← Book details Aalimah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 62 OF 91

Sashe 62

Aalimah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A baya Nebrass ya damkawa Aboulkhair file din Mu’az, kulawar sa da komai da ya danganci lafiyarsa ya koma hannunsa, amma bayan dawowarsa daga tafiyar da yayi zuwa gida Niger da rasuwar Aboulkhair zaune cikin kwakwalwarsa, dole ya nemo Nebrass da ya fahimci yana cikin risk na tashin ciwon sa a kowanne lokaci daga yanzu, da kuma rokon da Malam Raazee ya yi masa na ya kai kansa ga likitocin sa, in ba haka ba bazai bar su Daddy a hannunsa ba.
Ko kafin Nebrass ya iso gidansa don ya duba shi, kasancewar baya gari yayi ‘yar tafiya zuwa Orlando Mu’azzam ya riga yayiwa gidansa mummunar illah, ya ji wa hannayensa ciwo, yayi asarar dukiya mai yawa, ya shiga black episode na aggressive tendency sabida ya dade baya shan magani kuma ya kasa karbar reality na rashin Aboulkhairi na har abada a tare dashi....
Nebrass da Daddy sun san juna tsayin shekaru goma sha a baya, tun Mu’azzam na Boston yake dubashi kafin ya shiga jami’a a nan Nevada (Las Vegas). Wato tun dawowarsu Massachusetts sakamakon lalurar Mu’azzam, aka hada shi da Nebrass a matsayin mashahurin neuropsychiatrist din da babu kamar sa a U.S. Tsayin lokacin da Mu’azzam ya dauka yana karbar treatment a hannunsa ne ya haifar da aminci da girmama juna a tsakaninsu, Nebrass ya zama kamar Babansa sabida ya manyanta. A wani bangaren abokin sa. Sannan Mu’azzam na yi masa alheri sosai.

Daddy na kan gadon asibiti, ga dori a ko’ina a kafafu da hannayensa, amma sosai yake magana, yana kuma gane komai da kowa da ke kansa sabanin su Aboubacar. Nebrass ya sameshi a wannan ranar da daddare, ya gaya wa Daddy kudin account din Mu’azzam sun yi kasa sosai, jinyarsu da tasa (wadda ta fi tasu cin kudi) ya lamushe komai, jinya a turai ba wasa bace har ta rayuka uku ban da shi uban gayyar mai karbar (special psychiatric care), ya kara da cewa ya yi reporting din rashin lafiyar Mu’azzam a kamfanin su a matsayin sa na likitansa don haka sun bashi isashshen hutu har zuwa ya samu ingantacciyar lafiyar da yake ganin zai iya komawa bakin aikinsa.
Kamfanin man petir na Chevron na ji da Engnr. Mu’azzam Ishaq Razee sabida hazaqarsa da zurfin ilminsa, don haka yana daga cikin ‘yan gaba-gaban goshin da ake ji dasu a Chevron Corporation. Ya gayawa Daddy salary account din Mu’azzam baya hannun sa, Mu’azzam bai bashi ba, kuma a halin da yake ciki bazai iya tambayar sa ba, don haka kudi tafiya suke ba sa shigowa.
Daddy ya ce ya zo masa da waya ya kira Mummy Zulaiha.

Mummy, wadda ke can Niamey cikin sabuwar rayuwa ta dayanta Allah da jin tsoronsa hadi da jingine farin ciki baki daya a muhallinsa, ta amsa wayar mijin nata a can kuryar dakin Inna Bintou. Gaba daya Mummy Zulaiha ta zama kashi da rai don rama, idanunta kyawawannan sun zama abin tsoro sabida yadda suka zurma cikin kwarmin idanunta. Fatar bakinta ta bushe rayas, alamun babu isasshen ruwa da jini a jikinta. Sakamakon rashin cin wadataccen abinci na lokaci mai tsawo. Tsufan ta da gayu ke boyewa a yanzu ya fito sarari bakidaya kowa na ganinsa.

Daddy Ishaq yace.

