Sashe 6
Meenalyn Daddy Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Kasan cewar tsakanin Kaduna da funtua tafiyar two hours ce,hakan yasa cikin lokaci suka iso funtua,suna shiga funtua Alhaji Abba ya kalli mahaifinshi wato alhaji ya ce"Alhaji kace kyauyan Funtua ne,tom gamu cikin Funtua ta ina zamubi?"Alhaji shiru yayi sannan ya ce " Ikon Allah shekaru aruru kaga hanyar ta b'acemin sai dai muyi tambaya asamu ahanya,ka fita kasamu wani ka tambaye shi layin kad'anya"
Daddyn Meenal fita yayi daga cikin motar ya tambayi wasu nan dake zaune bakin titi.Nan fa suka nuna mai hanya suka ce kafin kakai d'andume anan zaka dauke hanyar ,sai karik'ayi kana tambaya"Godiya daddyn meenal yayi ya koma cikin motar,sai da ya koma baya sosai sannan yabi kwatancan da sukai mai.Alhaji Abba yana tafiya yana tambaya ahaka har suka kama hanyar kyauyan layin kad'anya.Nanfa suna tafiya mota na sama tana k'asa kasan cewar hanya babu kyau,ahaka suka shiga cikin garin layin kad'anya ,suna shiga daddyn Meenal ya kalli Mahaifinsa ya ce"Alhaji gamu a cikin garin,zaka'iya gane gidan?"."Ina Sani bazan ganeba,amma ka sauka katambayi gidan Malam Haruna mai allo".Daddyn meenal fita yayi ya tambayi wasu matasa da ke zaune.Aiko yana tambaya suka bashi amsa da basu San shi ba, juyawa daddyn meenal yayi ya koma cikin motar,gaba suka k'ara nan ma dai amsar iri d'aya basusan gidan ba,ak'alla sun tambayi mutane da dama amma amsar kenan basu san gidan ba.Alhaji Abba kallan Mahaifin shi yayi ya ce"Alhaji ko dai kamanta sunan shine,kaga kowa muka tambaya sai suce basu San shiba,in da ko sunan shi kenan inma ya mutune zasu ce ya rasu,shi yasa nace ko dai ka manta sunan ne?"." Mudai matsa gaba,amma taya zan manta sunan Haruna ,haka ake mai lak'abi da mai allo,mu matsa gaba mu tambaya".Daddyn Meenal shiga yayi suka matsa ,wani d'an dattijo suka gani suka tsaya ,Alhaji da kan shi ya bud'e ya fita,bayan Alhaji ya mik'amai hannu sun gaisane ya ce"Malam dan Allah gidan malam Haruna mai allo nake tambaya?".Shiru tsohonnan yayi yana tunanin inama yasan sunan nan,can bayan dogon nazarin da yayi ya ce"Wayyo haba nifa nasan nasan sunan nan da dad'ewa,amma sai na shafa'a,ai malam idan ka fad'i sunan sai ka b'ata sai dai irin mu da muka kwana biyu,amma kafi shekara talatin rabanka da kyauyan nan?".
Meenal da ke jin su daga cikin mota tsaki tayi ta ce"Kaji daddy wallahi d'an kyauyan mutum nada wuyar sha'ani,daga tambaya ya dage sai zuba ma tutane surutu yake idan yasani ba sai ya fad'amana ba muwuce idanma bai sani ba ne shima musani amma ya wani turke shi da fira".Daddyn meenal murnushi yayi ya komo hannun Meenal ya ce"Meenalyn daddy kenan ai yanzu zai fad'imai mu tafi".
Daga can kuma,shohon nan ya ce"Ai malam Haruna mai allo yanzu ai shine sarkin nomar garin nan,tun da aka bashi sarkin noma sunan shi ya b'ata da Haruna mai allo ya koma Sarki,yanzu ai indai ba Sarki kace ba mutane da dama bazasu gane ba,dan ko mu da muka kwana biyu wani ya manta sunan .kaga wata kuka can ko?,tom daga nan duk yaran da ka samu kace mai gidan sarki za'akaika".
