Sashe 3
Masarautar Mu Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Kasuwancin automobile din sa ma ya maido shi gida Nigeria ya dora Awaisu akan komai. Yanzu kuma da ya dawo sai ya hada da biyu daga cikin kannen sa wadanda suke gab da kammala karatun digiri akan kasuwanci, Suhail dan wajen Ya Kirjinoma da Ahmad kanin sa a dakin su.
An kai ruwa rana kafin Maimartaba ya yarjewa Yarima komawa Abuja da iyalin sa, don a tunanin sa da farko ya dawo Askira kenan don har ya fara shirin yi masa nadin sarautar Chiroma, amma sai Yarima ya zo da batun samun aikin sa da NTNU yana rokon Maimartaba alfarmar ya bar shi ya tafi, sai da Fulani Bilkisu ta sa baki sannan maimartaba ya amince don baya iya hanata kowacce alfarma ta nema, kuma Yarima ya zama dan gidan ta yanzu tun lokacin da Maimartaba ya damka mata amanar Sultana. Ya bar shi ya tafi da alkawarin duk bayan wata uku a gida zasu yi hutun kowanne karshen zangon karatu na jami'a.
Ranar wata Lahadi Yarima Sagir da maidakinsa Aisha-Sultana suka tattara suka koma Birnin tarayyah. Humaira da Naja'atu da sauran kannen sa maza ne suka yi masu rakiya, basu dawo ba sai da suka taya su suka shirya gidan su tsaf wanda Jami'ar NTNU ta baiwa Yareema Sagir cikin jerin gidajen malaman Jami'ar.
Jami'ar NTNU mallakar Turkawa ce (Turkish University) da suka bude a kasar Nigeria, suna biyan malamansu sosai a matsayin ta na (private international university) ko kusa ba daya take da jami'o'in Arewacin Nigeria ba wajen biyan malamai.
Haka gidajen malaman jami'ar dole tsarin su ya burge ka. Flat ne hawa daya mara girma sosai, dakuna ciki hudu, kitchen da bandaki a kowanne dakin barci, tafkeken falo da bangaren cin abinci (dining) sannan akwai garden daga bayan kowanne gida, daga gaban gidajen kuma balcony ne domin shan iska da yamma, akwai rumfar gargajiya (hut) a cikin gate din kowanne gida wadda aka zuba kujerun roba da gadon shan iska na Turkawa, gabadaya ginin daga na jami'ar har na gidajen malaman an dauko tsarinsa da sample dinsa daga Istanbul ne, duka gidajen iri daya ne sun kai guda 100 a cikin jami'ar.
Su Humaira suka dawo gida suna ta santin gidan Yayan su Yarima (Dr. Sagir Yusuf Askira) sunan da Jami'ar ta mayar masa, da alwashin zuwa hutu duk sanda suka samu hutu domin ba laifi Aisha - Sultana tana da kirki ga kowa nasa, daga auren zuwa yanzu ta saba da daukacin kannen Yarima na sauran dakunan matan sarki, banda 'yan dakin Ya Gumsu. Tun bata fahimta ba sabida rashin jin yaren hausa dana kanuri har zuwa yanzu ta fahimci Ya Gumsu bata yi na'am da ita a matsayin surukarta ba. Da suka je mata sallama ma zasu taho abuja ko kallon ta bata yi ba, haka tace da Yarima cikin fushi "tattara wannan danyen naman ku bar min sassa tun ranka bai baci ba".
Ba wai ta ji me Ya Gumsu ta ce bane amma ta fahimci ba maganar arziki bace duk da Yarima bai nuna komai akan kyakkyawar fuskarsa a lokacin da ta yi maganar ba, baya ga cewa da yayi da ita ta tashi su koma gida dare yayi.
Satin su guda itama ta fara neman aiki da (Insurance Brokers) kasancewar tattalin arziki ta karanta, Yarima ya samar masu kuku da mai gyaran gida duka kabilu, ba'a jima ba kuwa suka dauke ta, sai ya zamo daga shi har ita ba mazaunin gida, a lokacin ne Yarima yayi wani aboki dan kasar Turkey wanda yana cikin masu ruwa da tsaki na jami'ar sunan sa Dr. Ziyad, zasu yi shekaru daya kuma a tsangaya daya suke koyarwa. Tun haduwar Sageer da Dr. Ziyad abubuwa suka kara canzawa Yarima, domin Dr. Ziyad fitinanne ne na karshe kuma shi ba shi da mata, gidan sa babu nisa da gidan Yarima don haka lokuta da dama suna tare, suyi yawo cikin gari ko su debo 'yammata gidan Dr. Ziyad,
A haka suke rayuwar shi da Sultana kowa yana sha'anin gaban sa, don so suna son juna har gobe amma rashin albarkar uwa ya hana auren gamsar da kowannen su ba tareda sun san hakan ba.
