← Book details Ni Da Prince Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 13 OF 38

Sashe 13

Ni Da Prince Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Juyawa tai, idanunta suka had'u dana kamal, ta karaso inda yake tace yaya, kamal ya juya cikin b'acin rai da sauri tasha gabanshi tace yaya meya faru? Kamal yasa hannu yaja hannunta ya fara tafiya tace yaya😳? ina zaka kaini? Kamal kam tafiya yake sai da sukai tafiya mai nisa, mutane nata kallansu, har sukaje gunda ba mutane sannan ya saketa.

Tace yaya me kakeyi hakan? Kamal yace tambaya ta ma kike? Salma dama akwai ranar dazaki zauna da wani namijin cikin farin ciki bayan ni? Ta kalleshi da mamaki tace yaya ya kakeso inyi da rayuwata😰? cikin d'aga murya da fad'a yace salma tambaya ta kike? Duk son da kika nunamin dama na karyane? Ni zaki yaudara? Nad'auka yanda nake sanki haka kema kike sona ashe ba haka bane? Me zaki cemin? Itama cikin fad'a da kuka tace yaya ya kakeso inyi? So kake in kashe kaina? Duk jiran danamaka ka manta dani, kabarni da tsananin begenka, ba nema? Kamal ya dafa kafad'arta hawaye ya zubo mai yace salma ban barku ason raina ba y don't u understand? Ta ture hannunshi tace fahimtar dani yanzu😠, kamal yai shiru tace bazaka iyaba? Dama nasan bakada abinda zakace, ta juya tafara tafiya.

Hawaye take harta isa d'akin, goggo ta kalleta tace daga rakiya shine kila dade? Batai maganaba ta zauna kusa da Abba ta kama hannunsa ta rike tana hawaye.

Salman kam dama inya shiga class wayarsa yake d'auka yai ta d'annawa ba ruwanshi da abinda akeyi, yau kam yayi shiru tunanin salma kawai yakeyi, ko mahafin nata ya farka daga allurar baccin da akamai? Ko jikin ya kara tashi? In ya tashi ya salma zatai? Wannan dalilin yasa yai shiru, har malamin ya fita baimasan me akeyi ba.

Najib ne yatab'ashi yace Prince ya akai? Amir yace hala tunanin Amarya ake, salman ya mike yace tunanin Amarya? Allah ya sauwaka, ya fita waje najib ya bishi yace ina zaka? Salman yace hm wani guri, sai gobe.

Dasauri ya fad'a mota yai hanyar asibiti.

Salma na rike da hannun Abba taji yayi motsi, dasauri ta d'ago tace Abba😥? Yakalleta tare da lumshe ido tasa kuka tace Abba laganka kuwa? Murmushi ya kakkaro ta kalli umma tace umma me za'a bashi? Ta mike ta zubo mata faten tsaki wanda yasha manshanu da yakuwa, salma ta amsa tare da taimakawa Abba ya mike, nan ta shiga bashi,ahankali ya dinga amsa har ya shanye.

Salman gudu yakeyi ya kai wajen titin gyad'I_ gyad'I mota tamai faci, haushi duk ya isheshi ga yamma tafarayi, waya yama driver dinsa yace ka kawomin prince 4 yanzu, yace to ganinan ranka ya dade.

Salman nazaune a mota haushi duk ya isheshi ga salma bata da waya, sai wajen 5 ya iso.

Dasauri ya amshi motar tare da barin driver din anan gun d'ayar motar.

Salma ganin Abba ya koma bacci, ga goggo ta tafi gida, umma ce a ciki yasa ta fito waje ta zauna a dakalin gun, kamal ne yazo yazauna kusa da ita, ta d'ago ranta a had'e ganin kamal yasa ta mike, dasauri yasa hannu ya kamota yamaida ita inda take, tace yaya.

Kamal yace salman jarabawa na fad'I sai dana zauna wata semester din tazagayo na sakeyI😞 kiyi hakuri dana barki ke kad'ai.

