Sashe 65
Aalimah Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Mummy Zulaiha a wannan dan lokacin ta yarda kishiya ‘yar uwa ce (idan ka yi katari da mai kyakykyawar zuciya kuma ta kirki). Gumsu ta zama kamar kanwarta ta jini, tare suke gudanar da dukkan al’amuransu na yau da kullum a gidan Mu’azzam, kama daga girki yau wannan ta yi, gobe wannan ta karba, jinyar mijinsu da dan uwansa da taimakekeniya a tsakaninsu. Gumsu-Moiram, ba ta da matsala ko kadan, ke dai barta da wauta, ban dariya da barkwancinta wadanda ke sayo mata soyayyar jama’a, inda duk ta zauna sai an san da ita a wurin saboda ban dariyarta. Mummy ta samu kanta da jin kunyar kanta in ta tuno haukan data rika yiwa mijinta da ‘ya’yanta akan auren Gumsu. Ita kam in haka kishiya take, to tana alfahari da tata, da zuciya daya take son ‘ya’yan ta. Sai ka rantse da Allah kwanciyar mijinsu jinya ba ta dame ta ba, harkan gabanta kawai ta ke, shi ma kansa Daddyn gaya masa ta ke a gaban kowa.
“Gara ma ka mike daga jinyar nan haka Daddy, Allah ya gani na yi hakuri. Gumsu ba ta da wani mijin bayan kai, ya ya ka ke so ta yi da ranta?â€
Ko a gaban likitoci Gumsu kan fadi wannan magana idan ta bushi iska, sai dai Daddyn da Mummy su ji mata kunyar ita babu ruwanta.
Bayan tahowar Aboubacar, ya zama daga Daddy 1 sai Daddy 2 a gadon asibiti. Ba dakinsu daya ba, kowa da dakinsa daban, amma suna yawan haduwa, in an fito da su shan iska a garden din asibitin ko an fito da su motsa jiki a gym. A nan ne su kan yi hirarrakinsu da suka shafe su ko ‘ya’yansu, da kuma iyayensu da ke gida Niger.
A yau ma kamar kullum, an fito da su ‘garden’ domin shan iska. Daddy 1 ( Ishaq) ya dubi kaninsa Daddy 2 (Mansur) ya ce,
“Ina lissafe da watanni, Aalimah ta dade da gama takaba, me ka shiryawa rayuwar ta a bangarenka?â€
Daddy 2 yayi saurin girgiza kai, a sanyaye ya ce,
“Me kuwa na shirya mata ban da abin da Ubangijinta ya shirya mata?
Muna namu Allah na nashi, kuma nashin shi ne gaskiya, dukkanmu lalube muke yi a cikin duhu.
A da ne nake wannan wautar (future planning) ga ‘ya’yana, amma yanzu kullum cikin istigfari nake a bisa hakan. Duk abinda Allah ya shiryawa rayuwarsu dai-dai neâ€.
Daddy 2 ya yi murmushi, shi shaida ne a kan cewa Mansour ya fi shi shiga tashin hankali da rashin Aboulkhair, ya dade yana sambatu har a cikin baccinsa. Ko lokacin da ake masa gyaran karaya akwai Aboulkhairi cikin sambatunsa irin na radadin ciwo. Wani tunani ne mai nauyi ke yawo a zuciyarsa daga jiya zuwa yau, wanda ya ke tsoron furtawa gare shi, ko ko ya ce, ba shi da ikon furta shi ga kowa ko ta ina aka je aka dawo. Don haka ya ja bakinsa ya yi shiru, yana sauraron bugun da zuciyarsa ke yi, wanda ke tafe da sake da jaddada masa muhimmancin maganar da ba ya son yi din da kowa banda zuciyarsa a kowanne bugu guda daya na zuciyarsa, tunanin ya hana shi sakat, shi kuma yana bi yana danne shi da fin karfin zuciya da karfafa imani.
