← Book details Ni Da Prince Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 16 OF 38

Sashe 16

Ni Da Prince Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Salma ce tai kasa dakai tace fulani ayi hakuri abunda yafaru rannan munyi kuskure😞 tafad'a tare dayin kasa dakai, salman ya maka mata harara ta gefen ido amma a bayyane sai yace umma kinji hakuri take badawa bayan ninai laifin, fulanI aranta tace wato kana nufin kai kafi karfin bada hakuri kenan? Salman ya kalleta yasan metake tunani amma a fili yace umma bari mu wuce ina tunanin zamu d'an fita akwai inda zata rakani, yafad'a yana murmushi, sannan ya kalli salma yace muje dear😉 salma ta d'ago aranta tace dear😒? Mikewa tai salman yace umma yau nasanar dake ko? Fulani bakin ciki ne ke neman kasheta amma tad'aure kamar tai kuka ta saki yake tace eh mana, salman ya kalli salma yamata alama dakai muje, salma tafara tafiya jikinta yai sanyi, itakanta tasan bakaken maganganu salman ke fad'a amma ita ta d'auka bakar magana rai abace akeyinta?.

Suna Shiga d'aki takalleshi tace dagaske gun Abba zamu😬? Ya hade rai yace saki nai? Tace mene? Yace hakurin da kika bada mana🙄, saki nai? Tace hm ganinai kamar.....yakatseta karki sake banaso, tace amma ai....yace zaki fara ko? Ke ba'a isa ace kaza kice to bako? Salma ta turo baki tace to, salman ya matso yaja leben ta da karfi, ai kuwa ta fara shure_shure, ya saketa tasa kara tace da zafi fa😢tafad'a cikin shagwaba, salman yai dariya yace in ba zafi mezaisa inja? Tace ni wlh ban yarda ba☹ya juya baya yace shikenan in baki yarda ba sai mufasa zuwa gun Abban, dasauri ta dawo gabanshi tace a'a na yarda sosai ma😬 murmushi yai tare dasa hannu ya dungure mata kai yace sai ki fito.

Ya juya yai waje, tsayuwa tai a gun tare da daga gun da zuciyarta take, jitai tana harbawa tacw wayyo ni! Yaya ka....dasauri ta toshe bakinta tare da girgiza kai, fuskarta tad'an gyara ta yafa mayafi ta fito.

A mota tasami salman tashiga tare da murmushi salman ya hade rai yace da ai nafara tunanin fasa zuwa, dasauri takalleshi tace na'am😱? Yatada mota tare da cewa ina nufin da baki fito ba nan da 5min😏, salma tace ahhh ya fara tafiya, tace hmm yauwa kaga kud'in rannan a jakata sam namanta ban baka ba, tafad'a tana mikowa, hannu yasa ya dunkule hannunta da kud'in yace keep it, salma kam tai sororo jinyanda ya rike hannunta.

Shikanshi wani abune ke ratsashi da sauri ya saketa, sai dai salma tana rike da kud'in kuma bata d'auke hannunta ba, akasarima batasan yad'auke hannunsa ba, juyawa yai yakalleta a yanda ya barta, hanni yasa a kafadarta yace menene? Dasauri tai firgigit tadaure tace bakomai tunanin Abba nake.

Salman yace karki damu zai warke, kallanshi tai tad'an karkatar dakai aranta tace yaxanyi? In nikad'ai nafara sansa? Tasani sarai ita bata iya so ba.

A wani karamin mall ya tsaya ya fita, yana fita salma taji karar waya, wayarta ta duba taga ba ita bace ahankali ta kalli wayar salman, tace oh ankirashi gashi bayannan, tafad'a tare da kallan wayar, number ce, harta kai hannunta zata d'aga tai saurin girgiza kai tace ba ruwana😕.

Salman na dawowa tace mai ankiraka yace wa? Tace number, yace ok, yace bazaka kiraba? Ya kalleta yace 4get, ta tabe baki tace nima haka zai dingamin in na kira baya kusa? Batasan afili tafad'a ba jitai yace in kin kira sau d'aya bazan kiraki ba amma in sau uku kika kira bana kusa I promise to call u back.