Godiya sosai alhaji yayi mai ya ciro canjin ajjihun shi ya bashi,sannan ya koma motar suka tafi.
Suna zuwa dai_dai kukar suka tambayi matasan gun gidan Sarki daga nan aka nuna musu gidan suka k'arasa.Yaran da ya nuna musu gidan ne ya shiga yayi musu sallama da Sarki .
Sarki fitowa yayi yana musu sannu da zuwa, ya yi musu iso izuwa "yar ma dai_dai ciyar fadar shi.Bayan sun gaisane,Alhaji ya kalli Sarki ya ce"Malam Haruna bakaganeni ba ko?"."Wallahi Alhaji kabani sani?".Dariya kakan Meenal yayi ya ce"Tom Malam Haruna Abdullahi ne na Kaduna".Ai Sarki naji hanka ya zabura yazo ya rik'e kakan Meenal ya ce"Malam Abdullahi kaine ,Masha Allah barka da zuwa ,sannu_sannun ku"
Nanfa akafara sabuwar gaisuwa.Bayan an k'ara gaggaisawa ne ,Sarki ya ce"Gaskiya naji dad'in zumincin nan,dama bakamantani ba Malan Abdullahi ,kaddai kacemin wannan Sani ne ?"."Aiko shine banmantakaba duk da kai kamanta ni"."Wallahi banmanta da kaiba lokacin da kazomin da maganar auran sani tom nima alokacin na samu Sarkin noma na kyauyan nan har dama k'ananun kyauyukan da ke kusa damu,tom ince yau zanzo ince gobe da haka da haka dai na shafa'a,gashi kasan bantab'a zuwa ba bazan gane kwatancan da kaban ba,gashi lokacin ba lokacin waya ba kamar yanzu".Nan dai fira ta b'arke tsakanin su.Sarki wayar shi ya ciro ya mik'ama Alhaji wayar ya ce" Lalibomin number D'an juma ya kawo muku abin sanyi sana'ar shi kenan".
Dariya kakan Meenal yayi ya ce"Yo idon namu ai duk d'ayane nima baganin nake ba sosai".Kakan meenal mik'ama Alhaji Abba yayi wayar ya ce"Lalibomai number".Amsa alhaji Abba ya yi ya ce"Me ye sunan?"."D'an juma zaka gani".Cewar sarki"
Aiko Alhaji Abba na dubawa ya ga number,Kira d'aya d'an juma ya d'aga,yana d'agawa ,alhaji Abba ya mik'ama sarki wayar ya ce"Gashi an d'aga".
Sarki amsa yayi ya ce"Assalamu aikum,d'an juma kananan ne koko ka shiga Funtuar ne?".Banji mai akace ba sai ji nayi ya ce"Tom dan Allah ka aikoshi yanzu ya kawo nayi bak'ine".yana kaiwa haka ya kashe wayar yana cewa"Dama nayi tunani bayanan, ka ganshi nan kullum yana Funtua kome yake zuwa Funtua yi kullum oho mai".Murmushi kakan meenal yayi ya ce"Wai ina Yahaya ne?"."Malam ,da yake haka yake kiran shi,ya ce"Ai yaran nan da na kira d'an wajan shi ne,kasan shima Allah bai bashi haihu da wuri ba,sai da yayi wani auran ma,tom shine kad'ai yaron shi Namiji,sauran duk mata ne,nima dai shikenan jikan namiji".Sunanan suna hira wani matashin yaro ya shigo ya kawo musu laimummuka,bayan yaron ya aje zai fita ne, kakan Meenal ya ce" Shine d'an juman "."A'a shine dai Yaron da d'an juma yake barma tsaran shagon shi".Yaron zai tafi ne sarki ya kirashi ya ce"Isihu maza kaje wajan Maryama kace nace nayi bak'i daga Kaduna ai musu girki".
