Sashe 4
Meke Faruwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Ta ce tunda ba bani zai yi ba ai batun hanawa ma bata taso ba, shi fa yanda na kula koma menene kije kiyi amma kada ki tambaye shi, sukansu kishiyoyin nawa da yake sonsu baya musu komai, amma don rashin tunani suna nan suna ta zabga gasar haihuwa,yaran bacin kirki bare sutura, karatu kuwa sai dai na zagi ashar kam, kwando-kwando za ki ga dan karamin yaro yana saukewa, gaskiya 'yan gidanmu su ne suke bata ma zage zagi suna, shin haka kowane gida suke yi? Hajara tace a'a akwai dai masu yin amma ba duka ba.. Cike da farin ciki tabar gidan hajara, ta samu Bilkisu da yan kannanta a cikin daki, tana koya musu darasin lissafi, nan ta zayyane ma Bilkisu komai, Bilki ta ce mamanmu ki bari ni nayi aikin in an samu, ta ce a'a nafi soe ni in yi bana son kije ki bata ma masu gidan har su sallame ki, bukatarmu ya zama bata biya ba. tace mamanmu amma kinsan bana fada ko? tace na sani maigado, amma ki bari sai dai an samu din kisan ke yarinya ce ba kowane abu ne zaki iya yin shi ba. Sallamar Mansura ta katse su, suka amsa ta shigo kusa da mamanmu ta zauna sannan tce mamanmu ina kwana? Suja gaisa ta dubi Bilkisu tace "Bily ya dai, yaushe zaki fara shiga school ni dai on monday zan fara zuwa. Bilki tace ni kam ba rana Mansu, kila ma sai second term. Mansura tace akan me? Tace kudi, mamanmu tace kin san ko mai yanzu sai da kudi ana cewa ne dai makarantar gwamnati amma suma duk shegiyar darin ce ga kudin motan zuwa makaranta kullum mansura tace bari Abbanmu yazo week end zan gaya masa. Bilki har suna hada baki da mamanmu, a'a kar ki yi masa magana shima yana ji da nasa iyalin. Mansura tayi shiru, amma a ranta ta raya sai ta fada mashi... Haka kuwa yana dawowa ta gaya mishi, ya tambaye ta ko njawa suke nema? Ta ce ya basu kowanne ita dai bata sani ba, kuma ta san ko ta tambaye su ba zasu fada ba. Dubu goma ya bata yace, gashi ki basu." sai da ta kai kudin mamanmu da yaranta suka je suyi godiya,Bilki kuwa sai da tayi kukan murna, sannan tana ta mamakin dama da gaske ne akwai iyaye masu yiwa 'ya'yansu hidima? Ba sabanin iyayansu mata da wahala? Cikin nasara ta shiga j.s.1 mansura kullum in za su je makaranta sai ta saka direbansu ya biyo sun dauki Bily, sunan da ta ke kiran bilkisu kenan, ita kuma Bilki tace Mansu, wani abin da yake kara ba Bilkisu mamaki shi ne, yanda mafarkin Yarima ke kara yawaita a gare ta, ko gyangyadi take sai ta yi bare barcin dare. saboda sabon da suka yi har ta saka mishi Yarima aboki, shi ko yana kiranta Beauty, tana son sanar da mamanmu amma tasan mamanmu zata ce shirme ne, shi yasa take bar ma cikinta don ko mansu bata taba ba wa lbri ba. cikin haka hajara tazo ta ce, an samu aiki. Mamanmu tace ai ko zan yi,
[8:46AM, 12/28/2016] â€?+234 814 912 1821â€?: ðŸµMEKE FARUWA 09 ðŸµ
Suka je gidan hajara inda hajiyar da za a yiwa aikin take jiransu.Bayan sun gaisa tadubi mamanmu tayaba da tsaftarta don haka tace girki nake so zaki iya? Mamanmu tace me zai hana.Nan suka sasanta ita da hajiya kilishi, gidanta na nan tudun wada, sun sasanta kan dubu uku, kuma za'a dinga zuwa ana daukarta haka nan za'a dawo da ita ko da ta samu maigidan nasu da batun sai yace,shi ina ruwan shi,ta dai sani dole ran girkinta tazo shima ta mishi,dama tasan haka zai ce,tunda shi dama baya son ma mace tace ko da bani kudin kamu,wani lokaci takan zauna tana tunani, anya maigidansu yana