Sashe 5
Mummunan Zato Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kice zaki dinga haɗa min in kin koma gidana can Katsina? Ko ba za ki je Katsina ba?" Cikin cinyoyinta ta tura kanta,ya ce "Gaya min in ba ki son zuwa don bana son ki takura." Ta ɗago kanta ta ɗan dube shi "in dai zan dinga zuwa makaranta ai ba komai," ya ce "da gaske ki ke yi?" Ta ɗaga kai ya ce, "To za ki yi karatunki in ma makarantar da ki ke,ki ke so zan bar ki kiyi abinki,yanzun yaushe zaki koma?" Ta ce"jibi" ya ce "to shikenan,in na kai jibi a garin nan sai na kai ki." Ta ce,"To" bai san me zaice mata ba ma,yana jin nauyin yi mata magana, hannu yasa cikin aljihun rigarshi ya ciro bandir ɗin ƴan Naira ɗari biyu "Gashi kiyi shopping" ta ce,"A'a,ka barshi na gama shopping ai" ya yi yayi taƙi amsa,ta nufi cikin gida. Abbanta ya ce har kun gaisa?" Ta ce "Eh," ta shige ɗaki bakin gadonta ta zauna. Mutumin yana burge ta, ya iya gayu mai ƙyau da shi, tunda ya ce zatayi karatu ba ta damu ba, sai dai zata yi kewar Ummanta da Abba.
Washegari tafiyarshi ta kama,don haka ba zai samu kaita makaranta ba, Abba ya ce kada ka damu,dama da akwai motar da ke kai su, kuma ita ce ke ɗauko su. Ya ciro ƙwalin waya ƴar mai ƙyau ƙirar (Nokia), "Gashi ka ba ƴar gidan tawa in dai babu damuwa, saboda kasan ba zan dinga samun zuwa ba, duk da na san ba za ta da ita makaranta ba,in ta dawo ma ringa gaisawa,don na bata kuɗin ne taƙi amsa shiyasa na siyo mata da na fita ɗazun," Abba ya ce "ita da zata koma makaranta ka sai mata waya?" Alhaji Saddiƙ ya ce ka dai bata ƙila ma zata fi amsa min magana a cikin wayar," "shikenan" inji Abba, Allah ya biya maka da gidan aljanna,bari na turo ta kuyi sallama," "a'a ka barta tana jin nauyina yarinyar tana da kunya bana son matsa mata," "shikenan". Suka sake yin musabaha, sannan ya shiga mota sai Kano,ya bar motar a gidanshi na nan Kanon, sai ya hau jirgi.
Labarin da Alhaji Saddiƙ ya zo ma su Hajiyarmu da shi sun ji daɗi, amma suna fargaba sai dai Alhajinsu ya kawo shawarar a miƙe da roƙon Allah,tun kafin bikin,ya ce zai samu malamai kuma zai sanar Masallatai a saka su a cikin addu'a.
Nafisa auta itama cewa tayi Yaya Saddiƙ nima insha Allah zan soma tsayuwar dare tun daga yau. Ya dube ta "kin yi alƙawari fa?" Ta ce "insha Allah,Yaya zan cika" shima dama Allah ya ke gayamawa kullum sai dai ya sha alwashin dagewa.
Ya dubi Hajiyarmu wadda har yanzun ba ta ce komai ba, sannan bai karanci wani abu game da zancan a fuskarta ba,ka ra Hajiyarmu ta yi don haka bata furta komai ba. Amma zancan ya yi mata daÉ—i, duk da tana fargaban abin, ganin kallon da yake mata yasa ta ce "Allah yasa ma abin albarka."
Yayi ajiyar zuciya tare da miƙewa,can ƙasan zuciyarshi kuwa cewa ya yi "Amin Hajiyarmu".
Nafisa kuwa, dariya ta yi.
