Sashe 10
Meenalyn Daddy Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
B'angaran d'an juma ko yauma kamar kullum yana zaune acikin saif plaza dake garin funtua.D'an juma kallan Kamal yayi ya ce" Kamal kana yawan fad'amin wata magana,da sai yau nake son insan gaskiyarta,ka ce duk yarinyar da nace ina so da wuya tak'ini,shin a cikin kyauyan mu kake nufi koko har acikin gari,ma'ana cikin birni?".Murmushi Kamal yayi ya ce"Abdurrahaman a ko ina nake nufi ba wai a kyauyanku kad'ai nake nufi ba".Shiru d'an juma yayi ya ce"Kana ganin yarinyar da ta fito cikin garin kaduna tayi karatu agarin kaduna,ta tashi cikin gata ,Kamal dan Allah karka yau dareni kana ganin yarinyar nan ko zata iya soni?".
Murmushi Kamal yayi ya kamo hannun d'an juma,dan ya kula abokin nashi ya rufta da yawa ya ce"Abdurrahman,koda cikin garin Abuja ta tashi,tayi karatu acan ,sai dai son zuciya da girman kai irin na mata amma tsab zata soka".
Shiru d'an juma yayi sannan zuwa can ya ce"Kamal kallo d'aya nayi mata ,yadda naji akanta na tabbatar shi akekira so,tabbas yadda naji da kuma yadda nakeji yanzu tambari ne na soyayya,dan Allah ka ce inyi hak'uri Wallahi tafi k'arfina".
Shiru Kamal yayi ,na d'an wani lokaci sannan ya ce"Wacece ita Abdurrahman?"."Nima kaina bansan wacece ita ba,na gansu ne da Sarki,bisaga'alama dai kakanta abokin sarki ne"."Kai tom ai in hakane Abdurrahman kanada dahir,nasan sarki na sonka da yawa zai iya maka k'ok'ari ganin ka sameta".Cewar Kamal"
Shiru d'an juma yayi,sai kuma ya ce,"Ga sunanta mai dad'i ,Amina suna kiranta da Meenal,tana da fad'a da masifa,amma kasan me Kamal?".Kamal kai ya girgiza.D'an juma kuma ya ce"Tsiwarta kyau take mata,ta kasa b'acemin a ido lokacin da takemin fad'a zan kadata"
Kamal kai ya girgiza,dan yaga abin banawasa ba ne ,k'arshema sai cewa yayi"Amma idan haka ne Abdurrahman yana da kyau ka samu soyayyarta kafin ta tafi".Kai d'an juma ya girgiza ya ce"Kamal bazata soni b ,kawai dai nina san tamin shigar sauri,tabbas na kamu da sonta lokaci guda,kuma so mai wahalar fita".
Kamal da sosai ya gaskata maganar d'an juma dan ko dan yanayin yadda yake magana kamar wani maraya yasan tabbas so yayi mai shigar sauri.Kamal kallan d'an juma yayi ya ce"Kuna magana da ita ne?".Kai d'an juma ya girgiya ya ce magana da ita bazata yuwuba,yarinyar miskilar gaske ce,kuma kamar tana da jida kai bisa ga alamunta".
"Tom duk da haka dai ni shawarar da zan baka ,karik'a musu alheri ita da 'yan'uwanta kafin su tafi,sannan bahaushe yace da rashin tayi akan bar arha,lokuta da dama muna ma mututa ne kallan halinda ba d'abiyar su bace sai ka zauna dasu zaka San haka,dan haka ina mai baka shawara ka gwada sa'arka k'ila kadace" .
D'an juma kallan Kamal yayi ya ce"Kana ganin zan iya da cewa?"."Sosai ma kuwa".Cewar Kamal.Ranar dai haka d'an juma ya wuni yana mai jin wata irin fargaba akanta,dan ko ajikin shi bayajin za ta so shi ,hasalima zuciyar shi gargad'in shi take karya sake ya furta kalmar so ga Meenal.Wata zuciyar kuma ta ce "Koma biki gargad'an ba nima bazan iya furtawa".