Itama tunda ta waye da rayuwar Abuja shikenan ta koma harkokin ta na baya, bata kara tuna wani abu wai shi musuluncin data karba ba, shaye-shaye take na fitar hankali, data gane inda ake sayar da giya a Abuja kuwa shikenan kakarta ta yanke saka. Ta san halin Yarima akan 'giya' don haka bata taba gigin shigowa da ita gidan ba, kullum ta taso aiki sai ta tsaya a Bar ta sha mai isar ta, ta yo guzurin kayan mayen ta kala-kala sannan zata dawo gida, tana riga shi dawowa sau tari domin Dr. Sagir yafi fixing laccar yamma ga daliban sa, tana shigowa kai tsaye dakin barcin ta take nufa ta zube a kasa ko a gado tayi ta barci, har sai ya dawo ya tasheta da kan sa ya ce ta yi sallah.
Wannan itace kalar rayuwar Yarima da matarsa Aisha Sultana a birnin tarayyah, Abuja. Rayuwar da kowanne ya zabawa kansa. A haka lokaci ya cigaba da mikawa. Abinda Yarima bai sani ba tun dawowarsu Abuja da sati daya, Aisha-Sultana ta je an juya mata mahaifa.
*****
BAYAN SHEKARA BIYU!
Yau ne daliban El-Kanemi College of Islamic Theology suka kammala rubuta final paper din su ta barin makarantar sakandire wato SSCE wadda ta kasance darasin addinin muslunci (islamic studies). Farin cikin dake zukatan su ba zai bayyanu ba, fuskar Sa'adatu Hashim tafi ta kowa yalwar far'a, ta yi dakacen wannan rana inama da Rahima Kyari! Sun yi hotuna na tarihi kala-kala da kawayen ta da abokan arziki da suka yi zaman aminci tare. Babban farin cikin SA'ADE shine Alanguburo yayi mata alkawarin karatu a jami'ar Turkawa dake Najeriya (Nigerian Turkish Nile University) muddin ta fiddo da 9 credits, kuma daga yadda ta rubuta kowacce paper tana da kyakkyawan zato akan kokarin ta.
Humaira ta gama makaranta shekaru biyu baya, yanzu haka tana jami'ar Maiduguri. Da suka iso gida yau ta yi abinda bata taba yi ba a tsayin rayuwar ta (without minding the consequence); a guje ta shiga sassan su tana kwalawa Fulani kira, Fulani bata san hawa ba bata san sauka ba tana tsaye tana yi wa little Zarah fada taji anyi wuf! Da ita an kankameta a tsakar dakin. Dama ga ta babu kiba ko kadan. Saura kadan ta sha kasa "I have finally graduated Fulani, i've really -really made it!".
Kokarin banbare Sa'ade take daga jikin ta kada wani ya shigo ya gansu a haka, yayin da Little Zarah ke ta kyalkyala dariya cike da murnan ganin Sa'aden, ta tafi itama ta rungume su, Sa'ade ta saki Fulani da ke ta banbamin fadan so take ta karya ta? Ta russuna ta dauki Zarah tana rada mata cikin kunnen ta "na taho miki da choculates mai dadi" Zarah ta ce "bazamu san wa Fulani ba tunda tana yi miki fada" a haka suka shige dakin Sa'aden wanda Fanna ta gyare tsaf. Ta sanya turaren wuta irin nasu. Don tana da masaniyar yau ne graduation din Sa'adatun.
Sa'adatu Hashim dalibar El-Kenemi, doguwa ce sosai, mai kirar jiki na bare-barin usli, wadanda suka hadu da shuwa suka haifeta, suka bata colour din fata mai kyau da daukar ido. Doguwa sambaleliya tamkar kirar matan Saliyon, a yanzu ne take cikin shekaru goma sha takwas komai nata ya kai ya kawo, cikakkiyar budurwa mai wani irin class na daukar hankali.
Duka wadannan Fulani Bilkisu ta nazarce su ne a lokacin da Sa'ade ta dauki Zarah suka bata baya zuwa dakin Sa'aden, ta bisu da kallo cike da kauna tana jin wata irin soyayyarsu su a zuciyar ta, a yanzu kam ta saduda, ta tabbata ta kuma haqqaqe tana son 'yar ta, kwatankwacin ko ma fiyecda yadda ta ke son Fatima-Zarah.