A yau ne aka sallame su bakidaya daga asibitin Southern Hills, direban Mu’azzam ne ya kwaso su dukkansu zuwa gidan Mu’azzam, Mummy ta ce ya lissafa mata albashinsu daga ranar da Mu’azzam ya shiga asibiti zuwa yau ta biya su. Budan bakin Harrison sai cewa ya yi, albashin shekara Mu’azzam yake kullawa a lokaci guda ya basu, kuma ko ba don haka ba shi mai hidimtawa iyayensa ne ko babu ko sisi sabida kyautayinsa, jin kansa da kyautatawarsa gare shi. Harrison ya kare zancensa da cewa;
“I wish him a quick recoveryâ€.
Ya fita ya bar falon. Fuskarsa dauke da alhinin rashin sanin halin da Ubangidan nasa ke ciki. Wanda yake jin kamar ya dauka ya mayar a kansa.
Falon ya saura Daddy 1, Daddy 2 da matansa guda biyu, Yesmin da Nurat sun fita da Harrison zai kai su saloon, Daddy 2 ya ce,
“To alhamdulillahi, ni ma lokacin komawata gida ya yi, wannan gari naku sai ku, sanyin cikinsa mai takurawa da matsantawa ne. Yaya Ishaq, Zulaiha, Gumsu-Moiram na gode da dawainiyar ku, Allah ya rubuta a mizanin Hassanaat na zumunci, ya sa ya zame mana silar shiga aljanna baki daya, Ya jikan Aboulkhair, halinsa na gari ya bi shi. I have missed a darling son but I’m sure Ubangiji Rahmanur-rahimu ya fi ni son shi….â€.
Bai rufe baki ba ya lura sun soma yin sana’ar tasu (sharbe) Zulaiha da Gumsu, babu yadda za’a yi a ambato Aboulkhair a waje ko a yi masa addu’a suna wajen ba su zubda hawaye ba. Don haka ya yi maza ya sauya zancen sa da tambayar Daddy 1 yaushe Mu’azzam zai fito daga asibiti?
Zai so ya ganshi kafin ya koma. Akwai zantuka masu muhimmanci da yake son yi da shi. A take Daddy 1 ya karbi wayar Mummy. Dr. Nebrass ya kira, suka yi magana ya maida wayarsa aljihu.
Ya dubi kanin nasa ya ce, sai sabon wata za su kyale Mu’azzam ya shiga harkokinsa, they are very cautious a kan aikinsu ba kamar kasashenmu na Africa ba, sai sun tabbatar ba shi da damuwar da za ta dami kwakwalwarsa, kuma zai iya aikinsa normally, sannan zai iya daukan al’amuran rayuwa a zahirin yadda suke ba tare da sun shafi matsalarsa ba, amma shi zai iya ganinsa idan Mu’azzam din ya amince.
Ko da Nebrass ya gaya wa Mu’azzam Kawunsa na son yin sallama da shi zai koma Nigeria, bai ki ba. Hasalima sosai yake son ganinsa shima, ko yana kin jama’a ban da kawu Mansour da Aboulkhair shi kansa bai san dalili ba. Watakila don sun fi kowa iya tafiyar da shi ne da odd behaviours dinsa (baudaddun halayensa). Tare suka shiga dakin Mu’azzam da yammacin ranar, inda suka same shi yana sallah, Dr. Nebrass ya fita, Daddy 1 ya zauna zaman jiransa ya idar yana jan tazbahar hannunsa.
Bayan ya yi sallama ya dade yana addu’a, ko ba’a tambaya ba Daddy 1 ya san me Mu’azzam yake roka. A yanzu ya sani ba shi da wata bukata mafi muhimmanci wadda ta wuce ta samun rahmar Aboulkhair a wajen Allah. A sanda yake raye, ba su da bukata mai muhimmanci sai junansu. Aalimah ta taba gaya masa sabida Mu’azzam Aboulkhair ya dage ya tsaya tsayin daka ya karanci neuropsychiatry.
Al’amarin da ya dade yana burge shi hadi da kayatar da shi a zuci. Ya dade bai ga ‘yan uwan da ke son juna fisabilillah irin Mu’azzam da Aboulkhairi ba ko a labaran hikaya. Ta kuma gaya masa irin takaddamar da suka sha da Mu’azzam kan su zauna gida daya amma ya ki amincewa. Ba ya karantar zuciya, amma ya san Mu’azzam na nan yana regretting. In ya ce regretting yana nufin nadama mai sa zuciya ciwo da hanata jin dadin rayuwa ko ta yaya. Allah kenan.