Kallansa take tana hawaye tace yaya meyasa baka fad'aba ko ta waya? Yace banso kisan saurayinki rago ne gun karatu, ta runtse ido kwalla sai zubo mata take, yace muje ki rakani na siyoma umma lemo, nima inasan kati.

Ta mike suka jero suna tafiya, salman da tun da ya iso yana kallan sanda kamal ya rikota duk yagansu duk da baisan me suka ce ba amma ranshi yagama dugunzuma.

Ganin sun taho tare yasa ya kunna mota, cikin tsananin bakin ciki da bacin rai ya kunno motar da karfi, da gudu ya taho, saura kiris ya kadesu, dan sukam sun gama tsorata kamal ya kamo hannun salma yasata a bayansa da sauri, salman sai dayazo daf da kamal ya taka burki jikake kiiiiiiiiiiiiii...

Kallan kallo suka fara, sai a lokacin kamal yaga ashe salman ne, salman kam hannun kamal daya rike salma ya kalla, daure wa yaI tare da fitowa daga motar, ya saki murmushi kamar ba komai ya matso kusa da kamal ya zare hannun salma sai alokacin tasan salman nema, ta kalleshi cikin tsoro, saidai ga mamakinta murmushi ya saki tare da kallan kamal yace ayya kamar baka gani? Ka dinga kula in kana tafiya karkaja a ragema farashi😉.

Kamal kam mamaki ya hanashi magana, salman ya kalli salma yasa hannu yajawota yace kema kamar bakya gani? Tace hm hm bankula bane🙁 yaceina zaki? Without my permission? Ta kalleshi sannan ta kalli kamal tace dama....ya katseta yace muje muduba Abba mu wuce gidanmu, yafad'a tare da kallan kamal.

Salman yafara tafiya itama ta bishi a baya, kamal kam ya kame yama kasa tafiya yana kallo har suka shiga ciki haushi ya isheshi yakaima motar naushi da kafa, sai dai maimakon yaji sauki sai zafin dayaji akafarsa😕

Hmm to fa🤔

By Ayusher Mohd📚
[11/13, 10:23] 💞Maman Binafah💞: ☄☄☄☄☄☄☄
💥 *NI DA PRINCE*💥
☄☄☄☄☄☄☄

*NA AYUSHER MOHD*

NO.2⃣4⃣

Sun isa d'akin, Abba na jingine sai dai ya rame sosai, salman ya karasa tare da gaidashi, ahankali Abba ya amsa tare dama salman godiya.

Salman ya kalli umma ya gaida ita, tai kasa dakai ta amsa, sun d'an yi shiru kafin Abba yace kuje gida dare yayi, salman ya kalli salma sannan ya musu sallama, itama salma ta musu sallama ta fita.

A waje ya tsaya, yanakallan kamal ma tahowa gunsu yai murmushi tare da kallan salma yace muje ko? Ta kalleshi tace eh, ahankali ta matso suka jera suna tafiya, sai da sukazo daf da kamal sannan salma ta kalli kamal idanta taf da kwalla, salman ya kalleta ganin yanda take kallan kamal yasa ransa ya b'aci amma iya basarwa ta salman sai ya kalli kamal yace mr d'an rakiya dan zo ka shiga da ledojin nan tunda ciki zaka😉, kamal ya kalleshi sannan yace kai meyasa dazaka shiga baka wuce dashi ba? Salman yace karaso ka amsa, yafad'a tare da karasawa motar.

Kamal ya kalli salma ranshi duk a b'ace tace yahkuri yaya ba....wani kallo da kamal ya mata yasa tai shiru, kamal ya tsaya kikam salma tafara tafiya ta juya tace yaya? Kamal ya d'aure ya karaso, salman yai murmushi tare da mikomai manyan ledoji guda biyu yace tnx d'an rakiya😊, kamal yace karka kara kirana da sunan nan😠.

