Sashe 18
Mummunan Zato Part 1 Complete Hausa Novel · about 9 min read
Ɗakin Hajiya Jummai suka nufa,tana zaune ta doka tagumi,jin sallamar maigidan ta yi wata gwauruwar ajiyar zuciya. Ya ce,ina ne ake yin kitso Jummai?" Ta ce waza ayima kitso? Ya ce Beby ce,ta nanata sunan cewa Beby? Wacece haka? Kafin ya bata amsa A'isha ta shigo da sallama. Ran Jummai ya dugunzuma amma sai ta daure ta ce um kuje saloon ni dai can nake zuwa. Ya ce muje Beby, A'isha ta ce sai mun dawo Hajiya, Jummai ta ce "um hum" da ƙyar ta amsa,gaba ta shiga shi ke jan motar dan direba ya taso ya ce barshi malam Sale, in ka gansu zaka za ci ƙaramar ƙanwarshi ce ko kuma ƴarshi ta fari. Wani ƙaton comflek ya kaita sannan ya sadata da wani shahararren shagon gyaran kai, hannu ya riƙe mata yau ce rana ta farko da ya taɓa taɓa jikinta, shima ɗin ba wai don yaji wani abu bane a'a ya yi haka ne kawai don wani nishaɗi da yake cikin ranshi, yana son tafiya da yara, kasancewar shi sanannan mutum mai shagon da ƴan aikinta suka shiga yi mishi gaisuwa irin wadda ake yiwa manyan ƙasa. Ya ce,ga Bebyna tana son a gyara mata gashinta, mai shagon da kanta ta cire mata hijabi ta ce mai za'a saka miki? A'isha ta ce a'a kitso nake so,matar ta ce, to amma sai an ɗan wanke shi ya yi datti.
A'isha ta ce to amma kada a ƙona min gashina, Uncle ya ce kuyi mata yanda take so ku kula da ita,zan je na dawo,ya dube ta zan je in dawo,ya kalli mai shagon ku bata take care please,ta ce kada ka damu nan suka wanke mata kai suka gyara mata ƙunba suka yar fa mata kitso, har da wankin ƙafa dan ma sunyi taƙi ta ci wani abu.
Bayan ya kirata ta ce an gama ya iso,ba tare da ɓata lokaci ba suka ce mishi dubu uku, shi kam bai ma san me ya ɗibo ya basu ba, daga nan haka ya shiga yawo da ita guraren kayan ƙwalama da na wasan yara. Har dariya ma abin yake bata. Sai da suka biya gidansu wani abokinshi Alhaji Najib, matarshi mai kirki Hajiya Ummi, ita ma ba wata babba ba ce yaranta biyu amma tana da Uwargida yaranta biyar. Zuciyar A'isha ta ƙwanta da Ummi,sun ɗan yi hira sannan suka wuce gida, da ledoji ta shiga gidan shima ya shigo da wasu na Hajiya Jummai ne itama ya siyo mata abubuwan da take so.
Tana zaune a falo ita da su Safiya, suna yin sallama Suwaiba ta yi sauri tasa remote ta rage radio da ya cika gidan da kiɗa sannan kowace ta shiga neman ɗanƙwalinta, ita ko Hajiya Jummai sai ta kau da kai tamkar bata san sun shigo ba, gurin ta A'isha taje ta yi mata sannu da gida, sai ta wayance da cewa ai bata gansu ba, har sun dawo? A'isha ta ce eh,ta nufi ɗakinta. Zaman A'isha na ɗan kwanakin ta gama yarda Uncle ɗinta shi ba mugu ba ne ba ya shan jini haka nan ba ɗan yankan kai ba ne, ta yarda matan shi na baya ƙwanan su ne ya ƙare.
Shi ko nashi ɓangaren zuciyarshi ta amince da cewa kusantar matan da yake yi ne sanadin mutuwar su, domin ga A'isha, tafi wata ko zazzaɓi don haka ko sha'awar kallonta da auratayya ma ba yayi. Ita ko Jummai jin shirun nan ya yi matuƙar ɗaga hankalinta.