7/4/21, 9:48 PM - Buhainat: HABUBAKAR ADO
#######################################################
Cikin satin suka biyo jirgi da komai nasu suka baro kasar Amurka. Bari na din-din-din. Ishak Raazee na mai jin wata irin kewa wadda sabo ke haddasawa na mamayar zuciyarsa. Mummy na mai jin kamar ita daya ta rage a fadin duniya sabida kewar mijinta da ‘ya’yanta. Saidai ko kadan bata yi nadamar hukuncin da ta zartas ba. Yesmin na kuka kamar ranta zai fita a kan rabuwar iyayenta, suka taho shi da Moiram da diyarta Nurat, ya baro mata Yesmin ne don rage mata bacin rai.
Haka Mummy ta yi kokarin shanye damuwarta wannan karon ba tare da ta raba ta tare da Mu’azzam ba, ganin cewa bai jima da barin gadon asibiti ba. Kuma in ba za ta manta ba Aboulkhair ya hane ta dora wa Mu’azzam damuwa, ko dai ta shanye kayar ta ita kadai, ko ta raba ta tare da shi (Aboulkhair) din, amma sharing dinta da Mu’azzam babbar illa ce ga kyakkyawan treatment din da yake samu.
Ko da ta koma office a washegari da niyyar bada hakuri a maida ita bakin aikinta wani ta tarar a mazauninta (JP MORGAN CHASE) ba su daukar wasa da aiki, ko da kuwa da excuse. Balle ita nata babu excuse din ma. Rana daya aka nemeta a kasar aka rasa. Tsabar rudanin rayuwar data samu kanta ya mantar da ita cewa ita din ma’aikaciya ce, ma’aikaciyar ma ta babban bankin Amurka irin JP Morgan. Haka ta dawo kafafu a sage, ta soma neman wani aikin ta yanar gizo, amma har watanni uku suka shafe bata dace ba. Sakamakon matsin lambar da musulmin kasar ke fuskanta a lokacin daga sabuwar gwamnatin Amurka karkashin mulkin sabon shugaban kasa Donald Trump. Da yawa sai komawa suke kasashen su na asali. Ba don Yesmin da ke zuwa makaranta ba Las Vegas za ta tattara ta koma bakidaya, in Mu’azzam ba zai rike ta ba ita da autarta, ya san yadda zai yi da su. Shine kadai dolenta a yanzu.
******
“Gara ma ka mike daga jinyar nan haka Daddy, Allah ya gani na yi hakuri. Gumsu ba ta da wani mijin bayan kai, ya ya ka ke so ta yi da ranta?â€
Ko a gaban likitoci Gumsu kan fadi wannan magana idan ta bushi iska, sai dai Daddyn da Mummy su ji mata kunyar ita babu ruwanta.
Bayan tahowar Aboubacar, ya zama daga Daddy 1 sai Daddy 2 a gadon asibiti. Ba dakinsu daya ba, kowa da dakinsa daban, amma suna yawan haduwa, in an fito da su shan iska a garden din asibitin ko an fito da su motsa jiki a gym. A nan ne su kan yi hirarrakinsu da suka shafe su ko ‘ya’yansu, da kuma iyayensu da ke gida Niger.
A yau ma kamar kullum, an fito da su ‘garden’ domin shan iska. Daddy 1 ( Ishaq) ya dubi kaninsa Daddy 2 (Mansur) ya ce,
“Ina lissafe da watanni, Aalimah ta dade da gama takaba, me ka shiryawa rayuwar ta a bangarenka?â€
Daddy 2 yayi saurin girgiza kai, a sanyaye ya ce,
“Me kuwa na shirya mata ban da abin da Ubangijinta ya shirya mata?
Muna namu Allah na nashi, kuma nashin shi ne gaskiya, dukkanmu lalube muke yi a cikin duhu.