Haka dai d'an juma ya yi ta sak'arshi yana warware abin shi,kamar yadda ya saba tafiya gida gaf magriba yauma haka ya tafi,sai da ya biya ya sai mata fura,inda yaga d'azu ta siya ,sannan ya hau mashin d'in shi ya tafi".
WAYE D'AN JUMA?:
Mahaifin d'an juma mahaifiyar d'an juma ce uwar gidan shi,sai dai Allah yasa bata samu haihuwa da wuri ba,hakan yasa Sarki wato kakan d'an juma kasan cewar yana son ganin jikan shi yasa Mahaifin d'an juma k'ara aure,inda Mahaifin d'an juma ya k'ara auran badan yana soba,sai dai bayan auran su da Lami da wata goma ta haifi d'iya mace wato Rabi suna ce mata Yaya Rabi.Lami wato kishiyar Mahaifiyar d'an juma sai da ta haifi mata uku babu namiji aciki,hakan yasa Sarki yasa Mahaifin d'an juma k'ara aure ko za ahaifar musu Namiji.Cikin ikon Allah Maryama wato Mahaifiyar d'an juma da amaryar da Mahaifin d'an juma ya aura kusan atare su kai laulayin ciki,dan sati d'aya ne tsakanin su a haihuwa,inda ranar wata juma mahaifiyar d'an juma ta haifi d'a namiji,amaryar su kuma ta haifi mace.lokacin mahaifin d'an juma na da Yara biyar duk mata,hakan yasa Sarki da Mahaifin d'an juma suka rasa inda zasu sa Maryama wato Mahaifiyar d'an juma,tsabar murnar haihuwar Namiji da akai musu.Ranar sunan d'an juma yaci sunan Abdurrahman.Tom kunsan mutanan kyauye da rad'ama mutum sunan ranar da aka haife shi,dalilin ranar juma'a aka haifi d'an juma shine fa suka b'atar da da sunan shi suka rik'a Kiran shi da d'an juma.
Tun ranar sunan d'an juma aka fara cin karo da ban-banci,dan ko sarki ya kashe kud'in da bai tab'a kashe rabin su ba sauran jikokin da aka haifar mai .Haka Sarki da Mahaifin d'an juma suka d'auki son duniya suka d'orama d'an juma.D'an juma na yaro sosai akazo layin kad'anya akai gina musu primary School,tun ana ginin makarantar d'an juma ya kwallafa rai dan gani yake wani abunne,hakan yasa ana gama ginin Sarki da kan shi ya d'auki d'an juma ya kai shi.Allah kuma yasa d'an juma nada k'okari ,ahaka dai ya kammala aji shida,kasan cewar babu secondary agarin hakan yasa Sarki ya samar mai gurbin karatu a d'an dume dan babu nisa sosai tsakanin su,ahaka-ahaka dai d'an juma ya kammala secondary d'in shi,daga nan ne fa Sarki yace ba zai shigema kafuran nan da yawa ba dan haka ya isa hakanan karatun,dole d'an juma ya hak'ura badan yaso ba.Tom daga nan fa sai kuma ya fara zaman gida babu sana'a,gashi shi saboda Makaranta da yayi bai iya aikin gona ba.Sosai rashin sana'ar d'an juma ta fara damun Maryama,ana hakane Allah yayi ma Mahaifinta rasuwa,tom da aka rabamusu gado ne Maryama ta ba d'an juma ya bud'e provision, kusan babu abinda bai sai dawa .A funtua yake zuwa Sarin kaya,hakan yasa ya fara abokai,ahaka-ahaka dai suka saba da ogan nashi,ahankali-ahankali ya fara jawoshi jikin shi yana tsare mai kayan shi,shi kuma d'an juma shima can sai yayi yaro shima yana bashi tsaron nashi,tom inda d'an juna ke tsarewa plaza ce babba ba laifi.Abinda yasa yake b'oyema sarki gani yake kamar zai hana shi,shi yasa sarki bai San abinda d'an juma ke zuwa funtua yi ba kullum.
Layin kad'an ya Yaro d'an shekara goma sha bakwai,Shatakwa,ashirin suke aure, hakan yasa d'an juma ma tun yana matakin secondary suke bashi aure amma yak'i,atakaice dai har izuwa girman shi na cikakkan namiji .Wanna yasa akema d'an juma surutu sosai,dan wasu cewama suke k'ila aljana ce ta aurai.Shiko d'an juma tunda ya taso Allah yasa baida ra'ayin irin auran garin su,macan yarinya shima angon yaro.