A'isha tana zaune Uncle ɗinta ya shigo cikin tsokana ya ce Beby duk school ɗin da naje ban samar miki Form ba sun ƙi ɗaukarki, jikinta ya yi sanyi ta ce, to Uncle bari na koma makarantar da nake, ya yi dariya ya miƙo mata form din Ulil Albab,ya ce amma fa ta ƙwana ce,zamu je gobe su yi maki interview,tsabar murna bata san lokacin da ta rungume shi ba tana murna, tare da zabga godiya, cikin satin ya gama mata komai bayan sun mata interview,sai suka maida ta (SS1) maimakon (SS2) da take inda A'isha ta ji daɗin makarantar haɗe take da islamiyya.
Ranar da ta halarci makarantar ta ruɗe da ganin tsarin makarantar duk abinda ake sai wa ɗangata Uncle ya sai mata. Sannan ya yi mata nasihar ta kula da kanta kuma ta kama bakinta kada ta ce ita matar aure ce, tunda makarantar bata matan aure ba ce,ta kula da addininta. Ta yi abinda ya kaita, Ummanta da Abbanta duk suma sun mata nasihar, ko da ta je yiwa Jummai sallama ko kallonta bata yi ba, haka ta fito jiki ba ƙarfi,su Sofy da Suby kuwa dariya suka shiga yi suna cewa ci baya.
Tun zuwan A'isha makaranta ta samu ƙawaye kasancewar ta mai ƙwar jini. A'isha irin mutanen nan ce waɗanda nan da nan sun shigar ma mutum rai,hulɗar ta dasu Samira Kabir Malumfashi, Amina Sani Katsina,Zainab Tahir Kaita, ya sata ƙara wayewa, kasancewar su ƴaƴan masu da shi. Itama tun daga shopping ɗinta suka gane ƴar wani don ɗin ce, suna karatu sosai don makarantar babu wasa.
Ranar da ta cika sati uku, Uncle ya kawo mata ziyara lokacin suna zaune da su Samira suna tsifar kai, domin duk ranar Lahadi suke yin kitso, wata mai kula da gefen su ta zo, ta ce cikinku wacece A'isha Mustapha? Ta dube ta cikin razana ni ce,ta ce to kizo kina da visitor, tun kafin ta isa gurin da aka tanada don ganawa da maziyarta, ta gama yanke hukuncin cewa Uncle ne. Don haka ko da taga shi ɗin ne bata wani ji mamaki ba,ta yi murna da ganinshi sosai,ta rusuna ta gaishe shi ya amsa shima yana mai tsokanarta da cewa, wato kinfi son school fiye da gida ko? Tana dariya, ta ce me yasa haka Uncle? Ya ce,naga kin ɗan yi ƙiba ne,ta sake yin ƴar dariya sannan ta ce ina su Hajiyarmu da kuma Hajiya? Ya ce suna lafiya sun ma ce in gaida ki. Ta ce Anty Nafisa fa? Ya ce tana lafiya, kullum mukayi waya sai ta tambaye ki,ta yi ƴar dariya. Ya ce kin yi ƙawaye yanzun na sani ko? Ta ce eh to sai dai ƴan ɗakinmu kuma suna da kirki bari na kira maka su,ya ce to Bebyna kira su.
