Sashe 28
Aalimah Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
******
Jirgin Ethiopian Air ya sauke iyalin Ishaq Raazee a filin jiragen saman Diori Hamani International Airport da misalin karfe goma na safiyar lahadi agogonsu na can. Sun samu Hamoud babban dan Uncle Oussama yana jiran saukarsu, shi da Balkisa ‘yar Uncle Edrissa babbar kawa ga Aalimah kenan kaf dangi. Iyalin Ishaq sun zamo kamar wasu taurari sha kallo a cikin gidan Malam Ibrahim Raazee a yau saboda murjewa da kyan fatarsu, duk da cewa kowa a gidan fari ne kal! Amma nasu ya sha bamban da na kowa. Kan ka ce meye wannan? Gida da makwabta ya kacame da murnar zuwansu, aka shiga aiko da akussan abinci daga kowanne bangare. Inna Kasisi kam ko a launin fuska babu wani alamu da zai nuna maka ta yi farin ciki da zuwan nasu, sabgogin gabanta kawai ta ke na dora sanwar abincin rana na gidan bakidaya, kasancewar abincin gandu ake yi a gidan.
Inna Bintou ce ke ta hidima da su tun shigowarsu da ‘yammatan gidan (jikoki) sa’anninsu. Daddy Ishaq kasa yi wa Inna Bintou alkunya ya yi irin wadda ya saba, wato fara shiga sassanta, dakin mahaifiyarsa ya shiga kansa a duke yana jin wani irin nauyi a zuciyarsa. Ta kara tsufa mai nuna alamun girma a tare da ita tsayin shekaru shidda da ya kwashe bai sako kafarsa a gidan iyayensa ba. Zama ya yi a kan kilishi ya tankwashe kafafunsa, zuciyarsa ta yi nauyi mai cakude da matsananciyar nadama. Sam ta ki yarda ta zauna a dakin, sai dai ta shigo ta dauki abu ta fita ba tare da ta dubi bigiren da yake ba.
Ko da ta gama girkinta ba ta zubo masa ba, amma ta zuba wa su Aalimah. Shinkafa fara tas! Da miyar dage-dage wadda ta ji fala-falan ganyen kabeji da naman rakumi zuku-zuku. Abincin ya yi masa kyau a ido, ya kuma ba shi sha’awa. Ya shiga tunano yadda suke santin abincin Innar shi da yayyensa Oussama, Edrissa da kaninsa Mansour da sauran kannensu ‘ya’yan Inna Bintou. Da yake a faranti guda ake zuba musu, in an cinye a yi kari, kafin a zo karshe a yi wawa a rikice da kokawa. Kwalla ta ciko idanunsa, amma bai bari ta gangaro ba.
Reaction din Inna ya nuna masa Inna tana fushi da shi, duka tsayin wannan lokacin tana kullace da shi a kan banzatar da ita din da ya yi, ya shiga tambayar kansa me ya shiga kansa? All these while da ya manta da iyayensa, ya manta da girman hakkinsu a kanshi da kulawar da Allah ya ce ya ba su.
A lokacin ne Malam ya dawo daga rangadin da ya tafi wajen rakumansa a can wani kebantaccen muhalli. Tsufa ya bayyana sosai a tare da shi. Inna Bintou ce ta je ta sanar da shi zuwansu. Ko abinci kasa ci ya yi sai da aka kira mishi jikokin nashi, tare suka ci abinci a kwano guda yana tambayar Aalimah yanayin karatunta. Ta gaya masa komai lafiya, sannan ya ce da Basma, “Ina Mu’azzam? Ina kuma Abulkhair?†Cikin harshen buzanci.
Daddy yana yi musu sosai don haka suna ji sama-sama, sai ta juya nata harshen ta soma ba shi amsa cikin yaren Faransa.
“Monsiuer Abulkhair ya koma makaranta, bai ma san za mu zo nan ba, na tabbatar maka da sai ya ajiye jarrabawar da yake yi ya zo. Mu’az kuma yana nan yadda yake, annoying kamar koyaushe. Ya fi son rayuwa a LAS VEGAS fiye da ko’ina a duniya. Ba ya zuwa gidanmu don wai muna yi masa hayaniya. Mum and Dad, su suke zuwa wajen Mu’azzam. Grand-pere (kakanmu) Mu’az ba ya son mu ko kadan, Monsiuer Abulkhair kadai yake so a cikinmu. Ba dama mu yi magana in yana zaune he will throw a tantrum (zai yi masifa). He is the most annoying person in the world (ya fi kowa ban haushi a duniya), watakila shi ya sa ya kasa samun mataâ€. Ta karasa cikin dariya.
Tunda ta fara kakan yake sauraronta, yana duba maganganunta filla-filla. Shi kuma a wurinsa Mu’azzam is a nice person fiye da dukkan jikokinsa. Duk sanda ya tambaye shi me ya hana shi aure, sai dukkan walwalar fuskarsa ta canza, idan ya takura da tambayar sai ya ce,
“Idan ba ka daina yi min zancen aure ba Mallam zan daina kiranka a waya, ba kun yi min auren ba? Me na tsinta a cikinsa?â€
“Mu’azzam, ba mu muka yi maka aure ba, Babarka ce ta yi maka, babu saninmu, babu hannunmu. Babanka ya zo bagatatan ya ce za a daura maka aure don a ceci rayuwarka ba ka da lafiya, shi ya sa na amince wa Oussama ya je aka daura, amma ba mu san komai a kai baâ€.