“Ku yi shiri ke da Gumsu ku dawo, ku taho da Khaleesat da Yesmin tunda mijinta yana nan tare da mu. Ki nemo (credit cards) dina a suitcase dina ku zo da su Las Vegasâ€.
Muryar Mummy Zulaiha gaba daya ta dushe sabida yawan kuka, wanda ya zama babban abin yinta tun ranar da aka ce da ita babu Aboulkhair, tun ranar da ta bude kyallen da aka rufe shi ko fatar fuskar sa ba ta yi saura ba, ta zagwanye kamar konewa ta wuta a sakamakon munin hadarin mota, al’amarin da ya jefa ta a wani hali na kaka-ni-kayi, har yau kuma ba ta fita daga cikinsa ba, da tashin hankalin da faruwar hakan ya jefa ta a ciki.

“Daddy Aalimah fa?â€

Mummy ta tambaye shi, wasu sababbin hawaye na tsinke mata. Jin cewa zasu koma rayuwa a Boston, babu Aboulkhairi babu mai dakinsa Aalimah.
Shi ma hawayen yake yi, ya ce, “Zulaiha babu magana a kanta yanzu sai ta haihu. Ki barta kusa da mahaifiyarta zata fi sakewa. Kuna tare ne?â€
Mummy ta rushe da kuka wurjanjan.
“Daddy cikin ma babu shi, ya tafi tare da Babansa. Na rasa laifin da mu kai wa Ubangiji Daddy, ya yi mana wannan talalar a lokaci daya…â€.
“A’uzubillah! Kul Zulaihatu! Maza ki yi istigfari ga wannan sabon. Shi Ya ba mu, ba tareda mun san zai bamun ba, kuma Ya ga damar karbe abinsa a lokacin da ya ga dama sabida ya fi mu bukatarsa. Maza ki yi tuba ga sabonki Zulaiha, ki gode maSa da kyautar rayayyun ‘ya’ya har guda hudu da ya bar maki. Ki roka musu rayuwa mai tsayi da albarka tareda ke.
Hakika rashinsa ba karamin rashi ba ne gare mu baki daya, amma tunda Mu’azzam ya jure ke ma za ki iya jurewa. Ki yi hakuri Zulaiha kin ji, ki yi hakuri, ki yi hakuri ki fauwalawa Ubangijiâ€.
Mummy na ci gaba da kuka da hawaye da majina, ta ce,
“Na yi hakuri Daddy, na yi hakuri. Ya ya jikinku?â€
“Muna kara samun sauki kullum cikin rahamar Allah, har an sayo kafar da za a sanya wa Mansour. Ki gaya wa Aalimah ya ce yana gaishe ta, amma ba yanzu zan hada su su yi waya ba, ina so duka su kara samun sauki a zukatansu tukunnaâ€.
Mummy ta ce,
“Daddy ko kudin tikiti babu a hannuna, namu duk sun yi expire, dole in shiga cikin tsohuwar ajiya ta. Allah sarki Mu’azzam, yau shares (hannun jari) din da ya saya min da kudina zasu yi mana ranaâ€.
Ya ce, “Amfanin neman naki kenan ai, ki rufa min asiri a sanda na gaza, ni ma yanzu aljihuna zan shiga mun cinye na Mu’azzam tas! Rayuwa kenanâ€.
7/4/21, 10:50 AM - Buhainat: KWATARKWASHI

