it’s not easy to endure (jure hakan abu ne mai wuya)â€.
Inna ta mike don zancen ba ya mata dadi ko ta ina, a ganinta Aalimah kiyayya ta ke yi wa Mu’azzam kawai don ba shi da lafiya.
Ta ce, “In dai lalura ce babu wanda ya wuce ta, uwarta ma yau shekaru goma sha biyar tana fama, haka ubanta ke hakuri da ita da kalar tata lalurar, ita ma ta je ta yi hakuri da lalurar dan uwanta, waraka a hannun Allah take, cewa nake kun ce bada magani ta karanta? Ba sai ta yi ta ba shi maganin ba su zauna lafiya?â€.
Zancen ya so ya bai wa Basma dariya, da ta karanta bada magani ai ba likitar kwakwalwa ba ce. Likitancin ma sai neuro-psychiatry. Rokon Inna ta ke yi ta sa a raka ta gidan Gumsun (gidan mahaifinta), tana cijewa tana fadin,
“Kada ki wani je ki lallashe ta, bar ta da halinta na tsiya. Aure don Mu’azzam bai sa kansa ba ne, da tuni ya auri hudunta a rana dayaâ€.
Basma ta tabbatar Inna Kasisi ba za ta sa a raka ta inda Aalimah ta ke ba, ta dau zafi da ita sosai, sai ta koma wurin Bintou, ita ce ta sa autanta Bello ya raka ta.
Daga bakin kofa Basma ta tsaya, tana kallon diramar da ake tsakanin Aalimah da Antinta Gumsu a kan cin abinci, Gumsun na fadin;
“Ki ci kada mu kai ki da komada, haka kawai ki sossoke min Da, rama ba ta kyau da amarya’.
Ta ce, “Anti Gumsu ina girmamaki, ina ganin girman ki, amma in ki ka kai ni bango zan yaye hijabin girman nan da nake ba ki. Na ce ba zan ci ba, ki yi min dura in ya zama doleâ€.
7/6/21, 4:51 PM - Buhainat: BASMA
Basma ta kama haba, tunda suke tare ba ta san Aalimah da tsiwa da rashin kunya ga na gaba da ita ba. Lallai da gaske ta ke kin Mu’azzam din. Tunda har ya sauyata rana daya. Gumsu ta ce,
“Gara da ki ka gani da idanunki, in wani na bai wa labarin rashin kunyar da Aalimah ta ke min ba zai taba yarda ba, ni kuma kamar dole sai na shiga sha’aninta. Babanku ke ba ni hakuri wallahi da tuni ta tsufa a Las Vegas, don ta soma kawo ni bangoâ€.
Basma ta sako kafa tana shigowa falon ta ce, “I can relate. Amma ni lallashi ne nawa tunda ba zan so Yayana ya same ta duk kasusuwa ba, kada ta soke min shi. Na fi son ya ganta bul-bul, ko’ina ya taba ya ji tubus. Don haka don Allah don Annabi ‘Aal’ ki karbi abinci ki ci…â€.
Kawai sai Aalimah ta sunkuya a kan stool ta fashe da kuka, maganganun Basma kamar sabon Ubangiji ta ji su a kwanyarta. Shigowar Daddy kenan har zai wuce dakinsa ya jiyo kukanta, har zai kyale ya rabu da su don ya san maganar daya ce dai, sai kuma ya dawo sabida tausayin da Aalimah ke ba shi. Dakin ya shigo yana fadin, “Gumsu! Gumsu! Sabida Allah ba za ki lallashe ta ba sai dai ki dinga tunzura ta ko?â€
Sai kuma ya ga Basma, ya ce, “Ke kuma saukar yaushe? Me ku ka yi mata haka?â€
Cikin kuka ta ce,
“Daddy, Basma ta zage niâ€.
Basma ta hau gaishe shi da kokarin kare kanta, ya ki amsawa, ya hau ta da fada.
“Ku da za ku lallaba ta sai ku dinga kunnata, bayan kun san a kan tsini ta ke?â€
“Ka yi hakuri Daddy, ba za mu sake baâ€. Basma ta fada cikin ladabi.
Ya wuce cikin fushi. Basma da Gumsu suka kama abin da ke gabansu don yanzu tsoron sharrin Aalimah suke ji. Ka ce ‘allura’ ta ce ka ce ‘garma’, don ta ga Daddy yana biye mata.
