← Book details Mummunan Zato Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 16 OF 18

Sashe 16

Mummunan Zato Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Jummai ta ce, daina tsorona ko kunyata,ni ƴar'uwarki ce kin ji ko? Ta jawo plate ta soma zuba ma Alhaji shinkafa fara da miyar ganda,ta tura mishi, ita ko cous-cous ta zuba sannan ta ce me zaki ci ne ƙanwata? Shiru A'isha ta yi Uncle ya ce zuba mata shinkafa itama. A'isha dai tana jin su ba ta ce komai ba, domin ita ƙamshin abincin ma bai mata ba,tana ɗan tsakura tana korawa da ruwa kaɗan kaɗan,ya dube ta Beby ba ki cin abinci fa, ta ce ni dama bana cin abinci sosai. Jummai ta ce ki ci fa nan gidanki ne.

Bayan sun gama, ya dubi Jummai ya ce, to Jummai ga dai ƙanwa nan sai kiyi ta haƙuri da ita saboda yarinya ce, duk da na san A'isha tana da hankali da biyayya, duk in tayi ba dai-dai ba ki gyara mata, sannan ki nuna ta ga ma'aikatan gidan nan, ta ce insha Allah.

Ya dubi A'isha, Beby kin ga ƴar'uwarki nan kiyi mata biyayya sannan da akwai masu aiki babu abinda za ki yi hatta gyaran ɗakinki da wankin bayinki duk za su yi akwai mai girki,wato Uche kenan. Sai dai duk abinda ki ke so ƙya iya sanar dashi ga kitchen ɗin nan,za kuma a zo a saka miki wayar cikin gida a ɗaki saboda kiran masu aiki,in kin yi baƙi haka,ko dai wata matsalar,aikinki ɗaya ne jal shi ne gyaran ɗakina,wato shinfiɗa ta, to amma na ɗauke miki wannan tukunna don ba zaki iya ba.

Ta dube shi kamar zata yi magana, amma sai tayi shiru,na ta ganin menene abin wuya a gyaran gado? Nata ganin komai girman gado zata lailaye shi. Jummai ta ce, gaskiya kam, amma dai ka raba mana kwana saboda ko bata gyara maka shinfiɗar ba, saboda ƴan matsalolin ta kaga sai ka rinƙa ji,ya ce haka ne.

Bayan sun gama jawabansu, tana dai jin su,ta ƙosa ta koma ɗaki don jinta take tamkar kan ƙaya,ba don komai ba sai don Jummai,don haka ta soma hamma,ya ce je ki ƙwanta ai kafin ya rufe baki har ta miƙe ta nufi ɗakinta.

Jummai ta dube shi, Alhaji ni ko nawa ganin ba yi bane kace zaka ƙyale ta,ka san yaran yanzun da wayonsu sarai,mu da muke son yara ka tsaya renonta? Ya yi shiru, sannan ya ce ni abubuwan ne sun min yawa dubi fa yarinyar zan cutar da ita,ƙirjin ma babu komai sannan sai in dinga ganin tamkar in na ƙwanta da su ne suke mutuwa,shi yasa nake tsoro.

Jummai ta zaro idanu "kada fa asirinta ya tonu,ta ce mishi haba dai to da haka ne dani yanzun sai dai labarina ka daina wannan tunanin." Shiru ya yi yana nazarin maganarta,sai dai shi kam nashi ra'ayin ba zai taɓa ɗanɗana nauyin juna ba yanzun a tsakaninsu,yana ganin in ya ɓullo da haka ɗan sakin jikin da take mishi zata daina, amma sai ya bar wannan a ranshi don sirrinshi ne. Ya dubi Jummai ya ce haka ne,shi kenan sai ku riñƙa yin ƙwana bibbiyu in na gama ƙwanakina cike da jin daɗi ta ce Allah ya taimake mu ya bamu Sa'a, ya ce amin.

