Sashe 17
Raina Kama Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Tunda yadawo salla ya koma barci, saboda jiya bai wani samu yin isasheba, wajen 10 ya farka, brush kawai yayi yazo ya zauna yana hada wasu takardu, sosai aikin ya d'auke hankalinsa saboda muhimmancinsa, sauban datun d'azun yay shirin tafiya yagaji da jiran fitowar Galadima Dan haka yazo yaymasa knocking, Dan yanason biyawa wajen Munaya kafin ya wuce.
Galadima dake zaune bakin gado ya baje takardu yana kuma rubutu a jikin wasu ya d'aga kai ya kalli Computer d'in dake hasko masa dukkan CCTV camera's d'in sashen nasa, ganin Sauban ne sai ya d'auke idonsa yace ya shigo.
Zama sauban yayi saman stool d'in mirror ya gaida Galadima, hankalinsa nakan aikin dayake ya amsa. yace, “Dama katashi?”.
“Wlhy Yaya tun d'azun Na tashi, naga baka fito baneba gashi inason kafin Na wuce nabiya Na gaida Aunty gimbiya naga my Triplet's kuma”.
Galadima baice komaiba, sai had'e takardun gabansa daya shigayi, Sauban yamatso bakin gadon yana tayashi, saida suka gama tsaf, ya shiryasu cikin wani k'aramar briefcase sannan ya kalli Sauban dake zaune, “Mik'omin System d'incan”.
Sauban yad'an marairaice fuska cikin tausayawa. Yace, “haba yaa Sam kad'an huta mana”.
Da mamaki Galadima yace, “to idan Na huta kaine zakamin aiki?”.
Girgiza kai Sauban yay alamar a'a. Ya tashi ya d'ako masa.
Kar6a Galadima yay yana girgiza kansa saboda ganin yanda Sauban keta 6ata fusaka, a zuciyarsa yace bazaka fahimtaba yaro.
Batare da sake kallonsa ba yace, “yanzu mikake buk'ata kenan?”.
“yaa Sam kud'in wajenafa basuda yawa”.
“Humm” Galadima ya fad'a hankalinsa akan aikinsa. yace, “Aikai dama baku iya tausayin kud'iba kai da Samha, mutum yarasa uwar mi kuke saya? Kaje zan turo maka, Dan yanzu kama nima buk'atar kud'in nakeyi, gashi sunyi cak, nasan kuma daga inno har papi idan suna dashi baka zasuyi”.
“shikenan yaya, amma Dan ALLAH ko kad'anne”.
“ka duba cikin kayan dana cire, maybe ka samu”.
“yauwa Yaa Sam d'inmu. ALLAH ya k'ara girma”.
Galadima Dai baice komaiba, ya kwaso kud'in duka yana fad'in “na kwashe duka?”.
Kai kawai Galadima ya d'aga masa.
Sauban yazo ya rungume Galadima ta baya yana godiya, sannan ya sakesa. Murmushi Galadima yayi yana fad'in “ALLAH ya gyaraka Sauban”.
“Amin yayana”. Sauban ya fad'a cikin dariya.
Sunyi sallama ya tafi akan cewa shima saiya zo, yakuma gaida su papi.
*****************
Munaya taji dad'in ganin Sauban, sund'an ta6a hira sannan yamata sallama ya tafi tana shaida masa ya gaida mata su inno da k'yau, har k'ofar gida ta rakoshi, dukda dai bata fitoba iyakarta jikin gate, saida yashiga mota sannan ta koma ciki, tanamai jin k'aunar ahalin Galadima har cikin ranta.
************\/**********
Galadima na shirin fita kira ya shigo wayarsa, saida yagama d'aura belt d'in da yakeyi sannan ya matsa gaban gadon ya d'auki wayar, a dai-dai lokacin kiran ya kuma shigowa, ganin Sir Isa saiya d'aga.
Ko gaisuwa basuyiba yace, “yalla6ai kaga kuwa aika-aikar da ake neman mana?”.
“Aika-aika kuma? Tami?”.