Tunda d'an juma ya fara mallakar hankalin shi yafi buk'atar budurwa wadda tasan abinda takeyi ba kwaila ba irin na garin su.Wannan kenan"
D'an juma haka ya hawo mashin d'in shi ya dawo gida .
Meenal ko tun da ta farka daga bacin da tayi take neman wayar da zata Kira Daddaynta ta kai k'arar alhaji wato kakanta ,akan maganar shan addu'ar da ya ce sai ta sha, idan bata sha ba baza ta tafi ba.Wayar mommyonta ko tun jiya da tayi wurgi da ita ta d'auke, wayar mahaifiyar d'an juma kuma babu caji,hakan yasa ta rasa wayar da zatai kiran.
Meenal sosai take jinta atakure zaman kyauyan,dan ko abinci rana da Mahaifiyar d'an juma ta kawo musu k'in ci tayi.
Meenal kallan Mommynta ta yi, ta ce"Yanzu mommy da ban gama Exams ba haka mutunin nan zauzo nan kawai ya kama zaunar da muta ne,Allah ni dai kije ki mai magana,idan ba haka ba zaki nai man kirasa,dan ni daga gobe bazan k'ara kwana kyauyan nan ba,tun da nazo wayana baya aiki,inda ni M.T.N garan ,dan Alllahi nidai ki san yadda zaki Mommy Allah duka mutanan garin haushin su nakeji".Meenal dai har ta gama maganarta Mommynta bata tankamata ba,hakan yasa tayi shiru.
Meenal har dare tak'i cin komai kuma dama da daddaran tuwan gari akayi,ita kuma dama ba son shi take ba,nan fa yunwa ta fara damunta,dan ko sallar magriba da kyar tayi ,tana cikin sallar ne d'an juma ya shigo gidan,bai shiga d'akin ba daga waje ya gaida Mahaifiyar meenal sannan ya mik'ama mahaifiyar shi hurar da ya siyo ya ce"Inna gashi adamama mu su".
Hajiya Mariya cikin fad'ad'a fara'arta ta ce"Tom mun gode Allah yasaka da alkairi"
D'an juma fita yayi dan yin sallah Isha'i da ake kira,saboda ya k'osa yaje gidan Sarki yaji dangartakar dake tsakanin su da su Alhaji.
D'an juma masallacin k'ofar gidan su ya fara zuwa yayi sallar Isha'i sannan ya nufi gidan Sarki.Sai dai koda yaje badamar samun sanin abinda ya kawo shi dan Sarki fira suke da Alhaji sosai,bayan sun gaisa ne Alhaji wato kakan Meenal ya ce"Yauwa Abdurrahman dama yanzu zansa Malam Haruna ya kiraka,amma inda gaka kazo ai shikenan,maza kaje gidanku ka tafomin da Amina"."D'an juma tashi yayi ya fita yana mai jin dad'i zai kuma ganinta,yana tafiya zuciyar shi na ingiza shi da cewa" Ka gwada furta mata kallamar so mana ko zaka dace".Wata zuciyar ta ce"Gaskiya yaudarar kanka kawai kake,amma kaima kasan bazata amin ce ba".Can kuma sai ya ba kan shi amsa da "Darashin tayi akan bar arha,sosai d'an juma ya yadda da wanna kalma da hausawa ke cewa,hakan yasa cikin full Confidence ya idasa gidan su".
Meenal ko ta gama Shan furar da d'an juma ya kawo mata har tayi shirin bacci ta kwanta d'an juma ya yi sallama ya shiga d'akin.............✍️
Idan kin karanta ki Comment sister😗😗
📚 MEENALYN DADDY 📚
🔔📚
*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION📚*
_{Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa}_
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=337435884671992&id=103920888023494&sfnsn=mo
*⚜️©J.A.W📚🖌️*
Na
Fadila Sani Bakori.
page 12 & 13.