Jirgin Ethiopian Air ya sauke iyalin Ishaq Raazee a filin jiragen saman Diori Hamani International Airport da misalin karfe goma na safiyar lahadi agogonsu na can. Sun samu Hamoud babban dan Uncle Oussama yana jiran saukarsu, shi da Balkisa ‘yar Uncle Edrissa babbar kawa ga Aalimah kenan kaf dangi. Iyalin Ishaq sun zamo kamar wasu taurari sha kallo a cikin gidan Malam Ibrahim Raazee a yau saboda murjewa da kyan fatarsu, duk da cewa kowa a gidan fari ne kal! Amma nasu ya sha bamban da na kowa. Kan ka ce meye wannan? Gida da makwabta ya kacame da murnar zuwansu, aka shiga aiko da akussan abinci daga kowanne bangare. Inna Kasisi kam ko a launin fuska babu wani alamu da zai nuna maka ta yi farin ciki da zuwan nasu, sabgogin gabanta kawai ta ke na dora sanwar abincin rana na gidan bakidaya, kasancewar abincin gandu ake yi a gidan.
Inna Bintou ce ke ta hidima da su tun shigowarsu da ‘yammatan gidan (jikoki) sa’anninsu. Daddy Ishaq kasa yi wa Inna Bintou alkunya ya yi irin wadda ya saba, wato fara shiga sassanta, dakin mahaifiyarsa ya shiga kansa a duke yana jin wani irin nauyi a zuciyarsa. Ta kara tsufa mai nuna alamun girma a tare da ita tsayin shekaru shidda da ya kwashe bai sako kafarsa a gidan iyayensa ba. Zama ya yi a kan kilishi ya tankwashe kafafunsa, zuciyarsa ta yi nauyi mai cakude da matsananciyar nadama. Sam ta ki yarda ta zauna a dakin, sai dai ta shigo ta dauki abu ta fita ba tare da ta dubi bigiren da yake ba.
Ko da ta gama girkinta ba ta zubo masa ba, amma ta zuba wa su Aalimah. Shinkafa fara tas! Da miyar dage-dage wadda ta ji fala-falan ganyen kabeji da naman rakumi zuku-zuku. Abincin ya yi masa kyau a ido, ya kuma ba shi sha’awa. Ya shiga tunano yadda suke santin abincin Innar shi da yayyensa Oussama, Edrissa da kaninsa Mansour da sauran kannensu ‘ya’yan Inna Bintou. Da yake a faranti guda ake zuba musu, in an cinye a yi kari, kafin a zo karshe a yi wawa a rikice da kokawa. Kwalla ta ciko idanunsa, amma bai bari ta gangaro ba.
Reaction din Inna ya nuna masa Inna tana fushi da shi, duka tsayin wannan lokacin tana kullace da shi a kan banzatar da ita din da ya yi, ya shiga tambayar kansa me ya shiga kansa? All these while da ya manta da iyayensa, ya manta da girman hakkinsu a kanshi da kulawar da Allah ya ce ya ba su.
A lokacin ne Malam ya dawo daga rangadin da ya tafi wajen rakumansa a can wani kebantaccen muhalli. Tsufa ya bayyana sosai a tare da shi. Inna Bintou ce ta je ta sanar da shi zuwansu. Ko abinci kasa ci ya yi sai da aka kira mishi jikokin nashi, tare suka ci abinci a kwano guda yana tambayar Aalimah yanayin karatunta. Ta gaya masa komai lafiya, sannan ya ce da Basma, “Ina Mu’azzam? Ina kuma Abulkhair?†Cikin harshen buzanci.
Daddy yana yi musu sosai don haka suna ji sama-sama, sai ta juya nata harshen ta soma ba shi amsa cikin yaren Faransa.
“Monsiuer Abulkhair ya koma makaranta, bai ma san za mu zo nan ba, na tabbatar maka da sai ya ajiye jarrabawar da yake yi ya zo. Mu’az kuma yana nan yadda yake, annoying kamar koyaushe. Ya fi son rayuwa a LAS VEGAS fiye da ko’ina a duniya. Ba ya zuwa gidanmu don wai muna yi masa hayaniya. Mum and Dad, su suke zuwa wajen Mu’azzam. Grand-pere (kakanmu) Mu’az ba ya son mu ko kadan, Monsiuer Abulkhair kadai yake so a cikinmu. Ba dama mu yi magana in yana zaune he will throw a tantrum (zai yi masifa). He is the most annoying person in the world (ya fi kowa ban haushi a duniya), watakila shi ya sa ya kasa samun mataâ€. Ta karasa cikin dariya.
Tunda ta fara kakan yake sauraronta, yana duba maganganunta filla-filla. Shi kuma a wurinsa Mu’azzam is a nice person fiye da dukkan jikokinsa. Duk sanda ya tambaye shi me ya hana shi aure, sai dukkan walwalar fuskarsa ta canza, idan ya takura da tambayar sai ya ce,
“Idan ba ka daina yi min zancen aure ba Mallam zan daina kiranka a waya, ba kun yi min auren ba? Me na tsinta a cikinsa?â€
“Mu’azzam, ba mu muka yi maka aure ba, Babarka ce ta yi maka, babu saninmu, babu hannunmu. Babanka ya zo bagatatan ya ce za a daura maka aure don a ceci rayuwarka ba ka da lafiya, shi ya sa na amince wa Oussama ya je aka daura, amma ba mu san komai a kai baâ€.