Abinda ya soma ɗaga hankalin Jummai shi ne,yau satin amarya biyu, kullum tana jiran ta ji Alhaji Saddiƙ ya ce jama'a ku zo, har yau shiru. In ta kira Karima ta mata magana sai ta ce bata da haƙuri ne sun taɓa yin wannan abin ya yi musu gaddama? Ta ce ko dai har yanzun bai ƙwanta da ita bane? Jummai ta ce oho amma yau zan bugi cikinta. Matsiyaciyar yarinya kina ganinta haka na kula zata yi salo don yanzun kin san kullum daga Ofis sai ya aiko an karɓar mishi wani zoɓo da take mishi?" Kari ta ce daina bani labari, zan dai zo gidan gobe.

A'isha kam yanzun tafi ƙosawa da karatunta,don haka sai ta ɗebo littattafan ta na makaranta tana ta karantawa, Uncle ya shigo ta ajiye ta miƙe tare da yi mishi sannu da zuwa,da sha'awa ya dubi takardun me ki ke karantawa ne Beby ? Ta ce ina ɗan duba books ɗina ne na school,ya ce kin tuna min,an kusa a koma hutu ko? Ta ce ni da jiya ma zan koma Sunday. Ya zauna kina son makarantarki ne ko in samar miki wata? Ta yi shiru sannan ta ce duk yanda kace bani da zaɓi Uncle,daɗi ya ji sannan ya ce to shikenan,nan da ƴan ƙwanaki zaki ƙara zama student ko Bebyna? Ta yi dariya har kumatunta suka loɓa. Abinda yake burge shi sosai.

A'isha tana ta gyaran ɗakinta domin tunda take sau ɗaya ƴar aikinta ta taɓa zuwa ta gyara mata daga nan bata dawo ba,don haka sai ta ci gaba da aikinta,dama ba ta ɗauke shi aiki ba,ta gama ta jona na'urar da ake saka turaren wuta,ta zuba nan fa ƙamshi ya soma tashi. Hajiya Jummai da Hajiya Kari suka yi sallama,ta amsa nan take gabanta ya shiga faɗuwa ta soma karanta Allahumma kafihim bima shi'ita,domin yanzun addu'ar da ta koma karantawa Jummai kenan.

Suka shigo ta zauna ƙasa ta sunkuyar da kai,su kuma suka zauna bakin gado. Ta gaishe su kanta yana ƙasa suka amsa cikin fara'a, sai kurum suka ji an bugo ƙofa a tsorace A'isha ta ɗago kai. Suwaiba ce cikin rashin kunya ta ce Hajiya ki zo kinyi baƙi,me kike yi ne ɗakin wannan ƴar ƙauyen? Jummai ta miƙe tana cewa ubanki nake yi kin ji ko? Ta bita suka fita. Hajiya Kari ta girgiza kai tare da cewa, Allah wadaran irin wannan tarbiyya da Jummai ta koyawa yaran nan, ta dubi A'isha ƴar nan sai fa haƙuri kin dai ga abinda nake gaya miki nan,ta sake matsowa gaya min yanda kuka yi da Alhajin naki,baki dai gudun shi ko?" A'isha ta ɗaga kai amma zuciyarta cike da tsanar matar, ta ce yauwa ƴar nan,to ya ya kukeyi ɗakinshi ki ke zuwa? Ran A'isha ya ɓaci ta yi mata banza tana ta tambayarta A'isha tayi shiru, da ta matsa mata sai ma ta saka kuka.