Meenal ko ta gama shan furar da d'an juma ya kawo mata har tayi Shirin bacci ta kwanta d'an juma ya yi Sallama ya shiga d'akin.
Mommyn meenal zaune ita da mahaifiyar d'an juma sai fira suke,d'an juma ya shiga.
D'an juma gaida hajiya Mariya yayi sannan ya ce"Dama alhaji ne ya ce in kira Meenal,kuma naga tama kwanta"."A'a ai ba bacci tayi bari in mata magana"cewar hajiya Mariya"
Murmushi Kamal yayi ya kamo hannun d'an juma,dan ya kula abokin nashi ya rufta da yawa ya ce"Abdurrahman,koda cikin garin Abuja ta tashi,tayi karatu acan ,sai dai son zuciya da girman kai irin na mata amma tsab zata soka".
Shiru d'an juma yayi sannan zuwa can ya ce"Kamal kallo d'aya nayi mata ,yadda naji akanta na tabbatar shi akekira so,tabbas yadda naji da kuma yadda nakeji yanzu tambari ne na soyayya,dan Allah ka ce inyi hak'uri Wallahi tafi k'arfina".
Shiru Kamal yayi ,na d'an wani lokaci sannan ya ce"Wacece ita Abdurrahman?"."Nima kaina bansan wacece ita ba,na gansu ne da Sarki,bisaga'alama dai kakanta abokin sarki ne"."Kai tom ai in hakane Abdurrahman kanada dahir,nasan sarki na sonka da yawa zai iya maka k'ok'ari ganin ka sameta".Cewar Kamal"
Shiru d'an juma yayi,sai kuma ya ce,"Ga sunanta mai dad'i ,Amina suna kiranta da Meenal,tana da fad'a da masifa,amma kasan me Kamal?".Kamal kai ya girgiza.D'an juma kuma ya ce"Tsiwarta kyau take mata,ta kasa b'acemin a ido lokacin da takemin fad'a zan kadata"
Kamal kai ya girgiza,dan yaga abin banawasa ba ne ,k'arshema sai cewa yayi"Amma idan haka ne Abdurrahman yana da kyau ka samu soyayyarta kafin ta tafi".Kai d'an juma ya girgiza ya ce"Kamal bazata soni b ,kawai dai nina san tamin shigar sauri,tabbas na kamu da sonta lokaci guda,kuma so mai wahalar fita".
Kamal da sosai ya gaskata maganar d'an juma dan ko dan yanayin yadda yake magana kamar wani maraya yasan tabbas so yayi mai shigar sauri.Kamal kallan d'an juma yayi ya ce"Kuna magana da ita ne?".Kai d'an juma ya girgiya ya ce magana da ita bazata yuwuba,yarinyar miskilar gaske ce,kuma kamar tana da jida kai bisa ga alamunta".
"Tom duk da haka dai ni shawarar da zan baka ,karik'a musu alheri ita da 'yan'uwanta kafin su tafi,sannan bahaushe yace da rashin tayi akan bar arha,lokuta da dama muna ma mututa ne kallan halinda ba d'abiyar su bace sai ka zauna dasu zaka San haka,dan haka ina mai baka shawara ka gwada sa'arka k'ila kadace" .
D'an juma kallan Kamal yayi ya ce"Kana ganin zan iya da cewa?"."Sosai ma kuwa".Cewar Kamal.Ranar dai haka d'an juma ya wuni yana mai jin wata irin fargaba akanta,dan ko ajikin shi bayajin za ta so shi ,hasalima zuciyar shi gargad'in shi take karya sake ya furta kalmar so ga Meenal.Wata zuciyar kuma ta ce "Koma biki gargad'an ba nima bazan iya furtawa".
Haka dai d'an juma ya yi ta sak'arshi yana warware abin shi,kamar yadda ya saba tafiya gida gaf magriba yauma haka ya tafi,sai da ya biya ya sai mata fura,inda yaga d'azu ta siya ,sannan ya hau mashin d'in shi ya tafi".