A da ne nake wannan wautar (future planning) ga ‘ya’yana, amma yanzu kullum cikin istigfari nake a bisa hakan. Duk abinda Allah ya shiryawa rayuwarsu dai-dai neâ€.
Daddy 2 ya yi murmushi, shi shaida ne a kan cewa Mansour ya fi shi shiga tashin hankali da rashin Aboulkhair, ya dade yana sambatu har a cikin baccinsa. Ko lokacin da ake masa gyaran karaya akwai Aboulkhairi cikin sambatunsa irin na radadin ciwo. Wani tunani ne mai nauyi ke yawo a zuciyarsa daga jiya zuwa yau, wanda ya ke tsoron furtawa gare shi, ko ko ya ce, ba shi da ikon furta shi ga kowa ko ta ina aka je aka dawo. Don haka ya ja bakinsa ya yi shiru, yana sauraron bugun da zuciyarsa ke yi, wanda ke tafe da sake da jaddada masa muhimmancin maganar da ba ya son yi din da kowa banda zuciyarsa a kowanne bugu guda daya na zuciyarsa, tunanin ya hana shi sakat, shi kuma yana bi yana danne shi da fin karfin zuciya da karfafa imani.
A yau ne aka sallame su bakidaya daga asibitin Southern Hills, direban Mu’azzam ne ya kwaso su dukkansu zuwa gidan Mu’azzam, Mummy ta ce ya lissafa mata albashinsu daga ranar da Mu’azzam ya shiga asibiti zuwa yau ta biya su. Budan bakin Harrison sai cewa ya yi, albashin shekara Mu’azzam yake kullawa a lokaci guda ya basu, kuma ko ba don haka ba shi mai hidimtawa iyayensa ne ko babu ko sisi sabida kyautayinsa, jin kansa da kyautatawarsa gare shi. Harrison ya kare zancensa da cewa;
“I wish him a quick recoveryâ€.
Ya fita ya bar falon. Fuskarsa dauke da alhinin rashin sanin halin da Ubangidan nasa ke ciki. Wanda yake jin kamar ya dauka ya mayar a kansa.
Falon ya saura Daddy 1, Daddy 2 da matansa guda biyu, Yesmin da Nurat sun fita da Harrison zai kai su saloon, Daddy 2 ya ce,
“To alhamdulillahi, ni ma lokacin komawata gida ya yi, wannan gari naku sai ku, sanyin cikinsa mai takurawa da matsantawa ne. Yaya Ishaq, Zulaiha, Gumsu-Moiram na gode da dawainiyar ku, Allah ya rubuta a mizanin Hassanaat na zumunci, ya sa ya zame mana silar shiga aljanna baki daya, Ya jikan Aboulkhair, halinsa na gari ya bi shi. I have missed a darling son but I’m sure Ubangiji Rahmanur-rahimu ya fi ni son shi….â€.
Bai rufe baki ba ya lura sun soma yin sana’ar tasu (sharbe) Zulaiha da Gumsu, babu yadda za’a yi a ambato Aboulkhair a waje ko a yi masa addu’a suna wajen ba su zubda hawaye ba. Don haka ya yi maza ya sauya zancen sa da tambayar Daddy 1 yaushe Mu’azzam zai fito daga asibiti?
Zai so ya ganshi kafin ya koma. Akwai zantuka masu muhimmanci da yake son yi da shi. A take Daddy 1 ya karbi wayar Mummy. Dr. Nebrass ya kira, suka yi magana ya maida wayarsa aljihu.
Ya dubi kanin nasa ya ce, sai sabon wata za su kyale Mu’azzam ya shiga harkokinsa, they are very cautious a kan aikinsu ba kamar kasashenmu na Africa ba, sai sun tabbatar ba shi da damuwar da za ta dami kwakwalwarsa, kuma zai iya aikinsa normally, sannan zai iya daukan al’amuran rayuwa a zahirin yadda suke ba tare da sun shafi matsalarsa ba, amma shi zai iya ganinsa idan Mu’azzam din ya amince.