Sarki mik'amusu ledar da yaron ya kawo yayi ya ce"Malam Abdullahi ga laimu fa kusha dan Allah kafin ai muku girki,babu dai sanyi kasan Nepar tamu sai ahankali,dan ma d'an juma da daddare yana tada inji dan kayan suyi sanyi".Alhai mik'ama Mommyn Meenal yayi ya ce"Mariya kusha ko".Mommyn Meenal bud'ewa tayi taba kowa,sannan ta mik'ama Meenal da ke can gefe rakub'e tace Meenalyn daddy zoki amsa".Meenal cikin ya tsune fuska ta ce"Bazan shaba mommy".Sarki da sai yanzu ya lura da Meenal ,kallan Alhaji yayi ya ce"Ko ba afad'i ba nasan itace tawajan Sani,dan ga kama nan, a Kadunar take aure?".Alhaji wato kaka Meenal kai ya jinjina ya ce"Kaganta nan ko saurayi bata da shi bata da ranar aure ga mahaifinta nan ya d'aure mata gindi".Sarki kai ya jinjina ya ce"Wallahi Malam Abdullahi abinda ke damuna kenan ga d'an juma nan shima zaune babu ranar auran dan ko a wajan ku sai an mai surutu".
Sarki maida hankalin shi yayi ga Meenal yana al'ajabi dan shi gani yake ko abirni sai amma wannan surutun rashin aure,suko anan ai ba'ama magana.
Sarki kallan Meenal yayi ya ce"Zoki sha kinji irin nakune na binni".Alhai wato kakan Meenal kallan sarki yayi ya ce"karka biyema wannan miskilar banzar ,rabu da ita karta sha d'in kanta tayimawa".Kakan Meenal tashi yayi ya ce"Malam Haruna zamuyi sallah ga la'asarnan ana kira bamuyi azahar ba"."Tom bari in kira d'an juma ya turomin yaron da ya turo d'azu ya kawo lemu,sai ya rakasu can suyi sallar suhuta,mu kuma sai muyi zaman mu nan".
Sarki number d'an juma yasa aka k'ara kiramai ,ya ce ya turomai da isihu ya raka bak'in da yayi gidan su".
Aiko suna gama wayar ba dad'ewa yaron ya iso.Sarki sashi yayi ya ce" Karaka su gidan su d'an juma shashin Maryama"
Meenal dai na zunb'ure_zunb'ure ta tashi,sukabi bayan yaron.suna tafiya Mommyn Meenal na ma meenal na siha,tana cewa"Meenalyn daddy dan Allah kisaki ranki insha Allah gobe zamu bargarin nan,kinsan mutanan kyauye da tsegumu,karmu tafi anayi dake,dan Allah kiyi hak'uri karkiyi abinda zaki jawoma kanki magana".
Meenal dai bata tankama Mommynta ba,ahaka suka isa gidan.
Babban gidane Wanda akekira gidan gandu,dan gidan cike yake da yara da manya.Su meenal na shiga kallo ya dawo kan su ,nan fa mutane suka rik'a mamakin daga ina suke.wata daga cikin matan gidan ta ce"Bukuga shashin Maryama sukai ba,kunsan d'an juma ne zai kawo su".
Mommyn Meenal dai haka suka ri'kabin shashi_shashi suna tafiya,dan wadda aka Kira da Maryama wato surikar sarki ita ce Uwar gida agidan,hakan yasa sashinta ne acan k'arshe.Hajiya Mariya koda taga shashin da yaron ya shiga dasu sosai taji dad'i dan ita kanta tana tunanin yadda zasu kwana agidan suci abinci ,ganin sauran shashinan da suka baro kaca-kaca ,ga kwanonin cin abinci nan ko ina anbaza atsakar gidan.Hakan yasa mommyn meenal taji dad'in ganin inda aka saukesu saboda can fes yake babu alamun katsanta,daga gani dai matar shashin mai tsabta ce.
