Sashe 27
A Duniyata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Madaidaiciyar haraba ce wadda yanayinta yayi kama da gine ginen turawa ainun,irin gine ginen qasashen qetare,saidai kuma ba harabar kadai ba.....gidan dama sauran gidajen dake wajen dama unguwar gaba daya ba zaka dauka kana cikin abujar nigeria bane ba. Tamkar shi daya ne cikin gidan saboda rashin hayaniyar jama'a da kuma motsi,saidai a yawancin lokuta yakan zabi yanayi irin wannan don bawa zuciyarsa hutu da kwanyarsa. Bayan doguwar gwagwarmayar tabbatuwar buduwar kamfaninsa ap lagos kwanaki uku da suka wuce,sai ya zabi tsaiwa a abujan don ya sanya ido game da gudanarwar kamfanin koda na sati guda ne kafin ya koma bakin nasa ayyukan da suma a yanzu suke buqatar hankalinsa. Farin boxer ne a jikinsa da wata cotton shirt me gajeran hannu wanda ta bayyana ginuwar muscles na jikinsa,zubi da qirar qarfin da yake da ita. Tataccen natural ruwan blood orange ne a gabansa da ba'a sirka masa shi da sinadarin komai ba kaman yadda yake dabi'arsa ce a haka. Yafison komai natural da za'a sarrafashi da hannu,duk irin dukiyar da yake da ita amma yana sarrafa kanshi wajen sanin abinda zaici,wannan ya sanya yake da wata irin cikakkiyar lafiya. Wayoyin dake gabansa ya sake maida idanunsa akai,ya sake miqa hannu ya dauki daya daga ciki yana jujjuyata. Ba komai a ciki,baiga kuma komai ba. Dayar number maamah dince kawai akai,ba contact ko daya,kaman yadda ba massages a ciki,duk wani social app dake kai baya aiki ba'a budeshi ba,kamar yadda daya wayar take itama. Ba Facebook ba insta ba tiktok,ko watsapp babu duk da yana zaton an taba amfani dashi a kanta an rufe ne. Yanason ya zurfafa binciken sama da haka,amma sai wani sashe na zuciyarsa ya tunasar dashi haramcin zurfafa bincike akan dan adam......amma su ya halatta ya bincikesu har haka?,bayason maamah taci gaba da jefa qafafunta cikin halaka.....dole uwa uwa ce.....mutum daya ce duk duniya ke amsa wannan sunan......kamar yadda yayi imani yarinyar sai ya karanta mata menene rayuwa kafin ya sakar mata qofofin 'yanci ta yadda ba zata sake zama guba ga kowa ba. Maida wayar yayi ya ajiye,yana jin kamar zuwa yanzu ya kamata ya wuce gida hakanan ko don hankalin anni ya kwanta. Ya fahimci kamar tana zargin bai taho da yarinyar ba,amma da yake gwanar kawaici ce ita bata ce masa komai a kai ba. Ya sani ma inda farouq yana nan zuwa yanzu da tuni ya tona mishi asiri,sai Allah yasa suka shiga wata seminar kwata kwata bashi da lokacin kanshi. Wayarsa ya dauko ya lalubi saddiq "Kana ina ne?" Kanshi yadan shafa cikin jin shakka da nauyinsa "Katamfe extension" Ya amsa masa yana addu'an kada ya masa fada. Bayajin doguwar magana a kansa sosai,hasalima wata kasala ke damunsa,ruwan dumi yakeso yasha ya sake kwanciya,don haka kawai ya bashi saqon a dunqule "Kayi magana da team su shirya flight,gobe zamu wuce gida" "Okay in sha Allah" Ya amsashi yana jin dadin yadda bai matsa masa ba bare ya sanyashi baro soyayyar da yake raino a lokacin. Wayar ya mayar aljihun boxer din nasa,sannan ya dauke sauran kayayyakinsa da suke wajen ya fara saukowa daga farfajiyar dake a matsakaicin tsaho,shi ba upstairs ba shi ba qasa ba,amma lallai saiya biyo ta cikin dab da qofar parlor sannan ya shiga parlor din ya wuce duk inda zaije. Sam hankalinsa ba'a wajen yake ba sanda yake saukowar,cikin wani irin mamaki qofar parlor din ta