Kwana biyu bayan nan Daddy ya umarci Gumsu da ta kai ta cikin gida ta yi sallama da kowa, wurin Malam ya zama daki na karshe da za su je. Tun Aalimah na kallon al’amarin a matsayin almara har ta yarda gaskiya ne. A lokacin da Malam Ibrahim Raazee ya dora mata sadakinta a tafin hannunta ya kuma bude kofofin nasiha, ban hakuri, ban baki da neman afuwa daga gare ta, kan cewa sun yi exercising power dinsu ta iyaye a kanta kan ba yadda za su yi ne su ma, su samu nutsuwa da kwanciyar hankali in ba hakan ba.
Wannan ne gata na karshe da suke jin za su yi wa rayuwarsu ita da Mu’azzam. Babu mijin da suke ganin zai rike ta da daraja da kima bayan Aboulkhair sai shi Mu’azzam, su ma kuma babu matar da za ta rike musu Mu’azzam da lalurorinsa tsakani da Allah sai ita. Wannan ne hujjarsu ta hada su aure, ta fi kowa sanin yanayin rayuwarsa bayan Aboulkhair tunda sun zauna tare, ta kuma zauna da Aboulkhair ta ga yadda yake kula da shi. Don haka suke da kyakkyawan fata a kanta. Ta yi hakuri kada ta bada musu kasa a ido. Ta manta da kusancin dake tsakanin shi da Aboulkhair ta gina sabuwar rayuwa mai inganci. Aboulkhair ya riga ya yi tafiyar da bazai taba dawowa ba, kuma shima hakan ne gata na karshe da zata yi masa wato tallafar rayuwar Mu’azzam a sanda babu shi.
Gumsu ce tsaye a kan Aalimah tana fama da ita a kan ta yi wanka, yayin da ita kuma ta ce ko da a ce za ta fi kowa wari a duniya ta daina wanka.
Gumsu ta yi dariya wadda ke kara qular da Aalimmah, ta ce, “To ni da ki ke yi wa tambotsai mene ne nawa a ciki? Inji dai ba ni na kar zomon ba balle a bani ratayar sa? In ba tsoro ba ki yi a gaban Inna Kasisi mana? Sai a bayan idonsu ki ishe ni da rashin mutunci kala-kala, kada Allah ya sa ki yi wankan, Basma na hanya, ta zo ta ga abin da ki ke yi, wai don ba ki son dan uwantaâ€.
Wata irin harara Aalimah ta zuba wa Gumsu.
“Idan ita Basman uwata ce ta sanya ni karbar sadakin nanâ€.
Gumsu ta ce, “I can relate. Ni wallahi kin fara sa min ciwon kai, wajen Inna zan maida ki. Don in zan shekara ina fada musu rashin kunyar da ki ke min ba yarda za su yi baâ€.
Ta jefa mata bath kit dinta ta bar wajen.
Waya ce ta iso wa Gumsu cewa Basma ta iso, tana dakin Inna Bintou, tana tambayar inda Aalimah ta ke. Basma ba ta san da sabon gidan da mahaifinta ya gina a nan Yamai ba, kamar yadda ba ta san da sakin da ya shiga tsakaninsa da mahaifiyarta ba. Ta dade da sanin Mummy na son zaman U.S kamar me. Ta gaya mata ita ta zabi zaman can, shi da Gumsunsa sun zabi dawowa don haka kowa ya kama hanyarsa.
Ba irin rarrashin da Basma ba ta yi wa Mummy ba kan ta bi sawun mijinta, ta ce sai ranar da Mu’azzam ya warke, bayan tana da masaniyar babu maganin da zai yi maganin lalurar Mu’azzam a dare daya, sai dai a bi alternative a gode wa Allah.
A ganin Basma, Mummy ta yi amfani da lalurar Mu’azzam ne kawai don ta ci gaba da zama a U.S, in ban da haka mutumin da ba gari daya suke ba, me za ta kulla wa rayuwarsa?
Hatta sayar da lodge dinsu na Boston da Daddy yayi Basma ba ta sani ba. Don haka bata san cewa Mummy a gidan Mu’azzam take zaune ba.