Haushi ya kamata wato sai ma tayi sau uku?tace au in sau d'aya nakira bazaka kira ba? Yace yes saboda inkika kira sau d'aya ai abun ba important bane kenan, salma tadafa kanta aranta tace na shiga uku ni salma🤔.

Asibiti suka sauka ahankali suka karasa d'akin Abba, kamal na ganinta yashiga washe baki, sai dai yau salma murmushi kawai tamai tad'auke idanunta, sun gaisa da Abba, nan Abba yasakema salman godiya yace kaganmu ashirye sallama za'a bamu yanzu, salman yace Abba baka gama warkewa ba wacce sallama? Abba yace kayya ai nikam yau gida zani, goggo tace ai fa yadage sai hakuri, salman yace shikenan bari in anso sallamar sai in kaiku gida.

Sunzo shiga mota salman ya kalli kamal yace kai sai ka biyomin ko a mashin ne dan gun bazai ishemu ba ko? Kamal ya harareshi yace sai ka fad'a😠nan suka shiga mota sukai gida.

Tunda suka iso unguwar salman ke kallan unguwar tausayi duk ya kamashi, yanzu anan salma take? Amma ya hanata karatu a skul? Dasuka iso gidan jikinsa duk yai sanyi ya daure ya ajiyesu ya kalli salma yace ana la'asar zanzo tai murmushi tace to zan kula da wayata😊 yanda inka taho sai ka kirani yace to, harta juya ta dawo tace sai na ganka😊 yace hmm sai kin ganni😊 wani murmushi sukama juna yad'ago zaiyi magana aka sake kiranshi, tace bye tare dayin ciki shikuma yabita da kallo tare da d'aga wayar yasa a kunne.

Jiyai ance yayana is me? Cikin kid'ima da rudewa yace what? Aka kara cewa haba yayana ai sai in fishi in kace baka ganeni ba, Ur Farha ce, salman yace what? Farha? Tai murmushi tace naji kunya yayana dabaka d'au muryata ba☹anyway gani a airport kainake jira😊 tana gama fad'ar haka ta katse layin.

By Ayusher Mohd📚
[11/13, 10:23] 💞Maman Binafah💞: ☄☄☄☄☄☄☄
💥 *NI DA PRINCE*💥
☄☄☄☄☄☄☄

*NA AYUSHER MOHD*

NO.2⃣9⃣

Salman ciki kid'ima yai hanyar airport gudu kawai yakeyi, yana isa ya shiga kiran farha a gigice sai dayai kira 2 ana ukun tad'aga tace yayana har nayi fishi, salman yace farha? Dariya tai tace yayana kana ina? Nan ya mata kwatance.

Sanye take da riga da wando na 'yan kanti, sai dai rigar takai gwiwa, tayane kanta da bakin mayafi karami, jakar dake jikinta irin doguwarnan ce itama black sai takalmi flat akafarta black,tana jan trolley d'Inta.

Karasowa tai inda salman yamata kwatance, daga d'an nesa ta hangoshi tasaki murmushi tare da karasowa, sai datazo daf dashi ta ajiye trolley d'in tayi d'age tasa hannu ta rufemai ido, salman yai ajiyar zuciya tare da zare hannun ya juyo a sukwane, tofa kallon juna suka shiga yi, farha ta rufe idanta tace yaya wannan kallon fa? Salman yai gyaran murya yace farha? Kece? Dama zan ganki? Ta turo baki tace ba wani nan bayan kamanta dani?☹ tai maganar cikin shagwaba, salman yace wasa kike kema kinsan I can't, tace nasani yayana kaima kasani ai ko? Tafad'a tana kallansa, yai murmushi yace ina nasani ko mazan paris sun mantar dake ni🤔.