Hajiya Karima ta ce yau na shiga uku daga tambaya? To yi haƙuri,wayar A'isha ta soma ringing ta share hawayenta ta ɗaga Uncle ne ya ce na turo direba, ya amshi zoɓon nan na ji shi shiru, ta ce bai zo ba ko ƙila yazo bai samu wanda zaya aiko ba, ya ce to bari na kira Uche ya amsa ya bashi,ta ce to sai ka dawo, ya ce ba wata matsala ko? Ta ce a'a babu komai ta ajiye wayar bayan ta kashe ta kalli in da Karima take, tana nan zaune ba ta koma ta kanta ba, sai kawai ta shiga haɗawa Uncle ɗinta zoɓon da ta riga ta haɗa cikin wani ɗan ƙyakƙyawan ƙwando,yau har da cin-cin da diblan ta haɗa irin na bikinta ta zuba cikin wani ɗan ƙwanon tangaran saiti ne da jug ɗin ta zuba kofunan jug ɗin Uche ya ƙwanƙwasa ƙofar ta buɗe mishi sannan ta bashi tana juyowa taga Hajiya Kari ta miƙe ta ce, to sai anjima tunda kin ƙi mu yi hira A'isha can ƙasan maƙoshi A'isha ta ce to ta shige toilet.

########
[12/6, 16:20] Ummi Tandama😇: *📗 Page 15*

Cike da al'ajabi Kari ta isa ɗakin Hajiya Jummai da sauri, Jummai ta miƙe ta ce ta sanar dake komai? Karima ta ce, ina fa, wannan yarinyar tana da shegen wayo, na lura muna mata kallon biri ne ita kuma tana mana kallon ayaba.

Jummai ta dafe ƙirji ya ya ku kayi ne? Karima ta zauna,yarinyar da na matsa mata sai kurum ta saka min kuka,can kuma in gaya miki sai Alhajin ya kira ta,zo kiga kashe murya don sanabe Uncle ma take ce mishi an haɗa su soɓo da cincin an kai mishi.

Jummai ta ce,ni yanzu zama bai ganni ba,Kari shirya kawai mu nufi maguzawa in ko Boka na kan Dutse ya yi kuskuran aikin nan ne to ya cuceni,Kari ta ce daina wannan zancan kema kin san ba zaya ƙi yin aikin nan ba sai dai in tanan ne aka samu mishkila, amma yanzun ki bari sai gobe mu je muji dalili. Jummai ta ce bana bacci fa Karime, kullum sauraron ganin gawar yarinyar nake yi. Kari ta ce ki dai haƙuran ma goben.

Washegari tun safe ta fice ta riga maigidan fita, gidansu Kari ta nufa, shi dama ba'a ɗakin ta ya ƙwana ba, amma ga tsarin shi ko ba kece da shi ba zai shigo har ɗaki ku gaisa. To ya shigo ɗinne su Suwaiba suka ce mishi ta fita. Ya kalli agogon hannunshi,baƙwai da ƙwata ya dube su ina taje? Suka ce ba su sani ba,ya yi tsaki sannan ya fita. Ya samu A'isha tana gyaran gadonta, ya ce a'a Beby ina mai aikin naki ne? Ta ce Uncle ni na ce ta barshi bana son zama bana aikin komai shi ne dalilin,ya ce good,ta rusuna ta gaishe shi, ya ce zai fita,yau dai ta daure ta ce to Uncle kace ma Uche in aiki ya yi mishi yawa ni zan dinga taya shi, domin bai dace kana fita baka karya ba, kallonta ya dinga yi some times tana ɗaure mishi kai in tayi wata maganar domin sai ya ji tafi Jummai wadda ta haifeta hankali. Ya ce Beby kina son in dinga karyawa a gida ne? Ta ɗaga kai alamar eh,ya ajiye jakarshi ta Ofis ya zauna kan kujera je kitchen ki haɗo min ko menene zan ci,ta ce to amma kana ganin Anty Jummai ba zata ga kamar na canza mata tsari ba? Nan ma kallonta yake yi,ya girgiza kai sai ta saka takalmi to bara na zo ta fita ya bita da kallo zuciyarshi tana ta kai kawo an ya kuwa in ya ce zai bar A'isha sai zuwa wani lokaci ba zai ƙwaru ba? Shi yana mata kallon yarinya amma komai nata irin na masu hankali. Koda yake haka Allah yake ikonshi, sai ka ga yaro da hankalin manya.
Chapter 16 · 0% Book details