← Book details Meenalyn Daddy Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 21

Sashe 21

Meenalyn Daddy Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read

Rana bata k'arya sai dai uwar d'iya taji kunya.'Yan'uwan d'anjuma gaba d'aya sun hallara da 'yan'uwan meenal .Ababbban masallacin kawo wato shak Zafar,inda har yanzu babu daddyn meenal balabarinshi .Babban abokin daddyn meenal shi ya bada auran meenal ga k'anin mahaifin d'anjuma.

Bayan an d'aura auran ne da d'an jimawa Alhaji wato kakan meenal ya naimi d'anjuma dan yanason keb'ewa da shi.

D'anjuma zaune afalon alhaji,alhaji ya kalli d'anjuma dakanshi ke ak'asa ya ce "Abdurrahman naso ace tun jiya kazo dan maganganun da nakeso da kai suna da yawa,inda kaga yau ba lokaci inda yanzu zaku juya da amarya,wato d'anjuma da farko dai kafin in fad'i abinda nakeson fad'a maka ina naiman alfarma awajanka?"D'anjuma kanshi k'asa ya ce "Alhaji babu abinda zaka naima awajena banma shi ba,dan bacin kai nasan da bazan samu meenal ba dan haka karkaji komai kome kakeso awajena ni kuma zan maka shi insha Allah ."
Alhaji cikin jin dad'in bayanin d'anjuma ya fara magana kamar haka"Abdurrahman Amina dai ta zauna agidanku nasan ka fahimsu wasu halayyarta ko kad'anne duk da ba zama mai tsawo ta yi ba,Abdurrahman nasan zakasha wuyar Amina sosai kafin kagane kanta ,abinda nakeso da kai dan Allah kayi hak'uri aduk yadda kasamu Amina watarana sai labari kuma mahak'urci mawadaci watarana zaka girbi ribar hak'urin insha Allah, sannan Amina bata san lallashi ba sai ammata jan ido take abu.Babu lokaci katashi kuje Allah yayi muku albarka Allah ya baka hak'urin zama da Amina."Insha Allah alhaji zanyi hak'urin zama da Amina kodan halaccinka agareni,nagode sosai"
D'anjuma na kaiwa haka ya tashi ya tafi dan abokanshi dama sai kiranshi suke awaya suna k'ofar gidansu meenal suna jiran abasu amarya su wuce.

Acan gidansu Meenal ko da kyar Hafsat ta lallab'a meenal tayi wanka tasa gayan da mahaifiyarta ta d'inka mata dan su basuga lefeba.Hafsat na shirya meenal tana cewa "Meenal bana son kina nuna musu wani abu aranki ki saki ranki akaiki d'in ,adai zaman aure bai yuwuwa saida soyayya ko ,da akwai wata shawara ma da zan kuma baki amma kinga yanzu ba lokaci ki bari sai munje can sai muyi magana"
Ita dai meenal cigaba da kukanta tayi ,Hafsat nacikin shiryata ne hajiya Jamila tazo takamo hanunta tace "Muje wajan mommynki kuyi sallama.

Meenal na kuka akakaita gaban mommynta,Allah sarki mommyn meenal d'inma kasa cema meenal komai tayi saboda kuka da yaci k'arfinta,da kyar dai ta iya cewa "Meenal kiji tsoran Allah kiyi biyayya ga mijinji shine abinda zakiyi ki samu ceto ranar gobe k'iyama"Meenal da kuka yaci k'arfinta cikin kuka ta ce "Mommy daddy dan Allah ina son ganin daddyna "Mahaifiyar meenal gogema meenal hawayanta tayi ta ce "Meenal ki yi tak'uri ki tashi ki tafi mutane najira daddynki zaizo har d'akinki ya ganki"

Haka aka tafi da meenal tana kuka tana ciccijewa akasata amota aka tafi da ita .Hafsat ko babu yadda batayiba dan taraka Meenal amma hajiya Jamila lurada Hafsat kamar tana zuga meenal yasa tahana tafiyar da ita.

Mutum biyu suka raka meenal d'akinta daga hajiya Jamila yayar mommyn meenal sai Aisha autarsu Mommyn meenal.Sai gaf magriba suka shiga garin Funtua inda aka kai amarya d'akin mijinta acikin unguwar wanzamai .Meenal haka ta kwana kuka babu yadda su hajiya Jamila basuyi da itaba amma tak'iyin shiru.
Washe gari da wuri abokan d'anjuma suka kawomusu tea da bread suka karya,suna gama karyawa sukayi wanka suka kuma yima meenal fad'a sosai sannan mota tazo ta d'aukesu,aifa da zasu tafi meenal rik'esu tayi tana kuka sosai dan har hajiya Jamila sai da ta tausayama meenal halin da tashiga ,haka dai suka janye suka tafi suka barta suna mai tausayamata dan yadda take nuna k'iyayyar d'anjuma abin yayi yawa.
D'anjuma ko da su hajiya Jamila zasu tafi sai da suka k'ara ankarar da shi akan hak'uri komai mai wucewa ne.Motarsu zata tafi hajiya Jamila takalli d'anjuma ta ce "Abdurrahman kashiga gida kayi lallashi dan mun baro ta tana kuka kuma bataci komai ba".

Bayan motarsu hajiya Jamila ta tashine d'anjuma ja yayi ya tsaya ya kasa shiga gidan yana mai fargabar yadda Amaryar tashi zata karb'ai,dan tunda aka tsaida auranshi da ita magana bata kuma shiga tsakaninsu ba,hasalima shi tunda tabar garinsu bai kuma ganinta ba.D'anjuma cikin shahada da fargaba ya yi Sallama ya shiga gidan jin shiru ya k'arasa cikin d'akin ,can ya hango meenal bakin kadon sai kuka take iya k'arfinta ,d'anjuma ta kawa yayi ya isa inda take ,cikin sanyin ya kalli meenal ya ce.............✍️
Chapter 21 · 0% Book details