Sau da yawa tana mamakin yanda Hajiyarmu da Yaya SaddiÆ™ suke jin nauyin juna,tamkar surukai. Yace "to ni zan tafi,ban riga na sanar da Jummai ba tukun, sai na koma yanzun."
Nafisa ta ce, "Yaya don Allah kada ka gaya mata".
Kafin ya yi magana, Hajiya ta ce "Don me? Ke Nafisa kin cika fitina," shiko ƴar dariya ya fita yana yi, Nafisa ta bishi tana cewa "Yaya bani lambar A'isha,zan kira ta," ya ce "ayya Nafisa, A'isha yarinya ce ƙarama, gobe ma zata koma makaranta (S.S 1) take a Munjibir, kuma ba wai shekarunta ne suka kaita (SS) ɗin ba, ƙoƙari ne,she is fifteen."
Dariya ta yi.
"Yaya kana son ƙananan yara."
Ya ce,"to Nafisa Æ´ar abokina ce, shi ya bani duk da yasan matsalar gidana,ki bari in lokacin ziyarar É—aliban makarantar ta zo in kina gari sai muje ko?"
Ta ce, "to Yaya," Ta koma ciki,shi kam ya shige mota. Ya lura kowa yana son Aisha a dangin nashi, yanzun saura Jummai.
*** **** **** ****
Umma ta ce, "Ga wayarki can jikin chaji in ji Uncle ɗin naki, har ma da layi ya saka miki." Ta kalli wayar, "kai tana da ƙyau wayar, sai dai na san Abba ba zai bari na riƙe waya ba, kuma makaranta ma ba zasu bari ba ai".
Umma ta ce,"to ai Abban naki ne ya kawo" ta ɗauki wayar tana jujjuyawa,ga ta ƴar mai ƙyau,na gode. Umma ta yi dariya.
"A'isha kenan,dama ga ki da son yin (Game)."
Tayi dariya,ta zauna tana cewa, "Bari na gani zan gane kan wayar kuwa?" Ba tako gane ba, sai da Yaya Abdurrahman ya shigo, sannan ya koya mata.
Bayan sallar Isha'i,sun ɗan taɓa hira ta ce "bari na ƙwanta Umma,don gobe tashin wuri zan yi saboda komawa makaranta."
Jafar ya ce, "Yaya A'isha ko dai kina son ki buga (Game) ne da wayar?"
Ta ce,"Jafar ka raina ni ko?" Ta shige ɗakinta, gado ta haye tana buga (Game) ɗin (Bounce) kusan goma na dare wayar ta shiga ringing,ta saba da wayar Umma don haka ba taji komai ba,ta ɗauka. Da ƴar zazzaƙar muryarta ta ce,"Salamu alaikum" ya amsa da "wa'alaikis-salam, A'isha ce?" Gabanta ya faɗi saboda ta gano Uncle ne,ta amsa "Eh." Ya gyara ƙwanciya, "kin san mai magana?" Ta ce "Eh," ya ce to wanene?" Ta yi shiru ta rasa me zata ce,kina jina? Ta ce Umh,ya ce kiyi magana mana A'isha...
#######
[11/30, 21:03] Ummi Tandama😇: ____________________________
*📗MUMMUNAN ZATO📗*
*NA*
*HALIMA ABDULLAHI K/MASHI*
*ÆŠandano page 5*
Ya ce kiyi magana mana A'isha,wa ke magana da ke? Ta daure ta ce, Uncle ne. Yayi murmushi, "zan zama mijinki kuma kina ce min Uncle? Gara kin kira sunana" ta ce "bazan iya kiran sunanka ba". "To ki samin wani sunan mana ban da Uncle". Ta yi shiru, ya ce "to ba mu gaisa ba" ta yi maza ta ce "Ina yini?" Ya ce "lafiya lau Nana A'isha Saddiƙa,ya ya su Abbanki da Ummanki?" Ta ce"suna lafiya." Ya ce "za ki jini ina kiranki da sunaye duk na ki ne", ta yi shiru, shima ya kan rasa me zai ce mata,can ya ce, to bani labari" ta ce "Na me?" Ya ce, "Na komai mana" ta yi shiru,ya ce "To bani na ƙawayenki na makaranta."