WAYE D'AN JUMA?:
Mahaifin d'an juma mahaifiyar d'an juma ce uwar gidan shi,sai dai Allah yasa bata samu haihuwa da wuri ba,hakan yasa Sarki wato kakan d'an juma kasan cewar yana son ganin jikan shi yasa Mahaifin d'an juma k'ara aure,inda Mahaifin d'an juma ya k'ara auran badan yana soba,sai dai bayan auran su da Lami da wata goma ta haifi d'iya mace wato Rabi suna ce mata Yaya Rabi.Lami wato kishiyar Mahaifiyar d'an juma sai da ta haifi mata uku babu namiji aciki,hakan yasa Sarki yasa Mahaifin d'an juma k'ara aure ko za ahaifar musu Namiji.Cikin ikon Allah Maryama wato Mahaifiyar d'an juma da amaryar da Mahaifin d'an juma ya aura kusan atare su kai laulayin ciki,dan sati d'aya ne tsakanin su a haihuwa,inda ranar wata juma mahaifiyar d'an juma ta haifi d'a namiji,amaryar su kuma ta haifi mace.lokacin mahaifin d'an juma na da Yara biyar duk mata,hakan yasa Sarki da Mahaifin d'an juma suka rasa inda zasu sa Maryama wato Mahaifiyar d'an juma,tsabar murnar haihuwar Namiji da akai musu.Ranar sunan d'an juma yaci sunan Abdurrahman.Tom kunsan mutanan kyauye da rad'ama mutum sunan ranar da aka haife shi,dalilin ranar juma'a aka haifi d'an juma shine fa suka b'atar da da sunan shi suka rik'a Kiran shi da d'an juma.
Tun ranar sunan d'an juma aka fara cin karo da ban-banci,dan ko sarki ya kashe kud'in da bai tab'a kashe rabin su ba sauran jikokin da aka haifar mai .Haka Sarki da Mahaifin d'an juma suka d'auki son duniya suka d'orama d'an juma.D'an juma na yaro sosai akazo layin kad'anya akai gina musu primary School,tun ana ginin makarantar d'an juma ya kwallafa rai dan gani yake wani abunne,hakan yasa ana gama ginin Sarki da kan shi ya d'auki d'an juma ya kai shi.Allah kuma yasa d'an juma nada k'okari ,ahaka dai ya kammala aji shida,kasan cewar babu secondary agarin hakan yasa Sarki ya samar mai gurbin karatu a d'an dume dan babu nisa sosai tsakanin su,ahaka-ahaka dai d'an juma ya kammala secondary d'in shi,daga nan ne fa Sarki yace ba zai shigema kafuran nan da yawa ba dan haka ya isa hakanan karatun,dole d'an juma ya hak'ura badan yaso ba.Tom daga nan fa sai kuma ya fara zaman gida babu sana'a,gashi shi saboda Makaranta da yayi bai iya aikin gona ba.Sosai rashin sana'ar d'an juma ta fara damun Maryama,ana hakane Allah yayi ma Mahaifinta rasuwa,tom da aka rabamusu gado ne Maryama ta ba d'an juma ya bud'e provision, kusan babu abinda bai sai dawa .A funtua yake zuwa Sarin kaya,hakan yasa ya fara abokai,ahaka-ahaka dai suka saba da ogan nashi,ahankali-ahankali ya fara jawoshi jikin shi yana tsare mai kayan shi,shi kuma d'an juma shima can sai yayi yaro shima yana bashi tsaron nashi,tom inda d'an juna ke tsarewa plaza ce babba ba laifi.Abinda yasa yake b'oyema sarki gani yake kamar zai hana shi,shi yasa sarki bai San abinda d'an juma ke zuwa funtua yi ba kullum.
Layin kad'an ya Yaro d'an shekara goma sha bakwai,Shatakwa,ashirin suke aure, hakan yasa d'an juma ma tun yana matakin secondary suke bashi aure amma yak'i,atakaice dai har izuwa girman shi na cikakkan namiji .Wanna yasa akema d'an juma surutu sosai,dan wasu cewama suke k'ila aljana ce ta aurai.Shiko d'an juma tunda ya taso Allah yasa baida ra'ayin irin auran garin su,macan yarinya shima angon yaro.
Tunda d'an juma ya fara mallakar hankalin shi yafi buk'atar budurwa wadda tasan abinda takeyi ba kwaila ba irin na garin su.Wannan kenan"
D'an juma haka ya hawo mashin d'in shi ya dawo gida .
