← Book details Mummunan Zato Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 17 OF 18

Sashe 17

Mummunan Zato Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ita ko tana shiga kitchen ta samu Uche yana ta aiki suka gaisa nan ta tsaya tana kallon na'urorin girkin da yake amfani da su. Ta ce,ya ɗora mata ruwan zafi, sannan ta ɗebi dankali zata fere da wuƙa nan ya amsa yasa na'urar fere-fere nan da nan sai ga shi cikin lokaci ƙanƙani ya gama nan dai ya dinga taimaka mata ta shirya mishi abin kari mai sauƙi tunda sauri yake yi ta cika tire.

Ta zauna gabanshi tana cewa Uncle yi haƙuri na tsaida kai, ya ce Beby kenan,nan ta haɗa mishi tea tare da baje mishi dankali da ƙwai, duk da yana cewa tea bai dame shi ba,ya sha sosai, har ma ya gano ba wai baya son tea ɗin ba ne,ba a iya haɗawa bane. Ya dubi A'isha ya ce Beby kin san da can ina shan tea lokacin ina gidan Hajiya, daga baya sai na ji ban son shi,ta ce la ban sani ba shine kasha da ka gaya min me ka fi so da nayi maka shi. Ya ce a'a wannan ya yi min daɗi ina son irin shi, amma yaushe za ki min irin kunun gyaɗannan da Ummanki take yi? Ta ce gobe in ka fita ka ce Uche ya zo zan rubuta abubuwan da zana yi amfani da su sai ya siyo zan maka gobe,ya ce na gode.

Sun isa maguzawa kai tsaye suka zarce gidan bokan dutse,sun samu wasu halakakkun ƴan'uwansu a gurin, sai da suka jira suka fito sannan su kuma suka shiga. Yana kallon su ya soma sheƙa dariya tare da cewa, kowane shege ya ci tuwo damu miyar ma ba zai sha ba, Hajiya Jummai ta kalleshi,na kan dutse me ka ke nufi? Kari tayi saurin cewa ba dai ka ɓata mana aiki ba? Ya kuma ƙwashewa da dariya,na san dole ku dawo domin na san ba zaku ga da ƙyau ba. Jummai ta zaro idanu ya ce ke ƴar tselan uwar menene na zare idanu,kin maida ni kidahumi tunda ina daji ban san komai ba,kin kawo tsohuwar mota buga-buga an kawo min,to nima shi yasa na ce zaki gani, zufa ta shiga ketoma Hajiya Jummai, ta ce kash, to yanzu ya ya za'ayi ne? Ya ce ki zube kuɗi in miki aiki, ta ce haba na kan dutse, wannan aikin ai na biya ka na motar ne kurum aka sami akasi, ya ce ban san akasi ba,ta ce to naji yanzu nawa zan ba da? Ya ce sai kin zube min dubu ɗari biyu,shiru tayi abin duniya ya ishe ta,ta dubi Karima,to yanzu ya ya kenan? Kari ta ce kawai ki nemo kuɗi kin san na dutse bai san Allah ba bare a roƙe shi," ta ce to shikenan zamu dawo ta miƙe cikin damuwa,Karima ma ta miƙe suka fita. Cikin mota Hajiya Jummai sai mita take yi har da kukanta don baƙin ciki Karima ta ce ɗan iska ko yaushe ma ya san mota da har yasan an yi mata ƙwasƙwarima ne? Jummai ta ce bar matsiyaci ni yanzu ma kuɗin cikin account ɗina da ƙyar in ya kai dubu ɗari, Karima ta ce ki ƙwaƙula jikin shi mana. Hajiya Jummai taja tsaki tare da cewa, kada ki ban haushi Hajiya Kari kina yi kamar baki san halin shi ba? Kin san fa dole sai ya san me zan yi da kuɗi kafin ya bani,ta ce ke ja can, inji Kari wani sa'in sai ki ringa yin abu tamkar wawuya,ba za ki iya ce mishi biki ko sunan ƙawa ba? Ta ce, to zan dai ƙwatanta in bai bani ba sai na saida abin hannuna (warwaro) in yaso shima sai nasa a min aikin da na tambayi kuɗi zai bani,Kari ta ce kin yi tunani haka za'ayin ma kawai. Cikin satin zuwan Hajiya Jummai maguzawa uku, kuma ta kai duk abinda boka na kan dutse ya buƙata ta koma tana sauraron abinda zai biyo baya.

A'isha tana zaune tsakar ɗakinta kallon Cartoons take yi a tashar mbc 3 amma zuciyarta tana can ga tunanin Uncle ɗinta Wanda ya tafi Angeles ta ƙasar Amerika,don kasuwancinsu tafiyar ta ƙwana uku ce yau zai dawo gashi har yanzun bai iso ba, kuma tun safe ya ce sun taso,baya da abokin hira hasali ma tunda Uncle baya nan ba ta fita, domin su Suwaibar nan dariya suke mata tare da yi mata ba a wai ƴar ƙauye, ita ko Hajiya bata zama ma bare ta ƙwaɓa musu,don haka sai ta daina ma fita tunda tana da komai kuma Uche in ya gama abinci zaya kawo. Kasa ɗaurewa ta yi ta jawo wayarta ta shiga neman layin shi na can, cewa akayi ba zai je ba ta ajiye wayar ta saka kanta cikin guiwa. Sam bata ji turo ƙofa ba,bare taku sai dai taji an dafata a bayan ta. Firgigit ta waigo cike da tsoro, tare kuma da faɗin innalillahi wa'inna ilaihir'raji'un. Ganin Uncle sai taji wani shegen daɗi cikin fara'a take cewa har ka dawo? Sannu da zuwa ya ce yauwa sarkin tsoro, ta ɗan rufe fuskarta sannan ta ce zauna,ta nufi ɗan fridge ɗin dake ɗaki ta ciro mishi ruwan swan tare da kofi.