Tamkar ya mata susa,ta ce "ƙawayena biyu ne,da Suwaiba Shehu Ringim,sai kuma Zainab Shitu Katsina, duk suna da kirki."
"Ashe har da ƴar garinmu? Ki ce shi kenan in kin zo Katsina kina da ƙawa, sai kuyi ta wasanku ko?".
Kalmar ta bata dariya, har ma ta ɗan dara kaɗan, sannan ta ce "wasa kuma?" Ya ce, "Eh mana,ko baƙwa wasa a makaranta?" Ta ce "sai ka ce ƙananan yara?" Ya ce "Au,na manta ashe fa ku manya ne,ni da har ina son in saya miki kayan wasa su Tedi, haka su Cartoons." Ta ce "Haba dai?" Ya ce, "To shi kenan bari in bari sai kin haifa mana Beby sai in saya mata ko?"
Zancan ya yi mata nauyi, har ma ta kasa magana,ya ce "A'isha" ta ce "Umh" "kin ji me nace?" Ta ce "Um," "to kin yi shiru" ta ce "Uncle Ina jin bacci," ya ce"shikenan yi baccinki, sannan ki yi mafarki mai ƙyau na ƙyawawan yara masu kama dani" ya kashe wayar.
Shiru ta yi tana mamakin zancan da Uncle ya yi mata,ta yi addu'a ta shafa ta runtse idanu, har bacci ya yi gaba da ita.
Hajiya Jummai wadda ta jima tsaye kanshi tana sauraron surutun da yake yi, sai jikinta ya hau rawa,ta san tabbas da budurwa yake magana, kenan Alhaji aure yake nema? Cabdi! Daga gani kuma ko ma wacece yana sonta,dubi yanda yake wani kashe murya tamkar shima ɗan matashin saurayi ne? Lallai yana neman tada zaune tsaye ne, amma don ta san in har ta nuna ɓacin ranta yanzun ba zata san komai game da yariyar ba,don haka sai ta sako makirci da kisisina.
"Alhajina kai kuma da wa kake samartaka a waya?"
Cike da walwala ya dube ta,sanye take da rigar bacci mai santsi, ɗan gashin kanta da ya rage ta tufke shi da ƙyar ma yake tufkuwa saɓanin da da take da gashin da yawa, tsabar ƙalƙalin da take ma gashin duk ya karye.
Ya miƙa mata hannuwanshi alamun ta zo, sai ta basar ta zauna gefenshi, ta kuma cewa da shi.
"Kai da wa kake waya?"
Ya ce, "ƙanwarki to be insha Allah." Ta danne wani abu da ke son taso mata.
"A ina ka samo ta? Nifa ina jin tsoron ka ƙara aure yanzu in ina tuna baya."
Ya ce"to ni kaina a tsorace nake,Æ´ar abokina ce na Jigawan nan,wato Mustapha Gumel."
Ta miƙe da sauri tare da faɗin "Dama na san za'ayi haka,wato yaga kuɗi za'a ɗora shi manajan kamfani ba dole ba, kai ma in baka so cutarshi ba ai sai ka gaya mishi cewa gidanka duk wadda ka auro mutuwa suke yi."
Ya dube ta, "To menene na tada jijiyar wuya? Har kina gaya min cewa In ba na so cuta ba, wato ni ne macucin ko?"
Shiru ta yi ranta yana tafasa.
Ta miƙe tsaye "wallahi wannan karon ba zan yarda ba,ban amince da auranka ba, shiyasa ka ke waya har kana wani cewa zata haifa maka yara? Sai dai ka zaɓa ko ni ko ita, haka kawai kana auro matan suna mutuwa,ƙila ma ana can ana zagina ana cewa nice ke kashe su to ba zan iya ba."