Ta je ta kira su wai su zo su gaisa da Uncle ɗin ta,ya gaisa dasu ya yaba dasu har ranshi ya kuma yi masu ƙyautar da tasa su doguwar godiya, sannan ya ce ku dage da karatu ku dinga taimakon junanku ta gefen karatu kun ji ko? Suka ce to Uncle mungode,ya ce yauwa ban da faɗa. Bayan tafiyarsu ne ya tambaye ta koda matsala? Ta ce babu komai suka fito ta raka shi har cikin mota,yau ce rana ta farko da ya saka tafin hannunshi cikin nata ya haɗa su ya murza ta dubeshi, sannan ta sunkuyar da kai amma sai tana jin wani yanayi mai wuyar fahimta. Tamkar yana isar da wani saƙo ne daga jikinshi zuwa nata. A hankali ta zame yatsun ta daga nashi, shima jikinshi babu ƙwari ya miƙo mata kuɗi,ta kasa kallonshi sai dai cikin siririyar murya ta ce bani fa da matsala Uncle, ya ce na sani Beby ki dai amsa.
Ta samu su Samira suna labarin Uncle ɗin, A'isha wai mutumin nan ya yi wallahi, A'isha ta ce kamar ya ya kenan? Amina Sani ta ce komai ma, A'isha yana da yara? A'isha ta ce a'a matarshi bata taɓa haihuwa ba. Zainab ta ce ayya ni kam ƙyawunshi ne ya kasa tsere ma idanuna, amma ku fulani ne ko? A'isha dai ta ce eh, ranar dai sun kuma yarda A'isha ƴar gata ce,kusan duk sati uku Uncle yana zuwa duba A'isha, sannan cikin makarantar akwai wayar da ɗalibai suke amfani da ita yana kira haka ma Abba yana kiranta.
Cikin haka sukayi jarabawa suka sami hutu, inda Uncle ya zo ya ɗauke ta Hajiya Jummai kuwa wadda rashin mutuwar A'isha yasa ta yi wurjan-wurjan, tamkar ta zare saboda tashin hankali,tana jin cewa yau A'isha zata dawo bata yi ƙasa a guiwa ba gurin fito da dukkan asiran da ta tanada na gurin bokaye daban-daban ta shiga zuba su wasu na binnewa ne wasu kuma na yarfawa,kai har toilet ɗin A'isha sai da ta saka asiri cewa tayi wai ya buɗe ɗakin za a share mata, kafin ta iso,shi ko har da sa mata albarka.
Yanda yaga A'isha ta ɗan murmure har wasu ƴan mazaunai ta yi sannan ƙirjinta ya ɗan yi tudu ta riga sai kurum ya samu kanshi da sha'awar kusantarta. Ya kasa manta yanayin da ya ji a ranar da ya riƙe hannunta.
A'isha ba ta manta da addu'ar shiga gida ba,da ta ɗaki tana aje jaka ta shige toilet ɗauke da addu'a a cikin bakinta, ta yo wanka ta fito. Uche ya gabatar mata da abinci. Bayan sallar isha'i tana zaune Uncle ya shigo ya zauna bakin gadonta yini ya yi yana tunanin ta ina zai ɓullo mata? Ko ya sanar da ita ƙudurinshi game da ita? Kai in ya yi haka ƙila ta daina ganin girman shi,to ko ya....ta katse shi, lafiya Uncle? Ya ce zaki iya gyara min shinfiɗata? Ta yi ƴar dariya haba dai shinfiɗa kawai zan kasa gyarawa kuma na ke gyara nawa ma? Ya ce kin san fa gado na ba irin naki bane yana da girma,ta ce zan iya,ya ce to kiyi shirin baccinki kawai sai kije ki gyara min hope zaki iya? Ta ce why not, Uncle zan iya mana. Sam bata san nufin shi ba,don haka sai da ta gama shirinta tsaf na bacci har tana Uncle ya kawo min dabara ina dawowa sai in ƙwanta yau dai zan ga kalar wannan gado da Uncle ya ke cewa ba zan iya gyara shi ba. Hajiya Jummai tana zaune a falo lokacin da A'isha ta fito sanye da kayan bacci riga ce doguwa in and out. A'isha ta yi mata sannu, sannan ta wui. Sam A'isha bata san kishi ba sannan bata san ƙudirin Uncle ɗin nata ba,don haka kai tsaye ta shige ɗakin tare da sallama.