Zuk'unne suka sameta tana alwallah.Cikin fara'a ta tari mommyn Meenal ta ce"Barkan ku da zuwa hajiya".Ta fad'i maganar tana mai amsar jakar hannun hajiya Mariya,tayi musu iso izuwa cikin d'akinta".
Daddyn Meenal fita yayi daga cikin motar ya tambayi wasu nan dake zaune bakin titi.Nan fa suka nuna mai hanya suka ce kafin kakai d'andume anan zaka dauke hanyar ,sai karik'ayi kana tambaya"Godiya daddyn meenal yayi ya koma cikin motar,sai da ya koma baya sosai sannan yabi kwatancan da sukai mai.Alhaji Abba yana tafiya yana tambaya ahaka har suka kama hanyar kyauyan layin kad'anya.Nanfa suna tafiya mota na sama tana k'asa kasan cewar hanya babu kyau,ahaka suka shiga cikin garin layin kad'anya ,suna shiga daddyn Meenal ya kalli Mahaifinsa ya ce"Alhaji gamu a cikin garin,zaka'iya gane gidan?"."Ina Sani bazan ganeba,amma ka sauka katambayi gidan Malam Haruna mai allo".Daddyn meenal fita yayi ya tambayi wasu matasa da ke zaune.Aiko yana tambaya suka bashi amsa da basu San shi ba, juyawa daddyn meenal yayi ya koma cikin motar,gaba suka k'ara nan ma dai amsar iri d'aya basusan gidan ba,ak'alla sun tambayi mutane da dama amma amsar kenan basu san gidan ba.Alhaji Abba kallan Mahaifin shi yayi ya ce"Alhaji ko dai kamanta sunan shine,kaga kowa muka tambaya sai suce basu San shiba,in da ko sunan shi kenan inma ya mutune zasu ce ya rasu,shi yasa nace ko dai ka manta sunan ne?"." Mudai matsa gaba,amma taya zan manta sunan Haruna ,haka ake mai lak'abi da mai allo,mu matsa gaba mu tambaya".Daddyn Meenal shiga yayi suka matsa ,wani d'an dattijo suka gani suka tsaya ,Alhaji da kan shi ya bud'e ya fita,bayan Alhaji ya mik'amai hannu sun gaisane ya ce"Malam dan Allah gidan malam Haruna mai allo nake tambaya?".Shiru tsohonnan yayi yana tunanin inama yasan sunan nan,can bayan dogon nazarin da yayi ya ce"Wayyo haba nifa nasan nasan sunan nan da dad'ewa,amma sai na shafa'a,ai malam idan ka fad'i sunan sai ka b'ata sai dai irin mu da muka kwana biyu,amma kafi shekara talatin rabanka da kyauyan nan?".
Meenal da ke jin su daga cikin mota tsaki tayi ta ce"Kaji daddy wallahi d'an kyauyan mutum nada wuyar sha'ani,daga tambaya ya dage sai zuba ma tutane surutu yake idan yasani ba sai ya fad'amana ba muwuce idanma bai sani ba ne shima musani amma ya wani turke shi da fira".Daddyn meenal murnushi yayi ya komo hannun Meenal ya ce"Meenalyn daddy kenan ai yanzu zai fad'imai mu tafi".
Daga can kuma,shohon nan ya ce"Ai malam Haruna mai allo yanzu ai shine sarkin nomar garin nan,tun da aka bashi sarkin noma sunan shi ya b'ata da Haruna mai allo ya koma Sarki,yanzu ai indai ba Sarki kace ba mutane da dama bazasu gane ba,dan ko mu da muka kwana biyu wani ya manta sunan .kaga wata kuka can ko?,tom daga nan duk yaran da ka samu kace mai gidan sarki za'akaika".
Godiya sosai alhaji yayi mai ya ciro canjin ajjihun shi ya bashi,sannan ya koma motar suka tafi.