Ya dube ta,"zan auro ta, itama ta zo ta mutu,batun yarda kuma bana neman yardarki tunda bake bace Hajiya Sa'adatu uwata ba,kin ji ko? Batun kamfani kuwa da kike magana naga ba naki bane,bana kuma son shiga sharo ba shanu,in ma kyauta na bashi ba ruwanki sannan ki sani rashin mutuncinki da ki ka iya kada ki yarda ya zo kaina."
Fuu! Ta fice ta bar mishi ɗakin, kallo ya bita da shi, cikin mamakin ɗaga hankalin ta da tayi. Sam bai za ci haka daga gareta ba, saboda duk auren da ya yi a baya bata taɓa nuna damuwarta ba sai wannan.
Washegari tafiyarshi ta kama,don haka ba zai samu kaita makaranta ba, Abba ya ce kada ka damu,dama da akwai motar da ke kai su, kuma ita ce ke ɗauko su. Ya ciro ƙwalin waya ƴar mai ƙyau ƙirar (Nokia), "Gashi ka ba ƴar gidan tawa in dai babu damuwa, saboda kasan ba zan dinga samun zuwa ba, duk da na san ba za ta da ita makaranta ba,in ta dawo ma ringa gaisawa,don na bata kuɗin ne taƙi amsa shiyasa na siyo mata da na fita ɗazun," Abba ya ce "ita da zata koma makaranta ka sai mata waya?" Alhaji Saddiƙ ya ce ka dai bata ƙila ma zata fi amsa min magana a cikin wayar," "shikenan" inji Abba, Allah ya biya maka da gidan aljanna,bari na turo ta kuyi sallama," "a'a ka barta tana jin nauyina yarinyar tana da kunya bana son matsa mata," "shikenan". Suka sake yin musabaha, sannan ya shiga mota sai Kano,ya bar motar a gidanshi na nan Kanon, sai ya hau jirgi.
Labarin da Alhaji Saddiƙ ya zo ma su Hajiyarmu da shi sun ji daɗi, amma suna fargaba sai dai Alhajinsu ya kawo shawarar a miƙe da roƙon Allah,tun kafin bikin,ya ce zai samu malamai kuma zai sanar Masallatai a saka su a cikin addu'a.
Nafisa auta itama cewa tayi Yaya Saddiƙ nima insha Allah zan soma tsayuwar dare tun daga yau. Ya dube ta "kin yi alƙawari fa?" Ta ce "insha Allah,Yaya zan cika" shima dama Allah ya ke gayamawa kullum sai dai ya sha alwashin dagewa.
Ya dubi Hajiyarmu wadda har yanzun ba ta ce komai ba, sannan bai karanci wani abu game da zancan a fuskarta ba,ka ra Hajiyarmu ta yi don haka bata furta komai ba. Amma zancan ya yi mata daÉ—i, duk da tana fargaban abin, ganin kallon da yake mata yasa ta ce "Allah yasa ma abin albarka."
Yayi ajiyar zuciya tare da miƙewa,can ƙasan zuciyarshi kuwa cewa ya yi "Amin Hajiyarmu".
Nafisa kuwa, dariya ta yi.
Sau da yawa tana mamakin yanda Hajiyarmu da Yaya SaddiÆ™ suke jin nauyin juna,tamkar surukai. Yace "to ni zan tafi,ban riga na sanar da Jummai ba tukun, sai na koma yanzun."
Nafisa ta ce, "Yaya don Allah kada ka gaya mata".
Kafin ya yi magana, Hajiya ta ce "Don me? Ke Nafisa kin cika fitina," shiko ƴar dariya ya fita yana yi, Nafisa ta bishi tana cewa "Yaya bani lambar A'isha,zan kira ta," ya ce "ayya Nafisa, A'isha yarinya ce ƙarama, gobe ma zata koma makaranta (S.S 1) take a Munjibir, kuma ba wai shekarunta ne suka kaita (SS) ɗin ba, ƙoƙari ne,she is fifteen."