“Tabbas ansaka wani yamaka kutse cikin Computer, Nazatama kagani?”.
Gaban Galadima ne ya fad'i babu shiri ya yanke wayar, system d'insa ya jawo ya zauna bakin gadon, “innalillahi...” Yashiga ambata zufa Na tsatstsafo masa saboda abinda yagani Na shirin faruwa, ya manta daya gama aiki bai saka security a matakin farkoba, saurin sakawa yayi, dukda yasan babu tabbacin zai iya dakatarwa ahakan kawai da yayi, ya ajiye lap-top d'in yana mik'ewa da hanzari, sauri d'aukar rigarsa yayi ya saka, yana saka bottoms d'in a tsananin hanzarce, haka dai ya k'arasa shirin a gaggauce, ya d'auki abinda zai d'auka yafito, babu gaisuwar Wanda ya amsa, hannu kawai ya d'aga musu yanufi mota yashige da kansa yaja ya fice daga masarautar, Wanda yatafi kiran Sarkin Mota duka iso tare, duk mamaki ya kamasu, yau Galadima da kansa yaja mota, anya kuwa lafiya?.
Ganin wannan bazai musuba sarkin mota ya shiga mota shima ya bishi.
Yana tuk'i suna waya da Vijay abokin aikinsa Na India, a haka ya iso gidansa dake bayan gari, kusan lokaci d'aya suka Isa da sarkin mota, ganin Galadima zai fita ya bud'e gate da kansa, shi saiya kashe motar dayake ciki da sauri ya fito yazo ya bud'e masa ya shige, bai bisaba, tunda Alhmdllh yaga dai inda yazo, maybe kuma baya buk'atar kowa a wajene shiyyasa ya buk'aci tahowa shi kad'ai.
Wani d'aki dake cikin bedroom d'in gidan ya bud'e ya Shiga, bazaka ta6a tunanin akwaima d'aki a wajenba, da y'ar k'ura a d'akin, amma hakan bai damu Galadima ba a yau, k'yallen da aka rufe kujeru da Computers d'in d'akin yashiga yayewa, da sauri ya fito zuwa can bayan d'akunan, yad'anyi ajiyar zuciya saboda ganin Gen... d'in gidan akwai fetur, dayake yad'an zazzo gidan kwannan, tadawa yay ya kuma komawa cikin gidan, ya kunna komai sannan ya zauna a kujera, medical eyeglasses ya saka, idonnan yayi jazur saboda 6acin rai, duk jijiyoyin kansa sun mimmk'e, hakama gashin jikinsa, kallon farko zai tabbatar maka ran maza ya 6aci. Koma a yanda yake sarrafa Computers d'in.
Abinda ke kunnensa kawai naga ya danna yanayin kwatancen d'akin da za'a sameshi.
Mintuna 3 tsakani saiga Sir Isa da Baffi sun shigo, saikuma ga Sauban Wanda harsun d'auki hanya Muftahu ya kirashi akan ya dawo, dole ya dawo masarauta, shine suka fito shida Muftahun.
Sir Isa da Sauban duk zama sukayi, Galadima Na Sanar musu abinda zasuyi.
“Gaskiya shegene guy d'innan yalla6ai, wlhy yasan Computer, kagafa yana Neman lalata mana dukkan security d'inmu.......”. ‘hankali tashe sir isa yake magana.
Sauban kam har kwalla ta cika masa ido.
Galadima baice komaiba, aikinsa yake iya iyawar k'arfin zuciya dana k'wanji.
Sai Baffine yad'an bubbuga kafad'ar Sauban yana fad'in “ka kwantar da hankalinka Sauban, insha ALLAH bazasuci nasaraba, kacigaba dayin komai a nutse kaidai”.
Sauban ya kad'a kansa yana share hawaye.
Galadima dayay zufa sharkaf ya kalli Sir Isa, yarigada yaci k'arfinmu kafin muzo, k'ofa ukuce kacal ya rage masa bud'ewa yasamu dukkan komai, abinda zamuyi mu bud'e masa sauran kawai, bayan yashiga ciki insha ALLAH inada wata dabara”.