Duk abin da Ishaq Raazee da dansa Mu’azzam suka mallaka cikin asusunsu na bankunan kasar America ya kusa karewa a wannan doguwar kwanciya jinyar ba da sanin kowa ba daga shi sai matarsa. Bayan su Mummy sun koma Hamoud ya hadu da amaryarsa Khaleesat don shi da direban Mu’azzam suka je debo su daga filin jirgi, sai dai kowanensu zuciya ba dadi. A motar babu wanda ya yiwa dan uwansa magana.
Kai baka ce masoyannan bane masu neman cinye juna sabida soyayya gabanin faruwar wannan al’amari. Saidai ko yaya Khaleesat ta motsa sai ta hango idanun Hamoud akanta ta mudubin motar tana mai mamakin rama da jemewar da yayi cikin ranta. Ta ji zuciyar ta ta tabu. Amma kallon su take shi da aurensa dake kanta matsayin silar rugurgujewar farin cikin iyayenta da ‘yan uwanta.
Dukkansu a tankareren gidan Mu’azzam suka sauka bayan Mummy ta je Boston ta debo katinansu na banki kamar yadda Daddy yayi mata umarni.
Mummy na tausayin wadanda ke kwance a asibiti, amma hakika tana tausaya wa Hamoud da Khaleesat. Wadanda suka dauki alhakin faruwar komai suka dora a kan ‘AURENSU’. Dalili kenan da ya sa suka bi suka tsani auren bakidaya. Har basa son ganin juna. Ga su dai a gida daya, amma Mummy sai ta takura wa Khaleesat ta ke gaida mijinta Hamoud da safe. A cewarta ita bata son ganinsa. Wajen aikinsa nata bukatarsa amma ya kasa tafiya ya bar Kawunninsa a gadon asibiti. A satin da su Mummy suka zo aka ci gaba da ba su treatment domin kafin su zo an yi suspending medical treatment dinsu saboda karewar kudin da ke cikin duka account din Mu’azzam dake hannun Dr. Nebrass.

A kokarin Mummy na rage musu kashe kudi, ta dakatar da sayo wa Hamoud abinci a restaurant da yaron Mu’azzam ke yi sau uku a rana, maimakon hakan sai ta yo cefane mai dimbin yawa ta ke dafa musu bakidayansu, su dama majinyatan asibitinsu ne ke ba su. Wanda ya dace da lafiyar kowannensu.

Mummy na zaune ita da Hamoud a falo aka kira shi a waya. Tana gani ya share kiran, akayi-akayi ya ki dagawa, shi kuma bai kashe ba.
Ta cira kai daga abinda take yi tace, “Mahmoud ba kiranka ake ba ne?â€
Ya ce, “To ya zan yi Mummy? Su na gaya min ne hutun da aka deba min na aure ya kare in koma bakin aiki, ni kuma Mummy ba zan iya ba, har yanzu cikinsu babu wanda ya fara taka kafafunsa a kan kasaâ€.
Idanunsa suka kada suka yi jajir, ya ce,
“Mummy duk aurenmu ne ya jawo ko?â€. Ya fara kuka.
Mummy ta tashi ta koma kusa da shi, ta manta da surukuta tasa hannu ta dafa bayansa tana rarrashinsa, sai ga Khaleesat ta fito daga kitchen da faranti shake da abinci a hannunta. Tana ganinsa yana kuka wani abu kamar kibiya ya soki zuciyarta, ta saki farantin a kasa, ita ma ta yi kan Mummy tana kuka.
“Mummy da na san abin da zai faru ke nan, da ban ce ina son auren ba!â€.
Hamoud ya dago daga jikin Mummy jin abinda ta fada, yai mata wani irin kallo da saida Mummy ta rasa inda zata sa kanta don kunya, yace.
“Yanzu ne kika san hakan???â€
Tace “ko dama can ni ban shirya aure ba, takura min ka yi†yace “nikuma fa da aka takurawa in taimaka in aure ki da wuri ake son yi miki aure ana tsoron kada ki rasa miji?†Sosai Khaleesat ta kulu da jin gorin da yayi mata tace “Ni ce zan rasa mijin? Ai wallahi ka dai fada ne kawai amma nice nayi maka alfarmaâ€.
Mummy Zulaiha ta rasa yadda za ta yi da su Khaleesat, suna manne jikinta sai gori suke jefawa juna, amma kallo daya zaka yi musu ka fahimci fatar bakin su ce kadai ke magana amma cikin kwayar idanunsu kauna ce da soyayya zallah. Cece-kucen su da kukan Khalisat shi ya jawo Gumsu da ke kitchen.
Ta fito ta tsaya daga bakin kofar shigowa falon da ludayin miya a hannunta, hannunta daya ta sa ta kama kugunta, daya hannun ta nuna su da ludayin miyar hannunta, ta ce.

“Mummy, me nake gani haka? Wannan wace irin tabara ce? Kukan soyayya ne wannan ko mene ne???â€
Chapter 62 · 0% Book details