← Book details Raina Kama Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 24 OF 66

Sashe 24

Raina Kama Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

.................Jin tsayuwar motoci ya saka Ameer lek'awa ta window, juyowa yay ya kalli Galadima, “Ranka ya dad'e y'an sandane”.
Baki Galadima ya ta6e, ya share tamkarma baijiba, yana cigaba da bud'e wasu file daya fiddo a briefcase. Saida yaja kusan 1 minute sannan ya mik'ama Nuren dake kusa dashi wasu files, ya zaro takarda kuma yay rubutun dabai Gaza layi biyarba ya mik'ama Ameer da wata k'amar waya a kwali.
Kar6a Ameer yazo yayi, batareda Galadima yayi magana ba ya nuna masa window.
Muftahu daya fahimta yace, “Ameer ka jefa musu takardan da wayan”.
Ameer ya amsa da to, yanufi window d'in, cikin dabara ya jefa kwalin da takardar.
Wani d'ansanda dayaga tahowarsu yay saurin zuwa kusada window d'in, ALLAH yabashi nasarar cafewa.
D.p.o dake tsaye tare da sauran police ana shawarar yanda za'a shiga gidan ya kaimawa.
Yay salute nasu kafin ya Isar da sak'on dukda yasan duk sunga daga ina kayan suka fito, d.p.o ya gyara tsayuwarsa yana fad'in “bud'e kwalin mu gani”.
Bud'ewa yayi, yaciro wayar yana cewa, “wayace sir”.
Cikin ta6e baki d.p.o ya jinjina kansa, yace, “takardar fa?”.
Itama bud'ewa yayi, yafara karanto abinda ke jiki, wanda Galadima ya rubuta da harshen nasara.

*_Kamar yanda suka fad'a Muhammad Sameer ba d'an ta'adda baneba, inhar zakubi yanda nace lallai yarannan zasu fita lafiya, idan kuma har kuka nuna k'arfin iko, zanta jeho muku gawarsu d'aya bayan d'aya ta saman benenan, ga wayanan, idan kuna buk'atar magana koni ina buk'ata ta wadatar, Dan kar wani yay gigin cewa zai shigo. Idan nayi ba dai-daiba a gafarceni👏🏻_*

Daga d.p.o har jama'ar dake kusa dashi duk ajiyar zuciya suka sauke, ya jinjina kai yana cije bakin mamaki, cikin sauke numfashi yace, “saimu bishi yanda yakeso mugani, idan munga zai mana wasa da hankali sai a d'auki mataki, C.. babangida a zagaye gidan”.
“Ok sir”. C babangida ya amsa yana salute nashi.
Dandanan suka warware wani blue d'in zare suka zagaye gidan dashi, mutanen anguwa dasuka fara fahimta harsun fara taruwa kallo, harma wad'anda sukaji a labaran sunfara gangarowa anguwar damin ganema idonsu.

Duk abinda ke faruwa Galadima Na zaune k'afa d'aya kan d'aya yana kallo ta CCTV, sai famar buga pen yake saman la66ansa a hankali, suma dai su Muftahu dasu Harun suna kallon komai.

Kujera aka kawoma d.p.o ya zauna, dayake da sauran safiya babu maganar neman runfa ko umbrella.
Wayar d.p.o ya kar6a da kansa, dan case ne Na manya IG da kansa yakirashi, yakuma abbatar masa shima yana nan zuwa.
Shiru d.p.o yay yana bincikar wayar da Galadima ya aiko da ita, babu komai a cikinta sai Number guda d'aya, baice komaiba yaciro wayarsa yayma IG bayanin komai.
Daga can IG yafara fad'a, wai tayaya zasu saurareshi, bayan d'an ta addane, duk Wanda zai iya kidnapping aiko d'an ta'addane, kawai su nuna masa k'arfin iko wajen ku6tar da yaran.
Shidai d.p.o ya kwantar da murya cikin sigar lallashi yace, “Nidai Sir da ace za'abi ta tawa daminbishi a hankali, maybe akwai sak'on da yakeson isarwa, karfa mu manta shima d'an manyan mutanene, shikansa akwai sarauta mai daraja a kansa, ai mai martaba bazai ta6a jin dad'iba shima, tunda ya buk'aci dama mu bashi, idan munga batai manaba saimu d'auki mataki”.
IG yace, “shikenan, Ku kirashi muji miyake buk'ata, nima a had'a dukkan maganar da zakuyi dani naji komai, dukda munama hanyar isowa yanzunan”.
Cikeda farin ciki d.p.o yace, “ok sir”.
Duk kayan aikin dasuke buk'ata suma sun tanadesu, yayinda y'an jarida suka fara isowa wajen.
Shima C.P ma saigashi ya iso, duk suka k'ame wajen salute nashi har d.p.o.
Ya amsa musu cikin jinjina kai, sannan ya buk'aci jin mi'ake ciki?.
Bayani d.p.o d'in yamasa, shima ya gamsu da shawarar abi komai a sannu d'in.