Meenal ko tun da ta farka daga bacin da tayi take neman wayar da zata Kira Daddaynta ta kai k'arar alhaji wato kakanta ,akan maganar shan addu'ar da ya ce sai ta sha, idan bata sha ba baza ta tafi ba.Wayar mommyonta ko tun jiya da tayi wurgi da ita ta d'auke, wayar mahaifiyar d'an juma kuma babu caji,hakan yasa ta rasa wayar da zatai kiran.
Meenal sosai take jinta atakure zaman kyauyan,dan ko abinci rana da Mahaifiyar d'an juma ta kawo musu k'in ci tayi.
Meenal kallan Mommynta ta yi, ta ce"Yanzu mommy da ban gama Exams ba haka mutunin nan zauzo nan kawai ya kama zaunar da muta ne,Allah ni dai kije ki mai magana,idan ba haka ba zaki nai man kirasa,dan ni daga gobe bazan k'ara kwana kyauyan nan ba,tun da nazo wayana baya aiki,inda ni M.T.N garan ,dan Alllahi nidai ki san yadda zaki Mommy Allah duka mutanan garin haushin su nakeji".Meenal dai har ta gama maganarta Mommynta bata tankamata ba,hakan yasa tayi shiru.
Meenal har dare tak'i cin komai kuma dama da daddaran tuwan gari akayi,ita kuma dama ba son shi take ba,nan fa yunwa ta fara damunta,dan ko sallar magriba da kyar tayi ,tana cikin sallar ne d'an juma ya shigo gidan,bai shiga d'akin ba daga waje ya gaida Mahaifiyar meenal sannan ya mik'ama mahaifiyar shi hurar da ya siyo ya ce"Inna gashi adamama mu su".
Hajiya Mariya cikin fad'ad'a fara'arta ta ce"Tom mun gode Allah yasaka da alkairi"
D'an juma fita yayi dan yin sallah Isha'i da ake kira,saboda ya k'osa yaje gidan Sarki yaji dangartakar dake tsakanin su da su Alhaji.
D'an juma masallacin k'ofar gidan su ya fara zuwa yayi sallar Isha'i sannan ya nufi gidan Sarki.Sai dai koda yaje badamar samun sanin abinda ya kawo shi dan Sarki fira suke da Alhaji sosai,bayan sun gaisa ne Alhaji wato kakan Meenal ya ce"Yauwa Abdurrahman dama yanzu zansa Malam Haruna ya kiraka,amma inda gaka kazo ai shikenan,maza kaje gidanku ka tafomin da Amina"."D'an juma tashi yayi ya fita yana mai jin dad'i zai kuma ganinta,yana tafiya zuciyar shi na ingiza shi da cewa" Ka gwada furta mata kallamar so mana ko zaka dace".Wata zuciyar ta ce"Gaskiya yaudarar kanka kawai kake,amma kaima kasan bazata amin ce ba".Can kuma sai ya ba kan shi amsa da "Darashin tayi akan bar arha,sosai d'an juma ya yadda da wanna kalma da hausawa ke cewa,hakan yasa cikin full Confidence ya idasa gidan su".
Meenal ko ta gama Shan furar da d'an juma ya kawo mata har tayi shirin bacci ta kwanta d'an juma ya yi sallama ya shiga d'akin.............✍️
Idan kin karanta ki Comment sister😗😗
📚 MEENALYN DADDY 📚
🔔📚
*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION📚*
_{Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa}_
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=337435884671992&id=103920888023494&sfnsn=mo
*⚜️©J.A.W📚🖌️*
Na
Fadila Sani Bakori.
page 12 & 13.
Meenal ko ta gama shan furar da d'an juma ya kawo mata har tayi Shirin bacci ta kwanta d'an juma ya yi Sallama ya shiga d'akin.
Mommyn meenal zaune ita da mahaifiyar d'an juma sai fira suke,d'an juma ya shiga.
D'an juma gaida hajiya Mariya yayi sannan ya ce"Dama alhaji ne ya ce in kira Meenal,kuma naga tama kwanta"."A'a ai ba bacci tayi bari in mata magana"cewar hajiya Mariya"