Dariya ta yi.
"Yaya kana son ƙananan yara."
Ya ce,"to Nafisa Æ´ar abokina ce, shi ya bani duk da yasan matsalar gidana,ki bari in lokacin ziyarar É—aliban makarantar ta zo in kina gari sai muje ko?"
Ta ce, "to Yaya," Ta koma ciki,shi kam ya shige mota. Ya lura kowa yana son Aisha a dangin nashi, yanzun saura Jummai.
*** **** **** ****
Umma ta ce, "Ga wayarki can jikin chaji in ji Uncle ɗin naki, har ma da layi ya saka miki." Ta kalli wayar, "kai tana da ƙyau wayar, sai dai na san Abba ba zai bari na riƙe waya ba, kuma makaranta ma ba zasu bari ba ai".
Umma ta ce,"to ai Abban naki ne ya kawo" ta ɗauki wayar tana jujjuyawa,ga ta ƴar mai ƙyau,na gode. Umma ta yi dariya.
"A'isha kenan,dama ga ki da son yin (Game)."
Tayi dariya,ta zauna tana cewa, "Bari na gani zan gane kan wayar kuwa?" Ba tako gane ba, sai da Yaya Abdurrahman ya shigo, sannan ya koya mata.
Bayan sallar Isha'i,sun ɗan taɓa hira ta ce "bari na ƙwanta Umma,don gobe tashin wuri zan yi saboda komawa makaranta."
Jafar ya ce, "Yaya A'isha ko dai kina son ki buga (Game) ne da wayar?"
Ta ce,"Jafar ka raina ni ko?" Ta shige ɗakinta, gado ta haye tana buga (Game) ɗin (Bounce) kusan goma na dare wayar ta shiga ringing,ta saba da wayar Umma don haka ba taji komai ba,ta ɗauka. Da ƴar zazzaƙar muryarta ta ce,"Salamu alaikum" ya amsa da "wa'alaikis-salam, A'isha ce?" Gabanta ya faɗi saboda ta gano Uncle ne,ta amsa "Eh." Ya gyara ƙwanciya, "kin san mai magana?" Ta ce "Eh," ya ce to wanene?" Ta yi shiru ta rasa me zata ce,kina jina? Ta ce Umh,ya ce kiyi magana mana A'isha...
#######
[11/30, 21:03] Ummi Tandama😇: ____________________________
*📗MUMMUNAN ZATO📗*
*NA*
*HALIMA ABDULLAHI K/MASHI*
*ÆŠandano page 5*
Ya ce kiyi magana mana A'isha,wa ke magana da ke? Ta daure ta ce, Uncle ne. Yayi murmushi, "zan zama mijinki kuma kina ce min Uncle? Gara kin kira sunana" ta ce "bazan iya kiran sunanka ba". "To ki samin wani sunan mana ban da Uncle". Ta yi shiru, ya ce "to ba mu gaisa ba" ta yi maza ta ce "Ina yini?" Ya ce "lafiya lau Nana A'isha Saddiƙa,ya ya su Abbanki da Ummanki?" Ta ce"suna lafiya." Ya ce "za ki jini ina kiranki da sunaye duk na ki ne", ta yi shiru, shima ya kan rasa me zai ce mata,can ya ce, to bani labari" ta ce "Na me?" Ya ce, "Na komai mana" ta yi shiru,ya ce "To bani na ƙawayenki na makaranta."
Tamkar ya mata susa,ta ce "ƙawayena biyu ne,da Suwaiba Shehu Ringim,sai kuma Zainab Shitu Katsina, duk suna da kirki."
"Ashe har da ƴar garinmu? Ki ce shi kenan in kin zo Katsina kina da ƙawa, sai kuyi ta wasanku ko?".