Galadima ya murmusa yana lumshe idanunsa yana sauke ajiyar zuciya. Saboda dukkan wayar da d.p.o yay da IG a kunensa ne.
Sudai su Nuren sunyi jugum-jugum Dan son ganin minene shirin Galadima waine?, da har yaza6i fiddo kansa wa duniya a matsayin mai laifi?.

Kiran da C.P yayi da kansane ya shigo wayar Galadima bud'e ido yayi yana kallon su ta CCTV, sannan yay picking call d'in, shiru yay yak'i magana, saida C.P ya fara masa sallama sannan ya amsa.
C.P yace, “Ranka ya dad'e barka da safiya”.
Baki Galadima ya ta6e, ya amsa da “Barka dai”.
Gyara zama C.P yay yana kallon saman gidan, duk su Galadima suna ganinsa, yace, “Ranka ya dad'e muna saurarenka, ka fad'i buk'atar taka, inhar batafi k'arfinmu ba za'a biya maka insha ALLAH ”.
“Humm” Galadima ya fad'a yana mik'ewa tsaye, duka hannunsa Na zube cikin aljihu, dayake yana amsa call d'in ne da abin da ke kunnen sa.
Falon ya shiga zagayewa cikin takunnan nasa na k'asaita da izza, saikace namijin tantabara yana gwada gasar tafiya a gaban matarsa😜🤣.
Suko sai binsa da kallo suke tamkar wani magiji.
A hankali yace, “Buk'atata ta farko shine iyayen yarannan su fiddo Alhaji Auwal fharuk, idan sunyi haka lallai zakuji manufata kai tsaye batare dana ja muku raiba, Dan nima ina buk'atar hutu”.

C.P ya shiga jinjina kansa kawai yana sauraren Galadima da dukkan sauran police d'in dasuma sukeda alhakin jin komai ta hanyar abinda suka saka a kunne.
Bai k'ara komaiba ya yanke wayar, Yakoma mazauninsa ya zauna yana kallon yaran dasuma dukshi suke kallo, d'an murmusawa yayi yana d'aukar ruwan daya ajiye, saida ya bud'e murfin ya mik'ama Wanda yake kusa dashi.
Shima yay murmushi yana girgiza kai da fad'in “A'a ranka ya dad'e, Na gode”.
Galadima ya mik'ama sauran suma, amma duk sai sukace A'a, murmushi yayi yasaka kayansa a Baki yasha, yana kallon Harun daya zuba masa ido, rabi yasha ya mik'ama Harun sauran, amma saiya kauda kansa gefe, Galadima ya ta6e baki yana d'aga kafad'a alamar kaika Sani.
Sauran ruwan ya ajiye yana kuma kallon yaran, da hannu yakuma yima Na farko alamar yaya sunansa?.
Bai fahimtaba Dan haka ya kalli Na kusa dashi, sannan yakuma kallon Galadima yana nuna kansa da fad'in “Sunana wai?”.
Galadima ya jinjina kai yana lumshe idanu.
“Sunana Ahmad Bana bb gana".
Galadima ya had'e yatsansa babba da manuniya👌🏻 alamar nice name.
Ahmad yace, “Thanks you sir”.
Na kusa dashi Galadima ya sake nunawa, shikuma yace, “Ahakam Balala”.
Shima jinjina Galadima ya masa, nakusa dashi kuma Gebirel Timothy, sai Nerh-nerh Bilkisu Mansur, Rahma Abdul-naseer, Yassar Mamman, Sulaiman sager sulaiman, Marcel Miracle.
Cikin murmushi Galadima yace, “Duk sunan y'an gayune daku”.
Gaba d'aya suka sanya dariya, banda Harun da Alhaji Darma, Harun yasan Galadima sosai, dama yanada tsokana idan yaso hakan, koda kai zakayi dariyar shi ya fuske kuwa.
Galadima Yakuma fad'in “Duk kun kammala Secondary schools ne?”.
Duk suka amsa da eh, kowa yashiga fad'a masa matsayin karatunsa da abinda suke karanta, dukda ba magana yakeba murmushinsa Na sakasu farin ciki.....