Isowar su Niamey kenan ita da tagwayen ‘ya’yanta, Daddy ne ya kira ta musamman don ta taya Gumsu lallashin Aalimah kasancewar ta wadda tafi kowa shaquwa da Aalimah din, su kuma raka ta dakin ta su biyu. Basma jin ta ta ke kamar a gajimare don farin ciki da kulla wannan aure da iyayensu suka yi. Koda Mu’azzam ba ya shiga rayuwarsu Allah ya sani tana matukar son dan uwanta. Kuma ta dade tana fargabar ranar da Aalimah zata yi aure a wani gidan daban ta bar hannun su, don haka ko ta’ina ita wannan hadin ya yi mata daidai.
Akwai wata magana da suka taba yi da Aboulkhair ta sirri gabanin rasuwarsa, wadda ta goge duk wani bacin rai da kullaci da ta ke da shi akan yayan nata Mu’azzam;
Ya gaya mata Mu’az ba shi da lafiya.
Ya gaya mata aggressive patient ne.
Alakar su ta nesa-nesa na da alaka da mental state dinsa.
Bayan haka bai gaya mata kowanne irin disorder yake fama da shi ba.
Basma a dakin Inna Kasisi, bayan sun gaisa ta karbi twins tana fadin,
“Masha Allah da ‘yan lukutaye, kun zo don ku amshe min miji, to kwalelenku duk jar fatarkuâ€.
Dariya Basma ta yi tana fadin, “Kai Inna akwai kishi, ta ga ‘yammata masu lafiyayyar fata duk ta gigiceâ€.
Inna ta ce, “Ke kuwa ai dole. Muna zaune da mijina lafiya, yana nan-nan da ni ya ga wadannan larabawan naki ai sunana ma mantawa zai yiâ€.
Basma ta sake kwashewa da dariya da ma gwanar dariya ce tun yarintar ta. Abin dariya bai da wuya a wajenta. Kullum fararen hakoranta a waje suke. Very jovial kamar Yayanta Aboulkhair Ta ce,
“Inna ina amaryar tamu ne? Na leka dakin Inna Bintou ba ta nanâ€.
Inna Kasisi wadda ke jin haushin Aalimah har iya wuya ta kyabe baki, ta ce,
“Tana gidan Gumsu, kafaffiyar yarinya mai zuciyar banza. Ni da Aalimah ai mun dade da raba jiha. Wanda duk ba ya son Mu’azzam ni ce ba ya so wallahiâ€.
Murmushi Basma ta yi ta ciro nono tana bai wa ‘yarta, ta ce, “Inna ku bi ta a sannu, ba son shi ne ba ta yi ba. Monsieur Aboulkhair ta ke tunawa da kusancin da ke tsakaninsu, it’s not easy to endure (jure hakan abu ne mai wuya)â€.
Inna ta mike don zancen ba ya mata dadi ko ta ina, a ganinta Aalimah kiyayya ta ke yi wa Mu’azzam kawai don ba shi da lafiya.
Ta ce, “In dai lalura ce babu wanda ya wuce ta, uwarta ma yau shekaru goma sha biyar tana fama, haka ubanta ke hakuri da ita da kalar tata lalurar, ita ma ta je ta yi hakuri da lalurar dan uwanta, waraka a hannun Allah take, cewa nake kun ce bada magani ta karanta? Ba sai ta yi ta ba shi maganin ba su zauna lafiya?â€.
Zancen ya so ya bai wa Basma dariya, da ta karanta bada magani ai ba likitar kwakwalwa ba ce. Likitancin ma sai neuro-psychiatry. Rokon Inna ta ke yi ta sa a raka ta gidan Gumsun (gidan mahaifinta), tana cijewa tana fadin,
“Kada ki wani je ki lallashe ta, bar ta da halinta na tsiya. Aure don Mu’azzam bai sa kansa ba ne, da tuni ya auri hudunta a rana dayaâ€.
Basma ta tabbatar Inna Kasisi ba za ta sa a raka ta inda Aalimah ta ke ba, ta dau zafi da ita sosai, sai ta koma wurin Bintou, ita ce ta sa autanta Bello ya raka ta.
Daga bakin kofa Basma ta tsaya, tana kallon diramar da ake tsakanin Aalimah da Antinta Gumsu a kan cin abinci, Gumsun na fadin;
“Ki ci kada mu kai ki da komada, haka kawai ki sossoke min Da, rama ba ta kyau da amarya’.