Kalmar ta bata dariya, har ma ta ɗan dara kaɗan, sannan ta ce "wasa kuma?" Ya ce, "Eh mana,ko baƙwa wasa a makaranta?" Ta ce "sai ka ce ƙananan yara?" Ya ce "Au,na manta ashe fa ku manya ne,ni da har ina son in saya miki kayan wasa su Tedi, haka su Cartoons." Ta ce "Haba dai?" Ya ce, "To shi kenan bari in bari sai kin haifa mana Beby sai in saya mata ko?"
Zancan ya yi mata nauyi, har ma ta kasa magana,ya ce "A'isha" ta ce "Umh" "kin ji me nace?" Ta ce "Um," "to kin yi shiru" ta ce "Uncle Ina jin bacci," ya ce"shikenan yi baccinki, sannan ki yi mafarki mai ƙyau na ƙyawawan yara masu kama dani" ya kashe wayar.
Shiru ta yi tana mamakin zancan da Uncle ya yi mata,ta yi addu'a ta shafa ta runtse idanu, har bacci ya yi gaba da ita.
Hajiya Jummai wadda ta jima tsaye kanshi tana sauraron surutun da yake yi, sai jikinta ya hau rawa,ta san tabbas da budurwa yake magana, kenan Alhaji aure yake nema? Cabdi! Daga gani kuma ko ma wacece yana sonta,dubi yanda yake wani kashe murya tamkar shima ɗan matashin saurayi ne? Lallai yana neman tada zaune tsaye ne, amma don ta san in har ta nuna ɓacin ranta yanzun ba zata san komai game da yariyar ba,don haka sai ta sako makirci da kisisina.
"Alhajina kai kuma da wa kake samartaka a waya?"
Cike da walwala ya dube ta,sanye take da rigar bacci mai santsi, ɗan gashin kanta da ya rage ta tufke shi da ƙyar ma yake tufkuwa saɓanin da da take da gashin da yawa, tsabar ƙalƙalin da take ma gashin duk ya karye.
Ya miƙa mata hannuwanshi alamun ta zo, sai ta basar ta zauna gefenshi, ta kuma cewa da shi.
"Kai da wa kake waya?"
Ya ce, "ƙanwarki to be insha Allah." Ta danne wani abu da ke son taso mata.
"A ina ka samo ta? Nifa ina jin tsoron ka ƙara aure yanzu in ina tuna baya."
Ya ce"to ni kaina a tsorace nake,Æ´ar abokina ce na Jigawan nan,wato Mustapha Gumel."
Ta miƙe da sauri tare da faɗin "Dama na san za'ayi haka,wato yaga kuɗi za'a ɗora shi manajan kamfani ba dole ba, kai ma in baka so cutarshi ba ai sai ka gaya mishi cewa gidanka duk wadda ka auro mutuwa suke yi."
Ya dube ta, "To menene na tada jijiyar wuya? Har kina gaya min cewa In ba na so cuta ba, wato ni ne macucin ko?"
Shiru ta yi ranta yana tafasa.
Ta miƙe tsaye "wallahi wannan karon ba zan yarda ba,ban amince da auranka ba, shiyasa ka ke waya har kana wani cewa zata haifa maka yara? Sai dai ka zaɓa ko ni ko ita, haka kawai kana auro matan suna mutuwa,ƙila ma ana can ana zagina ana cewa nice ke kashe su to ba zan iya ba."
Ya dube ta,"zan auro ta, itama ta zo ta mutu,batun yarda kuma bana neman yardarki tunda bake bace Hajiya Sa'adatu uwata ba,kin ji ko? Batun kamfani kuwa da kike magana naga ba naki bane,bana kuma son shiga sharo ba shanu,in ma kyauta na bashi ba ruwanki sannan ki sani rashin mutuncinki da ki ka iya kada ki yarda ya zo kaina."
Fuu! Ta fice ta bar mishi ɗakin, kallo ya bita da shi, cikin mamakin ɗaga hankalin ta da tayi. Sam bai za ci haka daga gareta ba, saboda duk auren da ya yi a baya bata taɓa nuna damuwarta ba sai wannan.