son lahirarshi ta mishi kyau?In'yan abinshi suja motsa haka zai je ya nado tsiranshi yazo ya zauna gaban'ya'yanshi yana ci ba zai sammusu ba in ma yaga suna kallonshi sai yace kai daina kallona ka da ka saka ni in kware.Ko ya fita bakin titi da yamma ya sayi doyarshi da kwai ya zauna yana ci in an ce yara suzo suce yaba da kudin cefane sai yace kai zauna nan kayi wasan ka shareta,kuma fa in yaron nan ya zauna haka zai cinye ya hana yaron, halin wannan mutum sai shi hakika baici sunnanshi ba. Cikin sa'a Mamanmu ta soma aiki tana tafiya da safe in yaranta sun tafi makaranta da sha biyu suke maidota gida, in ta gama musu abincin rana domin tana son ta zo ta sallam yaranta. hajiya kilishi kan ce Dibar musu ki kai musu. Sannan karfe hudu zata koma tayi na dare, in ranar girkinta ne kuma sai shida take tafiya don ta samu ta gama na gida. Su kam su ladiyo, nan suka soma nuna hassada tare da canza mata suna daga uwar mata zuwa boyi. Su yi ta mata habaici tare da maganganu marasa dadi, kafin wani lokaci mamanmu da 'ya'yanta sun canza,sunyi kyau, saboda cima ta canza in ta kawo abincin takan dibar musu ta mika ma ladiyo tace su ba wa yara, suna zaginta suna komai haka zaki ga suna kason su sai kace daukin nama su da ya'yan suna ci tandar harshe. Hajiya kilishi tana da yara mata kusan sa'annin su Bilkisu don haka suna samun kaya. Rayuwa dai ta canza yanzu har da sabulu mai kamshi suke wanka. Cikin haka suka shiga J.S 2 lokacin alamun girma ya soma shigar ma Bilkisu, kyanta ya soma bayyana, duk layin kowa sai zancenta yake yi, sun kuma kara shakuwa da mansura duk in da kaga zara za ka ga wata.Bilkisu tana da kulafucin karatu don haka bata da lokacin komai sai na karatu. Azumi ya matso gashi, lokacin ana fama da rashin kudi a gari, 'yar doyar da maigidan ya kawo buhu daya ce, nan ya kasata gida hudu yace kowa ya kwasa sannan kada wacce tai mishi zancan geron kunu domin ba shi dashi, cikin haka Azumi ya kama. Saboda rashin hankalin su ladiyo sai suka ce ma maigidan su fa kowa tayi girkinta kenan suna kyashin taimakon juna, maigida yace wannan lalurarsu. Mamanmu ta ji dadin hakan domin ya'yanta hudu ne,kuma dama aiki yana mata yawa,ranar girkinta yanzu kam hajiya kilishi tace ki dinga hada girkin tare da yaranki,dama ga alale da kunun tsamiya na sadaka da ake yi ana bai wa al'ummar Annabi sai kurum ta huta da yin girki biyu,in ma dakinta yake sai ta dibi nashi cikin kwano samira da kunu a kofi. Bilkisu taje ta amso, wataran ta roki direban ya kawo nan zaka ga malam maman an baza tabarma tsakar gida ana kwasar gara, cefanan wani kai ka kasa, haka matan ke ce mishi,in sunga yana rawar kan cin abinci ran girkin mamanmu,haka nan mijinta da yayi rabon kayan azumi shinkafa, masara,gero,da kuma suga sai daya ba mamanmu kowanne buhu,jikin kishiyoyinta ya dauki bari bakin cikinsu ya kasa boyuwa ita kam kowa sai da ta dibar mishi har 'yan sauran sassan da su rukarta su goggon sasa tare da matan yayyin maigidan nasu da na kannai. Wato mamanmu mace ce mai rama alkairi ga duk wanda ya mata sharri, tana da matukar hakuri tare da sanin ya kamata, in ban da haka yanda kishiyoyin nan nata suke mata kai har shi kanshi maigidan yafi mata wulakanci akan sauran kishiyoyin nata, amma hakan bai sa tayi tunanin cin zarafinshi ko kishiyoyin ta ba sai ma kyautata musun da take yi, shi yasa kullum cikin ci gaba take. Hatta abincin sadaka ko nata in tayi sai ta basu..