Muftahu yace, “Amma Ranka ya dad'e hakan riskine gaskiya, idan kuma shi yanada plans akan hakan fa?”.
“Gaskiya ka fad'a Muftahu, amma hakan shine kawai hanya mai sauk'i da zamubi, inhar muka bari harya bud'e da kansa lallai zai lalata komaine, Dan wannan shine shirinsu”. Sir Isa ne mai maganar.
Galadima ya danna abin kunnensa yana fad'in “Vijay mubashi dama kawai, a lokacin daya shiga kaikuma ka tabbatar da ka zuk'e dukkan nasa shirin, ga wata akwatinan dayake yawo da ita a bayan handle d'in Computer d'insa, karka ta6ata Dan makircine ya shirya a cikinta, munayin kuskuren ta6awa labari zaisha Banban. Alex yay gaggawar had'amin sabbin Securitys muga kozasu ja hankalinsa can, ga hoton yaranan zan d'ora masa, dasu zaiyi amfani, dan dolene mu kauda masa hankali, yasan mi yakeyi sosai”.
“Ok! Ok! muje zuwa kawai” vijey ya amsa a hanzarce.
Da sauri Galadima ya maida kallonsa ga Sauban yana fad'in “dakaje duk ka d'auki su Amaturrahman ne?”.
“Eh yaya dukna d'aukesu”.
“A lokaci d'aya ko daban-daban?”.
Na d'aukesu lokaci d'aya, nakuma d'auki kowa shi kad'ai”.
“Alhmdllh taso nan”.
Tashi Sauban yayi ya matsa inda Galadima yake, wani glass Galadima ya tura masa, yace, “'Dora duka hannayenka anan mugani”.
'Dorawa Sauban yayi, bayan ya ta6a wani farin Abu da Baffi ya bashi, shatin hannun yaran suka bayyana, dayake yayi musu wasa sosai, amma kuma hakan bazai gamsarba.
Daga can Alex yace bazaiyiba, dole akawo yaran. Shima Galadima ya tabbatar bazaiyinba, sai hankalinsa ya kuma tashi, yaran sunyi k'ank'atar daza'a fito dasu daga gida.
Muftahu yace, “Ranka ya dad'e bara kawai naje Na kawosu inaga zaifi sauk'i”.
Baffi yace, “hakan shine kawai dai-dai sai dai bakai yakamata kajeba, a kira mahaifiyarsu tabama Wanda zai iya 6adda bamanni wajen kawosu, kuringa tunawa sumafa idonsu nakan kowane motsinmu a yanzu, shiyyasa tun a jiya naima Sameer hannunka mai sanda akan hakan”.
Galadima daya zubama Computers d'in ido kawai yana kallon 6arnar da ake shirin masa. Ya mik'e tsaye yana fad'in “Muftahu ka kira mai taxi d'innan yaje inda yata6a ajiyeta za'a kawo masa yaran”. fitowa yay daga d'akin yana k'ok'arin neman number Munaya ya kira.
Bugu biyu Munubiya da wayar ke hannunta ta d'aga, tana mannama Munaya wayar a kunne, bai amsa sallamarta ba yace, “Yanzunnan ki bama Innaro da laraba su Abdurraheem, sufito bakin layinku akwai mai taxi zai d'akkosu”.
Cike da mamaki Munaya tace, “yalla6ai ban ganeba?”.
A tsawace yace, “basai kinganeba, Dalla malama kibasu karki 6atamim lokaci”.
Sosai Munaya ta tsorata da tsawar tasa, kad'an yarage wayar ta su6uce mata ta daiyi azamar rik'ota, batada za6in daya wuce bin Umarninsa, dukda hankalinta bai kwantaba da hakan. Yanda yace ayi haka tayi, innaro da laraba Na fitowa suka samu mai taxi yana jiransu.
Cikin mintuna k'alilan suka iso, Muftahu da Sauban sukazo suka kar6i yaran, akabar su innaro a mota zasu jira.