Salman ya shiga mota tare da rufowa sannan salma ta shiga, ya zuge glass d'in mota ya kalli kamal yace ban san sunanka ba me kake so ince? Salma zatai magana ya juyo ya kalleta tai shiru tare da turo baki, ya kalli kamal yace nyt😏, yaja mota da gudu ya bud'ama kamal kura.

Kamal ya kalli motar yace wlh mutumincen sai na👊🏻.

Salma kam a mota suna hawa titi salma ta kalleshi tace plz ka dainacemai haka☹. Cikin zafin rai salman yai gefe ya taka burki da karfi, salma kam ta tsorata da sauri ta jiyo ta kalleshi, sai dai yanda taga idansa yasata tai shiru, ya kalleta tare da nunata da yatsa yace karki kuskura!
*karki kuskura ki kara tarema wani a gaba* don't u dare do that again😡.

Salma kam jikinta rawa yake amma ta daure tace menai kuma? Ni meyasa kakemin haka? Tafad'a tare da zubo da hawaye, sai dai ganin tana hawaye yasa jikinsa yai sanyi ya juya tare da fara tafiya batare dayace komai ba.

Salma ta juya kai tana kallan window, wajen mai saida waya ya tsaya baice mata komai ba yafita, takalleshi tare dacewa kada Allah yasa kacemin kana zuwa😗.

Yad'an dade kad'an kafin ya fito, ya bude mota ya shiga, baice komai ba itama haka, har suka isa gida sun fito zasu nufi bangarensu wanI bafade yazo gun salman yace Ranka ya dade mai martaba na kiranka, ya kalli salma tare da mikamata karamar ledar yace wuce dashi ina zuwa tace to.

Amsa tai ta wuce shima yai banaren mai martaba, salma na shiga bangarenta hanne ta taho da sauri tace ranki ya dade kun iso lafiya? Salma tace lafiya, hanne tace ina kukaje ranki ya dade🤕? Bakiga fad'an da fulani tai ba mai martaba ma sai da yai fad'a.

Salma tace bangane ba😳? Hanne tace a ka'idar gidan ba'a fita sai mace tayi wata biyu amma ke kun fita ku biyu ba driver kuma ba wanda yasani😞.

Salma tace bansani ba ai dana sanar😰, yanzu mai zai faru? Hanne tace kawai dai fad'a za'amai tunda ansan ke bakisani ba.

Salma ta mike tai d'aki tare da zama dabas a kasa ta jingina kanta a gado, tasan salman bazai yi bayani ba saboda pride dinsa yanzu tasan anacan anamai fad'a.

A hankali hawaye ya fara zubo mata tace because of me😪 kanta ta had'a da gwiwa, tayi wajen minti 30 a haka sannan salman ya turo kofa kallanta kawai yatsaya yanayi, meyasata kuka? Jin sheshekarta yasa ya kasa jurewa kofar ya rufe tare da karasowa inda take, ya tsugunna yasa hannu ya jawota jikinsa, ahankali tad'ago tace me akacema😰? Ran sarki ya b'aci ko? Sai a lokacin yasan dalilin kuka, hannu yasa ya fara shafo bayanta, ta kankameshi tace am sorry because of me...katseta yai yace ba saboda ke bane, meyasa kike da saurin kuka ne? Salma kam tai luf a jikin salman sai d'an shesheka datakeyi.

Salman shiru yai yana tunanin fad'an da sarki yamai, shifa shiyasa bayasan zaman gidan nan, ace komai sai ka sanar?.

Sun dade a haka kafin hankali salma ta zare jikinta, ta mike salman yasa hannu ya jawota ta zauna a inda take yace wa........sai kuma yai shiru, azahiri so yake ya tambayeta meye tsakaninta da kamal? Amma jiyai bazai iya ba, kamar zata rainashi tai tunanin ya damu da itane, kallansa tai tace wa me? Hannunta yasaka tare da kikewa yai gyaran murya yace hm waya nake nufi wace kika shigo da ita, kiyi amfani dashi in kinaso, yana gama fad'ar haka yai toilet.
Chapter 13 · 0% Book details