Jummai tana kallonta,kishi da baƙin ciki ya sa ta faɗawa ɗakinta da gudu,nata ganin A'isha ta yi haka ne don ta ɓata mata rai don ta nuna mata itama ta san daɗin namiji.amma da ta tuna bokan gindin tsamiya da na kan dutse bakinsu ya zo ɗaya,kan cewa in dai tayi amfani da maganin da suka bata ya yi amfani da ita ya koma ya yi da A'isha to an gama komai, kuma ita ta yi duk yanda zatayi yau da asuba ya kwanta da A'isha lallai ta san gawar A'isha kawai za'a ɗauko, domin bata da ja da maganar bokayen nan guda biyu dan sune abin dogaronta, wa'iyazu billa,shin hakan ta kasance?......
Mu haÉ—u a littafi na biyu.
Taku:-
K/Mashi.
A'isha ta ce to amma kada a ƙona min gashina, Uncle ya ce kuyi mata yanda take so ku kula da ita,zan je na dawo,ya dube ta zan je in dawo,ya kalli mai shagon ku bata take care please,ta ce kada ka damu nan suka wanke mata kai suka gyara mata ƙunba suka yar fa mata kitso, har da wankin ƙafa dan ma sunyi taƙi ta ci wani abu.
Bayan ya kirata ta ce an gama ya iso,ba tare da ɓata lokaci ba suka ce mishi dubu uku, shi kam bai ma san me ya ɗibo ya basu ba, daga nan haka ya shiga yawo da ita guraren kayan ƙwalama da na wasan yara. Har dariya ma abin yake bata. Sai da suka biya gidansu wani abokinshi Alhaji Najib, matarshi mai kirki Hajiya Ummi, ita ma ba wata babba ba ce yaranta biyu amma tana da Uwargida yaranta biyar. Zuciyar A'isha ta ƙwanta da Ummi,sun ɗan yi hira sannan suka wuce gida, da ledoji ta shiga gidan shima ya shigo da wasu na Hajiya Jummai ne itama ya siyo mata abubuwan da take so.
Tana zaune a falo ita da su Safiya, suna yin sallama Suwaiba ta yi sauri tasa remote ta rage radio da ya cika gidan da kiɗa sannan kowace ta shiga neman ɗanƙwalinta, ita ko Hajiya Jummai sai ta kau da kai tamkar bata san sun shigo ba, gurin ta A'isha taje ta yi mata sannu da gida, sai ta wayance da cewa ai bata gansu ba, har sun dawo? A'isha ta ce eh,ta nufi ɗakinta. Zaman A'isha na ɗan kwanakin ta gama yarda Uncle ɗinta shi ba mugu ba ne ba ya shan jini haka nan ba ɗan yankan kai ba ne, ta yarda matan shi na baya ƙwanan su ne ya ƙare.
Shi ko nashi ɓangaren zuciyarshi ta amince da cewa kusantar matan da yake yi ne sanadin mutuwar su, domin ga A'isha, tafi wata ko zazzaɓi don haka ko sha'awar kallonta da auratayya ma ba yayi. Ita ko Jummai jin shirun nan ya yi matuƙar ɗaga hankalinta.
A'isha tana zaune Uncle ɗinta ya shigo cikin tsokana ya ce Beby duk school ɗin da naje ban samar miki Form ba sun ƙi ɗaukarki, jikinta ya yi sanyi ta ce, to Uncle bari na koma makarantar da nake, ya yi dariya ya miƙo mata form din Ulil Albab,ya ce amma fa ta ƙwana ce,zamu je gobe su yi maki interview,tsabar murna bata san lokacin da ta rungume shi ba tana murna, tare da zabga godiya, cikin satin ya gama mata komai bayan sun mata interview,sai suka maida ta (SS1) maimakon (SS2) da take inda A'isha ta ji daɗin makarantar haɗe take da islamiyya.