Ta koma cikin hamshakiyar kujerar falon ta ta zauna, ta lumshe idon ta a hankali, yayin da tunanin shekaru goma sha tara a baya na yadda ta samu 'yar, ya soma rewinding filla-filla a cikin kanta.....
****
An kai ruwa rana kafin Maimartaba ya yarjewa Yarima komawa Abuja da iyalin sa, don a tunanin sa da farko ya dawo Askira kenan don har ya fara shirin yi masa nadin sarautar Chiroma, amma sai Yarima ya zo da batun samun aikin sa da NTNU yana rokon Maimartaba alfarmar ya bar shi ya tafi, sai da Fulani Bilkisu ta sa baki sannan maimartaba ya amince don baya iya hanata kowacce alfarma ta nema, kuma Yarima ya zama dan gidan ta yanzu tun lokacin da Maimartaba ya damka mata amanar Sultana. Ya bar shi ya tafi da alkawarin duk bayan wata uku a gida zasu yi hutun kowanne karshen zangon karatu na jami'a.
Ranar wata Lahadi Yarima Sagir da maidakinsa Aisha-Sultana suka tattara suka koma Birnin tarayyah. Humaira da Naja'atu da sauran kannen sa maza ne suka yi masu rakiya, basu dawo ba sai da suka taya su suka shirya gidan su tsaf wanda Jami'ar NTNU ta baiwa Yareema Sagir cikin jerin gidajen malaman Jami'ar.
Jami'ar NTNU mallakar Turkawa ce (Turkish University) da suka bude a kasar Nigeria, suna biyan malamansu sosai a matsayin ta na (private international university) ko kusa ba daya take da jami'o'in Arewacin Nigeria ba wajen biyan malamai.
Haka gidajen malaman jami'ar dole tsarin su ya burge ka. Flat ne hawa daya mara girma sosai, dakuna ciki hudu, kitchen da bandaki a kowanne dakin barci, tafkeken falo da bangaren cin abinci (dining) sannan akwai garden daga bayan kowanne gida, daga gaban gidajen kuma balcony ne domin shan iska da yamma, akwai rumfar gargajiya (hut) a cikin gate din kowanne gida wadda aka zuba kujerun roba da gadon shan iska na Turkawa, gabadaya ginin daga na jami'ar har na gidajen malaman an dauko tsarinsa da sample dinsa daga Istanbul ne, duka gidajen iri daya ne sun kai guda 100 a cikin jami'ar.
Su Humaira suka dawo gida suna ta santin gidan Yayan su Yarima (Dr. Sagir Yusuf Askira) sunan da Jami'ar ta mayar masa, da alwashin zuwa hutu duk sanda suka samu hutu domin ba laifi Aisha - Sultana tana da kirki ga kowa nasa, daga auren zuwa yanzu ta saba da daukacin kannen Yarima na sauran dakunan matan sarki, banda 'yan dakin Ya Gumsu. Tun bata fahimta ba sabida rashin jin yaren hausa dana kanuri har zuwa yanzu ta fahimci Ya Gumsu bata yi na'am da ita a matsayin surukarta ba. Da suka je mata sallama ma zasu taho abuja ko kallon ta bata yi ba, haka tace da Yarima cikin fushi "tattara wannan danyen naman ku bar min sassa tun ranka bai baci ba".
Ba wai ta ji me Ya Gumsu ta ce bane amma ta fahimci ba maganar arziki bace duk da Yarima bai nuna komai akan kyakkyawar fuskarsa a lokacin da ta yi maganar ba, baya ga cewa da yayi da ita ta tashi su koma gida dare yayi.
Satin su guda itama ta fara neman aiki da (Insurance Brokers) kasancewar tattalin arziki ta karanta, Yarima ya samar masu kuku da mai gyaran gida duka kabilu, ba'a jima ba kuwa suka dauke ta, sai ya zamo daga shi har ita ba mazaunin gida, a lokacin ne Yarima yayi wani aboki dan kasar Turkey wanda yana cikin masu ruwa da tsaki na jami'ar sunan sa Dr. Ziyad, zasu yi shekaru daya kuma a tsangaya daya suke koyarwa. Tun haduwar Sageer da Dr. Ziyad abubuwa suka kara canzawa Yarima, domin Dr. Ziyad fitinanne ne na karshe kuma shi ba shi da mata, gidan sa babu nisa da gidan Yarima don haka lokuta da dama suna tare, suyi yawo cikin gari ko su debo 'yammata gidan Dr. Ziyad,
A haka suke rayuwar shi da Sultana kowa yana sha'anin gaban sa, don so suna son juna har gobe amma rashin albarkar uwa ya hana auren gamsar da kowannen su ba tareda sun san hakan ba.