Akan wani Abu akad'an d'orasu, da hotonsu ya fota a Computer d'in sai'a ciresu, sud'uka duk aka d'ad'd'orasu, sannan su Muftahu suka maidasu wajensu innaro aka koma dasu. Sudai duk mamaki ya cikasu akan miya faru? Basuda mai basu amsar wannan lamari.
Galadima dake zaune bakin gado ya baje takardu yana kuma rubutu a jikin wasu ya d'aga kai ya kalli Computer d'in dake hasko masa dukkan CCTV camera's d'in sashen nasa, ganin Sauban ne sai ya d'auke idonsa yace ya shigo.
Zama sauban yayi saman stool d'in mirror ya gaida Galadima, hankalinsa nakan aikin dayake ya amsa. yace, “Dama katashi?”.
“Wlhy Yaya tun d'azun Na tashi, naga baka fito baneba gashi inason kafin Na wuce nabiya Na gaida Aunty gimbiya naga my Triplet's kuma”.
Galadima baice komaiba, sai had'e takardun gabansa daya shigayi, Sauban yamatso bakin gadon yana tayashi, saida suka gama tsaf, ya shiryasu cikin wani k'aramar briefcase sannan ya kalli Sauban dake zaune, “Mik'omin System d'incan”.
Sauban yad'an marairaice fuska cikin tausayawa. Yace, “haba yaa Sam kad'an huta mana”.
Da mamaki Galadima yace, “to idan Na huta kaine zakamin aiki?”.
Girgiza kai Sauban yay alamar a'a. Ya tashi ya d'ako masa.
Kar6a Galadima yay yana girgiza kansa saboda ganin yanda Sauban keta 6ata fusaka, a zuciyarsa yace bazaka fahimtaba yaro.
Batare da sake kallonsa ba yace, “yanzu mikake buk'ata kenan?”.
“yaa Sam kud'in wajenafa basuda yawa”.
“Humm” Galadima ya fad'a hankalinsa akan aikinsa. yace, “Aikai dama baku iya tausayin kud'iba kai da Samha, mutum yarasa uwar mi kuke saya? Kaje zan turo maka, Dan yanzu kama nima buk'atar kud'in nakeyi, gashi sunyi cak, nasan kuma daga inno har papi idan suna dashi baka zasuyi”.
“shikenan yaya, amma Dan ALLAH ko kad'anne”.
“ka duba cikin kayan dana cire, maybe ka samu”.
“yauwa Yaa Sam d'inmu. ALLAH ya k'ara girma”.
Galadima Dai baice komaiba, ya kwaso kud'in duka yana fad'in “na kwashe duka?”.
Kai kawai Galadima ya d'aga masa.
Sauban yazo ya rungume Galadima ta baya yana godiya, sannan ya sakesa. Murmushi Galadima yayi yana fad'in “ALLAH ya gyaraka Sauban”.
“Amin yayana”. Sauban ya fad'a cikin dariya.
Sunyi sallama ya tafi akan cewa shima saiya zo, yakuma gaida su papi.
*****************
Munaya taji dad'in ganin Sauban, sund'an ta6a hira sannan yamata sallama ya tafi tana shaida masa ya gaida mata su inno da k'yau, har k'ofar gida ta rakoshi, dukda dai bata fitoba iyakarta jikin gate, saida yashiga mota sannan ta koma ciki, tanamai jin k'aunar ahalin Galadima har cikin ranta.
************\/**********
Galadima na shirin fita kira ya shigo wayarsa, saida yagama d'aura belt d'in da yakeyi sannan ya matsa gaban gadon ya d'auki wayar, a dai-dai lokacin kiran ya kuma shigowa, ganin Sir Isa saiya d'aga.
Ko gaisuwa basuyiba yace, “yalla6ai kaga kuwa aika-aikar da ake neman mana?”.
“Aika-aika kuma? Tami?”.
“Tabbas ansaka wani yamaka kutse cikin Computer, Nazatama kagani?”.