Ranar da ta halarci makarantar ta ruɗe da ganin tsarin makarantar duk abinda ake sai wa ɗangata Uncle ya sai mata. Sannan ya yi mata nasihar ta kula da kanta kuma ta kama bakinta kada ta ce ita matar aure ce, tunda makarantar bata matan aure ba ce,ta kula da addininta. Ta yi abinda ya kaita, Ummanta da Abbanta duk suma sun mata nasihar, ko da ta je yiwa Jummai sallama ko kallonta bata yi ba, haka ta fito jiki ba ƙarfi,su Sofy da Suby kuwa dariya suka shiga yi suna cewa ci baya.
Tun zuwan A'isha makaranta ta samu ƙawaye kasancewar ta mai ƙwar jini. A'isha irin mutanen nan ce waɗanda nan da nan sun shigar ma mutum rai,hulɗar ta dasu Samira Kabir Malumfashi, Amina Sani Katsina,Zainab Tahir Kaita, ya sata ƙara wayewa, kasancewar su ƴaƴan masu da shi. Itama tun daga shopping ɗinta suka gane ƴar wani don ɗin ce, suna karatu sosai don makarantar babu wasa.
Ranar da ta cika sati uku, Uncle ya kawo mata ziyara lokacin suna zaune da su Samira suna tsifar kai, domin duk ranar Lahadi suke yin kitso, wata mai kula da gefen su ta zo, ta ce cikinku wacece A'isha Mustapha? Ta dube ta cikin razana ni ce,ta ce to kizo kina da visitor, tun kafin ta isa gurin da aka tanada don ganawa da maziyarta, ta gama yanke hukuncin cewa Uncle ne. Don haka ko da taga shi ɗin ne bata wani ji mamaki ba,ta yi murna da ganinshi sosai,ta rusuna ta gaishe shi ya amsa shima yana mai tsokanarta da cewa, wato kinfi son school fiye da gida ko? Tana dariya, ta ce me yasa haka Uncle? Ya ce,naga kin ɗan yi ƙiba ne,ta sake yin ƴar dariya sannan ta ce ina su Hajiyarmu da kuma Hajiya? Ya ce suna lafiya sun ma ce in gaida ki. Ta ce Anty Nafisa fa? Ya ce tana lafiya, kullum mukayi waya sai ta tambaye ki,ta yi ƴar dariya. Ya ce kin yi ƙawaye yanzun na sani ko? Ta ce eh to sai dai ƴan ɗakinmu kuma suna da kirki bari na kira maka su,ya ce to Bebyna kira su.
Ta je ta kira su wai su zo su gaisa da Uncle ɗin ta,ya gaisa dasu ya yaba dasu har ranshi ya kuma yi masu ƙyautar da tasa su doguwar godiya, sannan ya ce ku dage da karatu ku dinga taimakon junanku ta gefen karatu kun ji ko? Suka ce to Uncle mungode,ya ce yauwa ban da faɗa. Bayan tafiyarsu ne ya tambaye ta koda matsala? Ta ce babu komai suka fito ta raka shi har cikin mota,yau ce rana ta farko da ya saka tafin hannunshi cikin nata ya haɗa su ya murza ta dubeshi, sannan ta sunkuyar da kai amma sai tana jin wani yanayi mai wuyar fahimta. Tamkar yana isar da wani saƙo ne daga jikinshi zuwa nata. A hankali ta zame yatsun ta daga nashi, shima jikinshi babu ƙwari ya miƙo mata kuɗi,ta kasa kallonshi sai dai cikin siririyar murya ta ce bani fa da matsala Uncle, ya ce na sani Beby ki dai amsa.