Itama tunda ta waye da rayuwar Abuja shikenan ta koma harkokin ta na baya, bata kara tuna wani abu wai shi musuluncin data karba ba, shaye-shaye take na fitar hankali, data gane inda ake sayar da giya a Abuja kuwa shikenan kakarta ta yanke saka. Ta san halin Yarima akan 'giya' don haka bata taba gigin shigowa da ita gidan ba, kullum ta taso aiki sai ta tsaya a Bar ta sha mai isar ta, ta yo guzurin kayan mayen ta kala-kala sannan zata dawo gida, tana riga shi dawowa sau tari domin Dr. Sagir yafi fixing laccar yamma ga daliban sa, tana shigowa kai tsaye dakin barcin ta take nufa ta zube a kasa ko a gado tayi ta barci, har sai ya dawo ya tasheta da kan sa ya ce ta yi sallah.
Wannan itace kalar rayuwar Yarima da matarsa Aisha Sultana a birnin tarayyah, Abuja. Rayuwar da kowanne ya zabawa kansa. A haka lokaci ya cigaba da mikawa. Abinda Yarima bai sani ba tun dawowarsu Abuja da sati daya, Aisha-Sultana ta je an juya mata mahaifa.
*****
BAYAN SHEKARA BIYU!
Yau ne daliban El-Kanemi College of Islamic Theology suka kammala rubuta final paper din su ta barin makarantar sakandire wato SSCE wadda ta kasance darasin addinin muslunci (islamic studies). Farin cikin dake zukatan su ba zai bayyanu ba, fuskar Sa'adatu Hashim tafi ta kowa yalwar far'a, ta yi dakacen wannan rana inama da Rahima Kyari! Sun yi hotuna na tarihi kala-kala da kawayen ta da abokan arziki da suka yi zaman aminci tare. Babban farin cikin SA'ADE shine Alanguburo yayi mata alkawarin karatu a jami'ar Turkawa dake Najeriya (Nigerian Turkish Nile University) muddin ta fiddo da 9 credits, kuma daga yadda ta rubuta kowacce paper tana da kyakkyawan zato akan kokarin ta.
Humaira ta gama makaranta shekaru biyu baya, yanzu haka tana jami'ar Maiduguri. Da suka iso gida yau ta yi abinda bata taba yi ba a tsayin rayuwar ta (without minding the consequence); a guje ta shiga sassan su tana kwalawa Fulani kira, Fulani bata san hawa ba bata san sauka ba tana tsaye tana yi wa little Zarah fada taji anyi wuf! Da ita an kankameta a tsakar dakin. Dama ga ta babu kiba ko kadan. Saura kadan ta sha kasa "I have finally graduated Fulani, i've really -really made it!".
Kokarin banbare Sa'ade take daga jikin ta kada wani ya shigo ya gansu a haka, yayin da Little Zarah ke ta kyalkyala dariya cike da murnan ganin Sa'aden, ta tafi itama ta rungume su, Sa'ade ta saki Fulani da ke ta banbamin fadan so take ta karya ta? Ta russuna ta dauki Zarah tana rada mata cikin kunnen ta "na taho miki da choculates mai dadi" Zarah ta ce "bazamu san wa Fulani ba tunda tana yi miki fada" a haka suka shige dakin Sa'aden wanda Fanna ta gyare tsaf. Ta sanya turaren wuta irin nasu. Don tana da masaniyar yau ne graduation din Sa'adatun.
Sa'adatu Hashim dalibar El-Kenemi, doguwa ce sosai, mai kirar jiki na bare-barin usli, wadanda suka hadu da shuwa suka haifeta, suka bata colour din fata mai kyau da daukar ido. Doguwa sambaleliya tamkar kirar matan Saliyon, a yanzu ne take cikin shekaru goma sha takwas komai nata ya kai ya kawo, cikakkiyar budurwa mai wani irin class na daukar hankali.
Duka wadannan Fulani Bilkisu ta nazarce su ne a lokacin da Sa'ade ta dauki Zarah suka bata baya zuwa dakin Sa'aden, ta bisu da kallo cike da kauna tana jin wata irin soyayyarsu su a zuciyar ta, a yanzu kam ta saduda, ta tabbata ta kuma haqqaqe tana son 'yar ta, kwatankwacin ko ma fiyecda yadda ta ke son Fatima-Zarah.
Ta koma cikin hamshakiyar kujerar falon ta ta zauna, ta lumshe idon ta a hankali, yayin da tunanin shekaru goma sha tara a baya na yadda ta samu 'yar, ya soma rewinding filla-filla a cikin kanta.....
****