Gaban Galadima ne ya fad'i babu shiri ya yanke wayar, system d'insa ya jawo ya zauna bakin gadon, “innalillahi...” Yashiga ambata zufa Na tsatstsafo masa saboda abinda yagani Na shirin faruwa, ya manta daya gama aiki bai saka security a matakin farkoba, saurin sakawa yayi, dukda yasan babu tabbacin zai iya dakatarwa ahakan kawai da yayi, ya ajiye lap-top d'in yana mik'ewa da hanzari, sauri d'aukar rigarsa yayi ya saka, yana saka bottoms d'in a tsananin hanzarce, haka dai ya k'arasa shirin a gaggauce, ya d'auki abinda zai d'auka yafito, babu gaisuwar Wanda ya amsa, hannu kawai ya d'aga musu yanufi mota yashige da kansa yaja ya fice daga masarautar, Wanda yatafi kiran Sarkin Mota duka iso tare, duk mamaki ya kamasu, yau Galadima da kansa yaja mota, anya kuwa lafiya?.
Ganin wannan bazai musuba sarkin mota ya shiga mota shima ya bishi.
Yana tuk'i suna waya da Vijay abokin aikinsa Na India, a haka ya iso gidansa dake bayan gari, kusan lokaci d'aya suka Isa da sarkin mota, ganin Galadima zai fita ya bud'e gate da kansa, shi saiya kashe motar dayake ciki da sauri ya fito yazo ya bud'e masa ya shige, bai bisaba, tunda Alhmdllh yaga dai inda yazo, maybe kuma baya buk'atar kowa a wajene shiyyasa ya buk'aci tahowa shi kad'ai.
Wani d'aki dake cikin bedroom d'in gidan ya bud'e ya Shiga, bazaka ta6a tunanin akwaima d'aki a wajenba, da y'ar k'ura a d'akin, amma hakan bai damu Galadima ba a yau, k'yallen da aka rufe kujeru da Computers d'in d'akin yashiga yayewa, da sauri ya fito zuwa can bayan d'akunan, yad'anyi ajiyar zuciya saboda ganin Gen... d'in gidan akwai fetur, dayake yad'an zazzo gidan kwannan, tadawa yay ya kuma komawa cikin gidan, ya kunna komai sannan ya zauna a kujera, medical eyeglasses ya saka, idonnan yayi jazur saboda 6acin rai, duk jijiyoyin kansa sun mimmk'e, hakama gashin jikinsa, kallon farko zai tabbatar maka ran maza ya 6aci. Koma a yanda yake sarrafa Computers d'in.
Abinda ke kunnensa kawai naga ya danna yanayin kwatancen d'akin da za'a sameshi.
Mintuna 3 tsakani saiga Sir Isa da Baffi sun shigo, saikuma ga Sauban Wanda harsun d'auki hanya Muftahu ya kirashi akan ya dawo, dole ya dawo masarauta, shine suka fito shida Muftahun.
Sir Isa da Sauban duk zama sukayi, Galadima Na Sanar musu abinda zasuyi.
“Gaskiya shegene guy d'innan yalla6ai, wlhy yasan Computer, kagafa yana Neman lalata mana dukkan security d'inmu.......”. ‘hankali tashe sir isa yake magana.
Sauban kam har kwalla ta cika masa ido.
Galadima baice komaiba, aikinsa yake iya iyawar k'arfin zuciya dana k'wanji.
Sai Baffine yad'an bubbuga kafad'ar Sauban yana fad'in “ka kwantar da hankalinka Sauban, insha ALLAH bazasuci nasaraba, kacigaba dayin komai a nutse kaidai”.
Sauban ya kad'a kansa yana share hawaye.
Galadima dayay zufa sharkaf ya kalli Sir Isa, yarigada yaci k'arfinmu kafin muzo, k'ofa ukuce kacal ya rage masa bud'ewa yasamu dukkan komai, abinda zamuyi mu bud'e masa sauran kawai, bayan yashiga ciki insha ALLAH inada wata dabara”.
Muftahu yace, “Amma Ranka ya dad'e hakan riskine gaskiya, idan kuma shi yanada plans akan hakan fa?”.