Ta samu su Samira suna labarin Uncle ɗin, A'isha wai mutumin nan ya yi wallahi, A'isha ta ce kamar ya ya kenan? Amina Sani ta ce komai ma, A'isha yana da yara? A'isha ta ce a'a matarshi bata taɓa haihuwa ba. Zainab ta ce ayya ni kam ƙyawunshi ne ya kasa tsere ma idanuna, amma ku fulani ne ko? A'isha dai ta ce eh, ranar dai sun kuma yarda A'isha ƴar gata ce,kusan duk sati uku Uncle yana zuwa duba A'isha, sannan cikin makarantar akwai wayar da ɗalibai suke amfani da ita yana kira haka ma Abba yana kiranta.
Cikin haka sukayi jarabawa suka sami hutu, inda Uncle ya zo ya ɗauke ta Hajiya Jummai kuwa wadda rashin mutuwar A'isha yasa ta yi wurjan-wurjan, tamkar ta zare saboda tashin hankali,tana jin cewa yau A'isha zata dawo bata yi ƙasa a guiwa ba gurin fito da dukkan asiran da ta tanada na gurin bokaye daban-daban ta shiga zuba su wasu na binnewa ne wasu kuma na yarfawa,kai har toilet ɗin A'isha sai da ta saka asiri cewa tayi wai ya buɗe ɗakin za a share mata, kafin ta iso,shi ko har da sa mata albarka.
Yanda yaga A'isha ta ɗan murmure har wasu ƴan mazaunai ta yi sannan ƙirjinta ya ɗan yi tudu ta riga sai kurum ya samu kanshi da sha'awar kusantarta. Ya kasa manta yanayin da ya ji a ranar da ya riƙe hannunta.
A'isha ba ta manta da addu'ar shiga gida ba,da ta ɗaki tana aje jaka ta shige toilet ɗauke da addu'a a cikin bakinta, ta yo wanka ta fito. Uche ya gabatar mata da abinci. Bayan sallar isha'i tana zaune Uncle ya shigo ya zauna bakin gadonta yini ya yi yana tunanin ta ina zai ɓullo mata? Ko ya sanar da ita ƙudurinshi game da ita? Kai in ya yi haka ƙila ta daina ganin girman shi,to ko ya....ta katse shi, lafiya Uncle? Ya ce zaki iya gyara min shinfiɗata? Ta yi ƴar dariya haba dai shinfiɗa kawai zan kasa gyarawa kuma na ke gyara nawa ma? Ya ce kin san fa gado na ba irin naki bane yana da girma,ta ce zan iya,ya ce to kiyi shirin baccinki kawai sai kije ki gyara min hope zaki iya? Ta ce why not, Uncle zan iya mana. Sam bata san nufin shi ba,don haka sai da ta gama shirinta tsaf na bacci har tana Uncle ya kawo min dabara ina dawowa sai in ƙwanta yau dai zan ga kalar wannan gado da Uncle ya ke cewa ba zan iya gyara shi ba. Hajiya Jummai tana zaune a falo lokacin da A'isha ta fito sanye da kayan bacci riga ce doguwa in and out. A'isha ta yi mata sannu, sannan ta wui. Sam A'isha bata san kishi ba sannan bata san ƙudirin Uncle ɗin nata ba,don haka kai tsaye ta shige ɗakin tare da sallama.
Jummai tana kallonta,kishi da baƙin ciki ya sa ta faɗawa ɗakinta da gudu,nata ganin A'isha ta yi haka ne don ta ɓata mata rai don ta nuna mata itama ta san daɗin namiji.amma da ta tuna bokan gindin tsamiya da na kan dutse bakinsu ya zo ɗaya,kan cewa in dai tayi amfani da maganin da suka bata ya yi amfani da ita ya koma ya yi da A'isha to an gama komai, kuma ita ta yi duk yanda zatayi yau da asuba ya kwanta da A'isha lallai ta san gawar A'isha kawai za'a ɗauko, domin bata da ja da maganar bokayen nan guda biyu dan sune abin dogaronta, wa'iyazu billa,shin hakan ta kasance?......
Mu haÉ—u a littafi na biyu.
Taku:-
K/Mashi.