Ko da Nebrass ya gaya wa Mu’azzam Kawunsa na son yin sallama da shi zai koma Nigeria, bai ki ba. Hasalima sosai yake son ganinsa shima, ko yana kin jama’a ban da kawu Mansour da Aboulkhair shi kansa bai san dalili ba. Watakila don sun fi kowa iya tafiyar da shi ne da odd behaviours dinsa (baudaddun halayensa). Tare suka shiga dakin Mu’azzam da yammacin ranar, inda suka same shi yana sallah, Dr. Nebrass ya fita, Daddy 1 ya zauna zaman jiransa ya idar yana jan tazbahar hannunsa.
Bayan ya yi sallama ya dade yana addu’a, ko ba’a tambaya ba Daddy 1 ya san me Mu’azzam yake roka. A yanzu ya sani ba shi da wata bukata mafi muhimmanci wadda ta wuce ta samun rahmar Aboulkhair a wajen Allah. A sanda yake raye, ba su da bukata mai muhimmanci sai junansu. Aalimah ta taba gaya masa sabida Mu’azzam Aboulkhair ya dage ya tsaya tsayin daka ya karanci neuropsychiatry.
Al’amarin da ya dade yana burge shi hadi da kayatar da shi a zuci. Ya dade bai ga ‘yan uwan da ke son juna fisabilillah irin Mu’azzam da Aboulkhairi ba ko a labaran hikaya. Ta kuma gaya masa irin takaddamar da suka sha da Mu’azzam kan su zauna gida daya amma ya ki amincewa. Ba ya karantar zuciya, amma ya san Mu’azzam na nan yana regretting. In ya ce regretting yana nufin nadama mai sa zuciya ciwo da hanata jin dadin rayuwa ko ta yaya. Allah kenan.
7/4/21, 9:48 PM - Buhainat: HABUBAKAR ADO
#######################################################
Cikin satin suka biyo jirgi da komai nasu suka baro kasar Amurka. Bari na din-din-din. Ishak Raazee na mai jin wata irin kewa wadda sabo ke haddasawa na mamayar zuciyarsa. Mummy na mai jin kamar ita daya ta rage a fadin duniya sabida kewar mijinta da ‘ya’yanta. Saidai ko kadan bata yi nadamar hukuncin da ta zartas ba. Yesmin na kuka kamar ranta zai fita a kan rabuwar iyayenta, suka taho shi da Moiram da diyarta Nurat, ya baro mata Yesmin ne don rage mata bacin rai.
Haka Mummy ta yi kokarin shanye damuwarta wannan karon ba tare da ta raba ta tare da Mu’azzam ba, ganin cewa bai jima da barin gadon asibiti ba. Kuma in ba za ta manta ba Aboulkhair ya hane ta dora wa Mu’azzam damuwa, ko dai ta shanye kayar ta ita kadai, ko ta raba ta tare da shi (Aboulkhair) din, amma sharing dinta da Mu’azzam babbar illa ce ga kyakkyawan treatment din da yake samu.
Ko da ta koma office a washegari da niyyar bada hakuri a maida ita bakin aikinta wani ta tarar a mazauninta (JP MORGAN CHASE) ba su daukar wasa da aiki, ko da kuwa da excuse. Balle ita nata babu excuse din ma. Rana daya aka nemeta a kasar aka rasa. Tsabar rudanin rayuwar data samu kanta ya mantar da ita cewa ita din ma’aikaciya ce, ma’aikaciyar ma ta babban bankin Amurka irin JP Morgan. Haka ta dawo kafafu a sage, ta soma neman wani aikin ta yanar gizo, amma har watanni uku suka shafe bata dace ba. Sakamakon matsin lambar da musulmin kasar ke fuskanta a lokacin daga sabuwar gwamnatin Amurka karkashin mulkin sabon shugaban kasa Donald Trump. Da yawa sai komawa suke kasashen su na asali. Ba don Yesmin da ke zuwa makaranta ba Las Vegas za ta tattara ta koma bakidaya, in Mu’azzam ba zai rike ta ba ita da autarta, ya san yadda zai yi da su. Shine kadai dolenta a yanzu.
******