“Gaskiya ka fad'a Muftahu, amma hakan shine kawai hanya mai sauk'i da zamubi, inhar muka bari harya bud'e da kansa lallai zai lalata komaine, Dan wannan shine shirinsu”. Sir Isa ne mai maganar.
Galadima ya danna abin kunnensa yana fad'in “Vijay mubashi dama kawai, a lokacin daya shiga kaikuma ka tabbatar da ka zuk'e dukkan nasa shirin, ga wata akwatinan dayake yawo da ita a bayan handle d'in Computer d'insa, karka ta6ata Dan makircine ya shirya a cikinta, munayin kuskuren ta6awa labari zaisha Banban. Alex yay gaggawar had'amin sabbin Securitys muga kozasu ja hankalinsa can, ga hoton yaranan zan d'ora masa, dasu zaiyi amfani, dan dolene mu kauda masa hankali, yasan mi yakeyi sosai”.
“Ok! Ok! muje zuwa kawai” vijey ya amsa a hanzarce.
Da sauri Galadima ya maida kallonsa ga Sauban yana fad'in “dakaje duk ka d'auki su Amaturrahman ne?”.
“Eh yaya dukna d'aukesu”.
“A lokaci d'aya ko daban-daban?”.
Na d'aukesu lokaci d'aya, nakuma d'auki kowa shi kad'ai”.
“Alhmdllh taso nan”.
Tashi Sauban yayi ya matsa inda Galadima yake, wani glass Galadima ya tura masa, yace, “'Dora duka hannayenka anan mugani”.
'Dorawa Sauban yayi, bayan ya ta6a wani farin Abu da Baffi ya bashi, shatin hannun yaran suka bayyana, dayake yayi musu wasa sosai, amma kuma hakan bazai gamsarba.
Daga can Alex yace bazaiyiba, dole akawo yaran. Shima Galadima ya tabbatar bazaiyinba, sai hankalinsa ya kuma tashi, yaran sunyi k'ank'atar daza'a fito dasu daga gida.
Muftahu yace, “Ranka ya dad'e bara kawai naje Na kawosu inaga zaifi sauk'i”.
Baffi yace, “hakan shine kawai dai-dai sai dai bakai yakamata kajeba, a kira mahaifiyarsu tabama Wanda zai iya 6adda bamanni wajen kawosu, kuringa tunawa sumafa idonsu nakan kowane motsinmu a yanzu, shiyyasa tun a jiya naima Sameer hannunka mai sanda akan hakan”.
Galadima daya zubama Computers d'in ido kawai yana kallon 6arnar da ake shirin masa. Ya mik'e tsaye yana fad'in “Muftahu ka kira mai taxi d'innan yaje inda yata6a ajiyeta za'a kawo masa yaran”. fitowa yay daga d'akin yana k'ok'arin neman number Munaya ya kira.
Bugu biyu Munubiya da wayar ke hannunta ta d'aga, tana mannama Munaya wayar a kunne, bai amsa sallamarta ba yace, “Yanzunnan ki bama Innaro da laraba su Abdurraheem, sufito bakin layinku akwai mai taxi zai d'akkosu”.
Cike da mamaki Munaya tace, “yalla6ai ban ganeba?”.
A tsawace yace, “basai kinganeba, Dalla malama kibasu karki 6atamim lokaci”.
Sosai Munaya ta tsorata da tsawar tasa, kad'an yarage wayar ta su6uce mata ta daiyi azamar rik'ota, batada za6in daya wuce bin Umarninsa, dukda hankalinta bai kwantaba da hakan. Yanda yace ayi haka tayi, innaro da laraba Na fitowa suka samu mai taxi yana jiransu.
Cikin mintuna k'alilan suka iso, Muftahu da Sauban sukazo suka kar6i yaran, akabar su innaro a mota zasu jira.
Akan wani Abu akad'an d'orasu, da hotonsu ya fota a Computer d'in sai'a ciresu, sud'uka duk aka d'ad'd'orasu, sannan su Muftahu suka maidasu wajensu innaro aka koma dasu. Sudai duk mamaki ya cikasu akan miya faru? Basuda mai basu amsar wannan lamari.