Ta ce, “Anti Gumsu ina girmamaki, ina ganin girman ki, amma in ki ka kai ni bango zan yaye hijabin girman nan da nake ba ki. Na ce ba zan ci ba, ki yi min dura in ya zama doleâ€.
7/6/21, 4:51 PM - Buhainat: BASMA
Basma ta kama haba, tunda suke tare ba ta san Aalimah da tsiwa da rashin kunya ga na gaba da ita ba. Lallai da gaske ta ke kin Mu’azzam din. Tunda har ya sauyata rana daya. Gumsu ta ce,
“Gara da ki ka gani da idanunki, in wani na bai wa labarin rashin kunyar da Aalimah ta ke min ba zai taba yarda ba, ni kuma kamar dole sai na shiga sha’aninta. Babanku ke ba ni hakuri wallahi da tuni ta tsufa a Las Vegas, don ta soma kawo ni bangoâ€.
Basma ta sako kafa tana shigowa falon ta ce, “I can relate. Amma ni lallashi ne nawa tunda ba zan so Yayana ya same ta duk kasusuwa ba, kada ta soke min shi. Na fi son ya ganta bul-bul, ko’ina ya taba ya ji tubus. Don haka don Allah don Annabi ‘Aal’ ki karbi abinci ki ci…â€.
Kawai sai Aalimah ta sunkuya a kan stool ta fashe da kuka, maganganun Basma kamar sabon Ubangiji ta ji su a kwanyarta. Shigowar Daddy kenan har zai wuce dakinsa ya jiyo kukanta, har zai kyale ya rabu da su don ya san maganar daya ce dai, sai kuma ya dawo sabida tausayin da Aalimah ke ba shi. Dakin ya shigo yana fadin, “Gumsu! Gumsu! Sabida Allah ba za ki lallashe ta ba sai dai ki dinga tunzura ta ko?â€
Sai kuma ya ga Basma, ya ce, “Ke kuma saukar yaushe? Me ku ka yi mata haka?â€
Cikin kuka ta ce,
“Daddy, Basma ta zage niâ€.
Basma ta hau gaishe shi da kokarin kare kanta, ya ki amsawa, ya hau ta da fada.
“Ku da za ku lallaba ta sai ku dinga kunnata, bayan kun san a kan tsini ta ke?â€
“Ka yi hakuri Daddy, ba za mu sake baâ€. Basma ta fada cikin ladabi.
Ya wuce cikin fushi. Basma da Gumsu suka kama abin da ke gabansu don yanzu tsoron sharrin Aalimah suke ji. Ka ce ‘allura’ ta ce ka ce ‘garma’, don ta ga Daddy yana biye mata.
Kwana biyu bayan nan Daddy ya umarci Gumsu da ta kai ta cikin gida ta yi sallama da kowa, wurin Malam ya zama daki na karshe da za su je. Tun Aalimah na kallon al’amarin a matsayin almara har ta yarda gaskiya ne. A lokacin da Malam Ibrahim Raazee ya dora mata sadakinta a tafin hannunta ya kuma bude kofofin nasiha, ban hakuri, ban baki da neman afuwa daga gare ta, kan cewa sun yi exercising power dinsu ta iyaye a kanta kan ba yadda za su yi ne su ma, su samu nutsuwa da kwanciyar hankali in ba hakan ba.
Wannan ne gata na karshe da suke jin za su yi wa rayuwarsu ita da Mu’azzam. Babu mijin da suke ganin zai rike ta da daraja da kima bayan Aboulkhair sai shi Mu’azzam, su ma kuma babu matar da za ta rike musu Mu’azzam da lalurorinsa tsakani da Allah sai ita. Wannan ne hujjarsu ta hada su aure, ta fi kowa sanin yanayin rayuwarsa bayan Aboulkhair tunda sun zauna tare, ta kuma zauna da Aboulkhair ta ga yadda yake kula da shi. Don haka suke da kyakkyawan fata a kanta. Ta yi hakuri kada ta bada musu kasa a ido. Ta manta da kusancin dake tsakanin shi da Aboulkhair ta gina sabuwar rayuwa mai inganci. Aboulkhair ya riga ya yi tafiyar da bazai taba dawowa ba, kuma shima hakan ne gata na karshe da zata yi masa wato tallafar rayuwar Mu’azzam a sanda babu shi.