Suna zuwa dai_dai kukar suka tambayi matasan gun gidan Sarki daga nan aka nuna musu gidan suka k'arasa.Yaran da ya nuna musu gidan ne ya shiga yayi musu sallama da Sarki .
Sarki fitowa yayi yana musu sannu da zuwa, ya yi musu iso izuwa "yar ma dai_dai ciyar fadar shi.Bayan sun gaisane,Alhaji ya kalli Sarki ya ce"Malam Haruna bakaganeni ba ko?"."Wallahi Alhaji kabani sani?".Dariya kakan Meenal yayi ya ce"Tom Malam Haruna Abdullahi ne na Kaduna".Ai Sarki naji hanka ya zabura yazo ya rik'e kakan Meenal ya ce"Malam Abdullahi kaine ,Masha Allah barka da zuwa ,sannu_sannun ku"
Nanfa akafara sabuwar gaisuwa.Bayan an k'ara gaggaisawa ne ,Sarki ya ce"Gaskiya naji dad'in zumincin nan,dama bakamantani ba Malan Abdullahi ,kaddai kacemin wannan Sani ne ?"."Aiko shine banmantakaba duk da kai kamanta ni"."Wallahi banmanta da kaiba lokacin da kazomin da maganar auran sani tom nima alokacin na samu Sarkin noma na kyauyan nan har dama k'ananun kyauyukan da ke kusa damu,tom ince yau zanzo ince gobe da haka da haka dai na shafa'a,gashi kasan bantab'a zuwa ba bazan gane kwatancan da kaban ba,gashi lokacin ba lokacin waya ba kamar yanzu".Nan dai fira ta b'arke tsakanin su.Sarki wayar shi ya ciro ya mik'ama Alhaji wayar ya ce" Lalibomin number D'an juma ya kawo muku abin sanyi sana'ar shi kenan".
Dariya kakan Meenal yayi ya ce"Yo idon namu ai duk d'ayane nima baganin nake ba sosai".Kakan meenal mik'ama Alhaji Abba yayi wayar ya ce"Lalibomai number".Amsa alhaji Abba ya yi ya ce"Me ye sunan?"."D'an juma zaka gani".Cewar sarki"
Aiko Alhaji Abba na dubawa ya ga number,Kira d'aya d'an juma ya d'aga,yana d'agawa ,alhaji Abba ya mik'ama sarki wayar ya ce"Gashi an d'aga".
Sarki amsa yayi ya ce"Assalamu aikum,d'an juma kananan ne koko ka shiga Funtuar ne?".Banji mai akace ba sai ji nayi ya ce"Tom dan Allah ka aikoshi yanzu ya kawo nayi bak'ine".yana kaiwa haka ya kashe wayar yana cewa"Dama nayi tunani bayanan, ka ganshi nan kullum yana Funtua kome yake zuwa Funtua yi kullum oho mai".Murmushi kakan meenal yayi ya ce"Wai ina Yahaya ne?"."Malam ,da yake haka yake kiran shi,ya ce"Ai yaran nan da na kira d'an wajan shi ne,kasan shima Allah bai bashi haihu da wuri ba,sai da yayi wani auran ma,tom shine kad'ai yaron shi Namiji,sauran duk mata ne,nima dai shikenan jikan namiji".Sunanan suna hira wani matashin yaro ya shigo ya kawo musu laimummuka,bayan yaron ya aje zai fita ne, kakan Meenal ya ce" Shine d'an juman "."A'a shine dai Yaron da d'an juma yake barma tsaran shagon shi".Yaron zai tafi ne sarki ya kirashi ya ce"Isihu maza kaje wajan Maryama kace nace nayi bak'i daga Kaduna ai musu girki".