Ta tsiyaya mishi ya amsa ba tare daya zauna ba, har zai kai ruwan bakin shi yana cewa yauwa Beby. Ta ce Uncle ka zauna mana, Manzon Allah (S.A.W) ya ce kada É—ayanku ya sha yana daga tsaye. Uncle ya zauna yana cewa,na gode Beby, kin tunasar da ni,ya sha ya aje kofin bari nayi wanka ko? Kai ta É—aga shi kuma ya fita dama yau gurin Jummai yake.

A'isha kam baki tasa ki tana kallon tsarabar da Uncle ya kawo mata,shin an ya ma Uncle yana sane ya kawo mata kayan nan kodai yayi mantuwa ne? Ba wai da yawan kayan ko tsadar su ba, a'a illa ganin ƴan bulawus ne na yara tare da takalma sawu ciki, sai rigunan jeans da wandunansu, wani abin dariya har da Tedi,ta tasa kayan tana kallo tana juyawa,ƙofarta aka buɗo tare da sallama,ta amsa, Nafisa ce ta miƙe da sauri tana cewa "Anty Nafisa sai yau? Ta zauna tana cewa yauma nazo in yi muku sallama ne, A'isha ta dube ta haba? Ina za ki? Zan koma ma makaranta mana, A'isha ta cika da mamaki, ta ce dama ba ki gama ba Anty Nafisa? Nafisa ta ce sauran wata shida in kuma na tafi ba zan dawo ba, sai na gama. A'isha ta ce, Allah sarki,za ki bar Hajiyarmu ita ɗaya dama Uncle ya maida ni can kafin ki dawo, yanda A'isha ta karya murya,ta yi maganar ya yi matuƙar bawa Nafisa dariya, ta ce ban da shirme irin naki yaushe ki ka ga matar aure ta bar ɗakinta,ta koma wani gida? Ta ce can ma fa gida ne don Allah ki gaya ma Uncle dama fa ban taɓa zuwa ba tun lokacin da su innata suka kai ni.

Nafisa dariya take yi tare da ƙara yarda,lallai A'isha ƙaramar yarinya ce, Uncle ya shigo da sallama. A'isha zumbur ta miƙe tsaye tana mishi sannu da zuwa. Ya amsa yana duban ta yauwa sannu Beby,ya zauna bakin gado yana kallon Nafisa,auta kin zo ne? Tana dariya ta ce eh jiya Hajiyarmu ta ce kazo bana nan gidan Anty Fatima na ƙwana ya kuma sai ga tsaraba, A'isha ta isa fridge ta ɗibo goran ruwa da na jus ta tsiyaya ta miƙa mishi ya ce yauwa Beby shi yasa ko'ina na shiga da naji ƙishin ruwa sai kawai na tuno ki. Nafisa ta ce a'a da yake kai Uncle ɗinta ne amma ni ai bata bani ba. Cikin tsokana Nafisa tayi maganar, A'isha ta dube ta tare da cewa,ayya Anty Nafisa ba haka ba ne,ko fa gaisawa ba mu gama ba fa don Allah,ta ɗauko wani kofin tana zuba mata. Nafisa ta ce,ba wani shima Uncle ɗin naki ai tun kafin ma ya gama zama ki ka bashi. Ta miƙa mata ruwa to gashi yi haƙuri shi dai Uncle dariya ya ringa musu, A'isha ta ce sha to,ki gani nima ga tsarabata.

Nafisa tana ɗaga kayan ta shiga gumtse dariya don kada Brother ya ci ƙaniyarta, amma wannan kayan da bai wuce su Maama su saka shi ba yaran Anty Sadiya.

A'isha ta ce kuma zai min dai dai Anty Nafisa? Uncle ya katse ta da cewa,baki gwada ba ne Beby? Nawa kema ki ke za suyi miki mana.

Nafisa ta kasa daurewa sai da ta dara sosai ma. Ya ce, menene kuma na dariya? Ta ce Brother na tuna ne ta wayance da cewa, A'isha ce wai na ce nazo muyi sallama, sai ce min ta yi wai don Allah in ce maka ka maida ta gurin Hajiyarmu ta taya ta zama kada ta zauna ita kaÉ—ai, Uncle ya yi murmushi.

A'isha kenan haka suka ringa tsokanarta suna mata dariya ita ko ta dage tsakaninta da Allah in za'a kaita gidan Hajiyarmu tana so. Cikin ƙwanakin Uncle ya matsama Aisha dole take saka kayan kowanne da ɗan takalmin sa,in tasa ta kalli madubi sai ta ganta tamkar irin yaran shahararrun masu kuɗin nan waɗanda ake bala'in ji dasu.

Sai dai iyakarta ɗaki, shi ko nashi ganin nawa take bata wuce sa su ba. Yau ma riga da wando ne masu ƙyau na jeans sai dai tana sawa ta saka hijabi. Tana so ne in Uncle ya shigo yau ta ce tana son yin kitso,aiko yana shigowa koɗa ta ya soma yi,kai kai kai Beby kin ganki kuwa? Ta saka tafukan hannunta ta rufe fuska ya ce iyyeh cire hijabin in gani? Ta cire ya dinga koɗata sai dariya take yi. Can ta ce Uncle ina son yin kitso, ya dubi agogo zo muje in kai ki,ta soma murna yau dai zata fita,ta ce in cire kayan ko Uncle? Ya ce bar kayan ki saka hijabin. Iyakarshi gwiwa ta saka takalmin kayan mai ƴar igiya suka fito ya rufe ƙofar.

#######
[12/6, 22:08] Ummi Tandama😇: *📗 Page 16*
Chapter 17 · 0% Book details