Tace su sun isa? Yace waya sani, atare sukai dariya yace muje mota ko? Ta kalli akwatinta sannan ta kalleshi, yace hmm badai ni akeson ind'au jakar ba? Tace yayana nifa mace ce☹kallanta yai ya wucewarsa mota, takalleshi tare da jan jakarta tace har yanzu dai halin nanan.

A baya tasa jakar sannan ta bude gaba ta shiga, farha ta kalleshi tace yayana how many years?yace hmm 4 ko? Tace ahh gaskiya mun dade ko? Yai murmushi yace sosai ma, hannu tasa takamo nashi tace yaya kasan meyasa nazo? Ya kalleta yace a'a, tace yaya jinai inban gankaba akwanakin nan kila mutuwa zanyi😪 salman yace haba farha meyasa kike fad'an haka? Tace yaya bakasan yanda nakeji ba, gashi narasa dalili dana ma mum maganar zuwa hanani tai, yace y? Yace cemin tai wai ko kayi aure😄ta d'auka zan yanda in hakura da zuwa, salman ya kalleta yace gaskiya tafad'a farha, cikin tsananin mamaki tace what?me kake nufi da hakan? Bai bata amsa ba yaja motar yace gida ko? Tace eh amma....ganin ya d'auke kai yasa kawai tasa kuka, daurewa kawai yake dan sam bayasan kuka, ganin yanda take shesheka yasa kawai yai parking ya kalleta yace farha?dasauri ta matso ta rungumeshi, janyeta yad'anyi sannan ya miko mata tissue yace bansan kukan nan kinsani sarai, bari in fita inkin gama sai inshigo, yafad'a tare da mikewa zai fita, dasauri tajawo hannunsa tace nadaina, karka fita plz.

Yakalleta sannan ya shafa gefen fuskarta yace yauwa farha, kallanta tai tace yaya amma......yace farha please karkibatan rai bayan inajin farincikin ganinki, tace cewa fa zan kasai min icecream😰murmushi yai yasan waskewa tai amma sai yace bari muje a siya.

Haka farha taita sashi yawo daga tace ka za sai tace ka za har suka kai 5 sannan sukai gida.

Farha kanwar matar sarkice wato mahaifin salman, lokacin salman na 10yrs Abbansa yakaishi paris gun kanwarsa bayan mahaifiyar salman din ta rasu, anan suka kulla wata muguwar soyayya da shakuwa tsakaninsa da farha, sai dai Abba yabada umarnin gaggawa akan salman ya dawo gida, wannan dalilin yasa salman ya rabu da farha kuma bai karasa karatunshi daya fara acan ba.

Salma kam na zaune sai kallan waya take amma sam bataga salman ya kira ba, kamal dake zaune yana mata magana sam batasan me yake cewa ba kawai dai tanacewa eh, ganin hankalinta ba'a kansa yake ba yasa yafit, Abbane ya kwalla mata kira dasauri ta mike ta karasa gunshi.

Abba yakalleta yace salma dare yafarayi kinga ankusa kiran magriba, ki kira salman kiji, tace to Abba.

D'akinta tashiga tare da kiran wayarsa, sai dai har kira uku tai bai d'aga ba kuma bai kira ba, zama tai taredayin shiru tace ina ya shiga?

Salman kam shiya raka farha gun fulani, nan akasa aka gyara mata d'akin dazata zauna, tajashi tace yarakata d'akin nan suka shiga taitamai zance sam yamanta da d'auko salma ga wayarsa na kan madubin farha,a silent take, sarai ta kula da wayar na haske amma ita batasan salman ya tafi, hakan yasa ta juya wayar.

Sai da salman ya mike zashi masallacin jin kiran sallar magrib yad'au wayarsa missed call din daya gani na salma ne yasa ya kalli farha yace farha am sry bari inje indawo, takalleshi da shagwaba tace yayana yaushe rabon mu hadu? Ina laifin kai sallah a nan? Ya kalleta kamar baisan metake nufi ba yace zanje mosque daganan zanje wani guri, ta mike tace yaya ina kuma? Nifa yau so nak........ga mamakinta bata karasa maganarta ba taga ya fita.
Chapter 16 · 0% Book details