Sarki mik'amusu ledar da yaron ya kawo yayi ya ce"Malam Abdullahi ga laimu fa kusha dan Allah kafin ai muku girki,babu dai sanyi kasan Nepar tamu sai ahankali,dan ma d'an juma da daddare yana tada inji dan kayan suyi sanyi".Alhai mik'ama Mommyn Meenal yayi ya ce"Mariya kusha ko".Mommyn Meenal bud'ewa tayi taba kowa,sannan ta mik'ama Meenal da ke can gefe rakub'e tace Meenalyn daddy zoki amsa".Meenal cikin ya tsune fuska ta ce"Bazan shaba mommy".Sarki da sai yanzu ya lura da Meenal ,kallan Alhaji yayi ya ce"Ko ba afad'i ba nasan itace tawajan Sani,dan ga kama nan, a Kadunar take aure?".Alhaji wato kaka Meenal kai ya jinjina ya ce"Kaganta nan ko saurayi bata da shi bata da ranar aure ga mahaifinta nan ya d'aure mata gindi".Sarki kai ya jinjina ya ce"Wallahi Malam Abdullahi abinda ke damuna kenan ga d'an juma nan shima zaune babu ranar auran dan ko a wajan ku sai an mai surutu".
Sarki maida hankalin shi yayi ga Meenal yana al'ajabi dan shi gani yake ko abirni sai amma wannan surutun rashin aure,suko anan ai ba'ama magana.
Sarki kallan Meenal yayi ya ce"Zoki sha kinji irin nakune na binni".Alhai wato kakan Meenal kallan sarki yayi ya ce"karka biyema wannan miskilar banzar ,rabu da ita karta sha d'in kanta tayimawa".Kakan Meenal tashi yayi ya ce"Malam Haruna zamuyi sallah ga la'asarnan ana kira bamuyi azahar ba"."Tom bari in kira d'an juma ya turomin yaron da ya turo d'azu ya kawo lemu,sai ya rakasu can suyi sallar suhuta,mu kuma sai muyi zaman mu nan".
Sarki number d'an juma yasa aka k'ara kiramai ,ya ce ya turomai da isihu ya raka bak'in da yayi gidan su".
Aiko suna gama wayar ba dad'ewa yaron ya iso.Sarki sashi yayi ya ce" Karaka su gidan su d'an juma shashin Maryama"
Meenal dai na zunb'ure_zunb'ure ta tashi,sukabi bayan yaron.suna tafiya Mommyn Meenal na ma meenal na siha,tana cewa"Meenalyn daddy dan Allah kisaki ranki insha Allah gobe zamu bargarin nan,kinsan mutanan kyauye da tsegumu,karmu tafi anayi dake,dan Allah kiyi hak'uri karkiyi abinda zaki jawoma kanki magana".
Meenal dai bata tankama Mommynta ba,ahaka suka isa gidan.
Babban gidane Wanda akekira gidan gandu,dan gidan cike yake da yara da manya.Su meenal na shiga kallo ya dawo kan su ,nan fa mutane suka rik'a mamakin daga ina suke.wata daga cikin matan gidan ta ce"Bukuga shashin Maryama sukai ba,kunsan d'an juma ne zai kawo su".
Mommyn Meenal dai haka suka ri'kabin shashi_shashi suna tafiya,dan wadda aka Kira da Maryama wato surikar sarki ita ce Uwar gida agidan,hakan yasa sashinta ne acan k'arshe.Hajiya Mariya koda taga shashin da yaron ya shiga dasu sosai taji dad'i dan ita kanta tana tunanin yadda zasu kwana agidan suci abinci ,ganin sauran shashinan da suka baro kaca-kaca ,ga kwanonin cin abinci nan ko ina anbaza atsakar gidan.Hakan yasa mommyn meenal taji dad'in ganin inda aka saukesu saboda can fes yake babu alamun katsanta,daga gani dai matar shashin mai tsabta ce.
Zuk'unne suka sameta tana alwallah.Cikin fara'a ta tari mommyn Meenal ta ce"Barkan ku da zuwa hajiya".Ta fad'i maganar tana mai amsar jakar hannun hajiya Mariya,tayi musu iso izuwa cikin d'akinta".