[8:46AM, 12/28/2016] â€?+234 814 912 1821â€?: ðŸµMEKE FARUWA 10ðŸµ
[8:46AM, 12/28/2016] â€?+234 814 912 1821â€?: ðŸµMEKE FARUWA 09 ðŸµ
Suka je gidan hajara inda hajiyar da za a yiwa aikin take jiransu.Bayan sun gaisa tadubi mamanmu tayaba da tsaftarta don haka tace girki nake so zaki iya? Mamanmu tace me zai hana.Nan suka sasanta ita da hajiya kilishi, gidanta na nan tudun wada, sun sasanta kan dubu uku, kuma za'a dinga zuwa ana daukarta haka nan za'a dawo da ita ko da ta samu maigidan nasu da batun sai yace,shi ina ruwan shi,ta dai sani dole ran girkinta tazo shima ta mishi,dama tasan haka zai ce,tunda shi dama baya son ma mace tace ko da bani kudin kamu,wani lokaci takan zauna tana tunani, anya maigidansu yana son lahirarshi ta mishi kyau?In'yan abinshi suja motsa haka zai je ya nado tsiranshi yazo ya zauna gaban'ya'yanshi yana ci ba zai sammusu ba in ma yaga suna kallonshi sai yace kai daina kallona ka da ka saka ni in kware.Ko ya fita bakin titi da yamma ya sayi doyarshi da kwai ya zauna yana ci in an ce yara suzo suce yaba da kudin cefane sai yace kai zauna nan kayi wasan ka shareta,kuma fa in yaron nan ya zauna haka zai cinye ya hana yaron, halin wannan mutum sai shi hakika baici sunnanshi ba. Cikin sa'a Mamanmu ta soma aiki tana tafiya da safe in yaranta sun tafi makaranta da sha biyu suke maidota gida, in ta gama musu abincin rana domin tana son ta zo ta sallam yaranta. hajiya kilishi kan ce Dibar musu ki kai musu. Sannan karfe hudu zata koma tayi na dare, in ranar girkinta ne kuma sai shida take tafiya don ta samu ta gama na gida. Su kam su ladiyo, nan suka soma nuna hassada tare da canza mata suna daga uwar mata zuwa boyi. Su yi ta mata habaici tare da maganganu marasa dadi, kafin wani lokaci mamanmu da 'ya'yanta sun canza,sunyi kyau, saboda cima ta canza in ta kawo abincin takan dibar musu ta mika ma ladiyo tace su ba wa yara, suna zaginta suna komai haka zaki ga suna kason su sai kace daukin nama su da ya'yan suna ci tandar harshe. Hajiya kilishi tana da yara mata kusan sa'annin su Bilkisu don haka suna samun kaya. Rayuwa dai ta canza yanzu har da sabulu mai kamshi suke wanka. Cikin haka suka shiga J.S 2 lokacin alamun girma ya soma shigar ma Bilkisu, kyanta ya soma bayyana, duk layin kowa sai zancenta yake yi, sun kuma kara shakuwa da mansura duk in da kaga zara za ka ga wata.Bilkisu tana da kulafucin karatu don haka bata da lokacin komai sai na karatu. Azumi ya matso gashi, lokacin ana fama da rashin kudi a gari, 'yar doyar da maigidan ya kawo buhu daya ce, nan ya kasata gida hudu yace kowa ya kwasa sannan kada wacce tai mishi zancan geron kunu domin ba shi dashi, cikin haka Azumi ya kama. Saboda rashin hankalin su ladiyo sai suka ce ma maigidan su fa kowa tayi girkinta kenan suna kyashin taimakon juna, maigida yace wannan lalurarsu. Mamanmu ta ji dadin hakan domin ya'yanta hudu ne,kuma dama aiki yana mata yawa,ranar girkinta yanzu kam hajiya kilishi tace ki dinga hada girkin tare da yaranki,dama ga alale da kunun tsamiya na sadaka da ake yi ana bai wa al'ummar Annabi sai kurum ta huta da yin girki biyu,in ma dakinta yake sai ta dibi nashi cikin kwano samira da kunu a kofi. Bilkisu taje ta amso, wataran ta roki direban ya kawo nan zaka ga malam maman an baza tabarma tsakar gida ana kwasar gara, cefanan wani kai ka kasa, haka matan ke ce mishi,in sunga yana rawar kan cin abinci ran girkin mamanmu,haka nan mijinta da yayi rabon kayan azumi shinkafa, masara,gero,da kuma suga sai daya ba mamanmu kowanne buhu,jikin kishiyoyinta ya dauki bari bakin cikinsu ya kasa boyuwa ita kam kowa sai da ta dibar mishi har 'yan sauran sassan da su rukarta su goggon sasa tare da matan yayyin maigidan nasu da na kannai. Wato mamanmu mace ce mai rama alkairi ga duk wanda ya mata sharri, tana da matukar hakuri tare da sanin ya kamata, in ban da haka yanda kishiyoyin nan nata suke mata kai har shi kanshi maigidan yafi mata wulakanci akan sauran kishiyoyin nata, amma hakan bai sa tayi tunanin cin zarafinshi ko kishiyoyin ta ba sai ma kyautata musun da take yi, shi yasa kullum cikin ci gaba take. Hatta abincin sadaka ko nata in tayi sai ta basu..
[8:46AM, 12/28/2016] â€?+234 814 912 1821â€?: ðŸµMEKE FARUWA 10ðŸµ