bude sannan ta bayyana gaba dayanta cikin ba zata. Saura kadan ya hada jiki da ita,don ta shigo ne da wani irin zafin nama,banda shima me zafin namar ne yaja baya da sauri da ba abinda zai hana jikkunansu haduwa guri guda. Cikin second biyu ya maido hankalinsa jikinsa,suka fara yiwa juna kallon kallo. Fareeda,d'iya ga ambassador din nigeria a qasar china. Matashiyar da duniya ke gara mata fiye da yadda takeso,ta samu gata.....ta samu ilimi.....ta mallaki kyau......tana da tsananin wayewar da bata barinta fayyace daidai a addininta da ba daidai ba.......wayewar dake haska mata komai ya yiwa ranta dadi.....komai ranta keso daidai ne,wayewar da gatan da sukayi mata jagora tare da nuna mata kome takeso lallai zata sameshi ta kowacce hanya. Doguwa ce fara sannan kuma siririya,wadda ke tattalin jikinta da amfani da mayuka da kuma supplement masu tsananin aji da tsada ba tare data bari zallar hutun da take ciki ya zama jagoran gyaruwar komai nata ba. Zai wahala ka kalleta ka kirata da mummuna kai tsaye......saidai bata cikin sahun kyawawan da kallo daya zai sanya ka gamsu kyakkyawa ce,tana mataki na kyau a middle class....duk da tana kai kanta high class a koda yaushe tana ganin ta cancanta da aje kanta a can. Ta jima tana jin sunan muhammad fu'ad jadda yana gilmawa kunnuwanta.....wani lokaci daga bakin manyan friends dinta yaran gata irinta,wani lokaci kuma daga bakin mahaifinta. Saidai ko sau daya hakan bai taba jan hankalinta ba,saboda tana da wata izza akan namiji da saidai ya nemeta,don ta hada komai da take ganin babu kalar d'a namijin da bata zarce masa ba......in fact tana tunanin ma ita har yanzu cikin wannan duniyar da muke ciki babu kalar mijinta. Sau tari idan sunan ya gilma mata kawai tana surantashi kamar sauran alhazawan masu kudin dake hauka a kanta,masu shekaru,kai duka furfura ko kuma furfurar ta fara ketowa,masu qiba da ajiyayyen tumbi,masu matan aure uku hudu da tarin 'ya'ya. Bisa rakiyar tilas data yiwa mahaifinta nigeria don zuwa bikin bude company din JADDA SPARKLE WORLD daga nan su qarasa garinsu gaisuwar mutuwar qanin mahaifinsa da ya kusa cimma wata uku da rasuwar amma bai samu zuwa ba. Kafaffe kuma tsayayyen yaya ga kakansu qwaya daya daga rage shi ya zuba bala'i akan fareeda,sam yarinyar ba wanda ta sani a cikin su kaf,saboda rabonta da garin tun batafi shekara biyar ba a duniya,basa qaunar zuwa kwata kwata,wannan ya sanya mahaifinta ambassador khaleed mustapha ya tilasta mata saboda rufe bakin mutane. A karon farko da sanarwar bayyanar me kamfanin kan dandamalin jawabi ta ratsa microphone din,ta daga kanta daga kan wayarta da take qoqarin posting hotunanta a shafukanta,ta kuma saukesu akan muhammad fu'ad dake tsaye gaban abun magana yana daidaitashi yadda zai dace da bakinsa. Wata lafiyayyar suit ce a jikinsa data tsone idon duk mutumin dake zaune a wajen. Suit din da musamman aka sarrafata tun daga qasar Italy saboda rana irin wannan. Ta sake fidda tsahonsa da murjewar jikinsa da wani irin mahaukacin kwarjini da ya zame masa garkuwa wajen karya maqiya da abokan gabarsa. Idanunsan nan masu wani irin kyau da bata taba ganin irinsu ba suna yawo saman fuskokin tarin al'ummar da sukazo wajen saboda shi yayi cikakakkiyar sallamar da duk wanda ya sanshi yasan wata abace da baya tsallakewa yinta ako ina koda wanne irin mutane ne a gabansa,ba ruwansa da banbancin addini qabila