.............★

A can kuwa waje, police nata k'ullawa da kwancewa da jiran isowar IG, Dan yace su jirayi zuwansa.
Dukda Galadima yana hira da yaran hankalinsa nakan saurarensu ta abinda ke kunnensa.

Babu dad'ewa saiga IG ya iso, kar6ar wayar yayi da kansa bayan sungama salute nashi ya zauna, ya kuma kiran Galadima da kansa.
Galadima yay picking amma sai yak'i magana yanzunma, hakanne yasaka IG yin magana cikin takaici da fusata, “Kai bamason rainin hankali, kafad'i abinda kawai kakeso duka amaka kabasu yaransu”.
K'ala Galadima bai ceba ya yanke wayar.
Mamaki ya kama IG, C.P yace, “Sir dadai anyi hak'uri an musu magana kawai suma aji mizasu ce”.
Cikin matuk'ar takaici IG ya dangwarar da wayar yana huci da cire hular kansa, da hannu yayma C.P umarnin a kirasun.
Da Sauri Aka danna kiran wayar d'aya daga cikin su, dama duksun tattarune a waje d'aya, Dan haka ya saka Hans free duk sunaji.
C.P da kansa ya sanar musu buk'atar Galadima, kallon kallo aka dungayi, kowa ya kasa magana, Shidai C.P ya yanke wayar yana fad'in “nanda mintuna 10 zasu kira”.
Suna ganin C.P ya yanke wayar suka hau cecekuce da fad'in yaronan yagama raina musu hankali, kaza-kaza dai, wasu suna bada goyon bayan abadashi sai abi tawata hanyar a kar6i camera d'in saboda suna matuk'ar k'aunar yaransu, wasu kuma sunce kar'a sakeshi, Dan haka tamkar tonon sililine agaresu. Sundai kasa samun matsaya har 10minute's ta cika C.P ya sake kira. Ba'a samu Wanda ya iya d'agawaba harta yanke.......

(**************************)

Zuwa yanzu gidan su Munaya sunsan halin da'ake ciki game da Galadima dakuma maganar fitowar Abba, Dan y'an jarida nata yad'a komai live a gidajen redio da TV, ga masu d'auka a waya y'an gani da ido dasukazo suka kafa suka kuma tsare.
Kuka dai Munaya Na shansa, tayi wujigi-wujigi, miji da Uba duk suna cikin matsala, da k'yar inna ta bata tea tasha da kanta, yaranma sai an mata dole take shayar dasu, ta lafe jikin innarsu tanata hawaye daga ita har Munubiya, yaran sai innaro dasu mama rabi'a da sukazo gidan Tun farar safiya ke kula dasu.

A can gefe kuma Zarah da Siyama NATA zagayen d'akin Abba Dan son samun damar shigewa su d'auki camera🤦🏻‍♀.

**************************

Alhaji Hallurune yabasu shawarar su d'auka kawai suce su k'arya ake musu Alhaji Auwal baya hannunsu.
Wannan shawarar sukabi, da Kansu suka kira C.P suka shaida masa. Sharri Galadima ke musu.
Galadima dakejin komai yayi murmushi kawai yana cizar lips. Laptop d'insa ya janyo yafara danne-danne.

Daga can C.P ya yanke wayar yana Neman izinin IG domin kiran Galadima shima.
IG ya bada izini zuciyarsa Na sakejin zafin Galadima da rainin wayonsa.

Saida ta kusa tsinkewa sannan Galadima yay picking, C.P ya sanar dashi amsar da suka bada.
Cikin murmushi mai sauti da har su C.P sukeji Galadima yace, “ga za6i biyunan, kodai su fad'i inda yake, kokuma su sakoshi, kokuma shi yasaki video d'in yanda suka saceshi”.
Jikin C.P fa kansa yafara sanyi, Dan yafara hango k'amshin gaskiyar Galadima.
Chapter 24 · 0% Book details