ko kuma yare.....ako yaushe yana yin abinda xai ci gaba da tuna masa....zai kuma ci gaba da bayyanawa ko waye suke tare cewa SHI MUSULMI NE. Sanda ya fara jawabin taron da wani irin tataccen turanci da lanqwashewar harshen da zaka rantse cikin fadar queen Elizabeth aka haifeshi sai dataji kowacce gaba ta jikinta ta saki. Wani irin abu da bata taba ji akan kowa ba ya soma bin sassan gudanar jini na jikinta yana aika saqo wa zuciyarta,wanda kafin ya kammala bayanansa ya sauka gaba daya ya wuce da nutsuwarta dama zuciyarta gaba daya. Ta fahimci akwai ire irenta da yawa a wajen bayan tashin taron,saidai ba alamun samun fuska ko dama daga wajen kowacce diya mace,wannan dalilin ya sanya tabi ta hanyar mahaifinta. Ta samu damar gaisawa dashi,saidai abu na farko daya sanyaya mata jiki hannu data bashi da nufin suyi hand shaking kamar yadda yake gaisawa da kowa,sai ya jefa mata wani irin kallo ya maida hankalinsa ga wani abu na daban. Bata haqura ba sai data sanya mahaifinta ya nema ganawa dashi a masaukinsa dake banana island kafin yabar lagos kenan,a nan ta fito kanta tsaye ta gaya masa abinda ke dauke dashi,amma sai ya saki wani murmushi daya qarasa qona mata ruwan jiki gaba daya,ya kuma bata saqon daya kusa tashin kanta a aiki. "Am so sorry kinji....ni bana soyayya.....infact ba time na ire iren wadannan shirmen,ina fata kema zaki maida hankalinki akan karatunki okay?" Gaba daya shirme ya dauki abun,yadda ya tsaya ya mata maganar ma ta tabbatar albarkacin mahaifinta taci. Still bata jin zata iya haqura dashi,ta samu daman ganinsa a karo na biyu ba tare da yasan ita bace. A nan ta gane ainihin wayeshi,ya fiddo mata true color dinsa,abinda ya birkitata kenan,batayi qasa a gwiwa ba ta bashi tabbacin bata taba neman abu ta rasa ba.....a kansa kuma ba zata fara ba,zatayi duk yadda zatayi don ganin ta mallaki soyayyarsa ta kuma mallakeshi.....ta kuma ci masa alwashin duk inda ya shiga tana biye dashi har sai randa ta samu abinda takeso. Ko a yanzun zare rafkeken sunglasses din idanunta tayi tana qoqarin sakar masa murmushi,yayin da ransa ya motsu da zummar baci amma kuma mamaki ya mamaye wannan gurbin. "May i ask who's let you in?" Yayi maganar yana qoqarin danne fushinsa. Murmushi ta kuma saki tana rolling idanunta cikin salon jan hankali "As your guest,i think you should welcome me first" Ta furta tana narke murya. Baya ya sake ja kadan ganin tana qara takowa inda yake "What brings you here?" Wannan karon ya fada adan tsaurare,alamun bacin ransa suna fitowa fili. Kallonsa tayi a kaikaice tana sake yadda da maganganun da aka gaya mata a kansa. He's not a womanizer,he's not into playing games with women......ta yaya kike tunanin zakiyi winning kansa?" . Ta tuna da maganar da daya daga cikin qawayenta suka mata. A lokacin ta dauki zancan nata ne a matsayin kishi,saboda samun cikakakkiyar dama da tayi da take ganin zata kawoshi cikin rayuwarta,damar da mata da yawa suke nema basu samu ba. "Am here for you fu'ad.....please ka bani gurin zama tukunna mu tattauna a nutse" *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 _ZAFAFABIYAR_ "Get out of my house" Ya fadi ba alamun fara'a ko walwala a tattare dashi. Wannan fuskar me cike da miskilanci,wadda zai wahala kaga wani abu me kama da murmushi a kanta ta sake dinkewa tsaf "Please mana" Ta fada da wata irin shagwaba tana hade hannayenta waje daya "Zaki