← Book details Masarautar Mu Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 22

Sashe 18

Masarautar Mu Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read

A da, na sanya kwanaki uku auren Yarima da Sa'adatu, don in samu inyi gayyata, to na fasa yanzu, nida Waziri zamu daura auren yau Juma'ah bayan sakkowa masallaci. Don in nuna miki ni ke da iko daku daga ke har dan naki. Gara ke na baki hakkin ki na uwa na sanar miki... shikuwa saidai ya ji labari......".
Yana gama fadin haka yasa kai ya fice fadar da bai yi niyyar fita yau ba.
Waziri sai ganin maimartaba yayi yana shigowa fada a matukar fusace, shikadai yake iya gane fushin mai Askira. Kyawun fuskarsa da kamalarsa kan boye fushin sa a yawancin lokuta.
Yana zama fadawa suka yi kirari suka kuma basu wuri, don sun lura ya shigo fada ne kawai sabida Wazirin sa Ibrahim.
"Ka fadawa 'King-makers' akwai daurin auren Yarima bayan sakkowa daga masallaci yau".
Waziri yayi kabbara a fili, don ya dade yana jiran ranar da Askirama zai zo masa da zancen karin auren Yarima, yana daga wasu daga cikin labaran halin da rayuwar auren Yarima ke ciki daga abakin Awaisu, hatta zancen cire mahaifa da Aisha -Sultana ta yi ya sani, bai gayawa mai Askira bane don ya san in rashin jikoki ya ishe shi da kan shi zai magantu.
"Amma Allah ya taimakeka baka ganin gara a hada masa guda uku a wanke su rana daya a kai masa? Hakan taimako ne babba gare shi a bisa nazari na na halin da yake ciki, kamar guda daya ta yi masa kadan".
Askirama yayi murmushi ya dubi Waziri Ibrahim, "wannan daya ce tamkar da goma! Kuma itace maganin matsalolin Yarima insha Allahu. Tun farko ita naso ya aura ya kawo min zancen baturiyar nan, idan har ta fito daga cikin Bilkisu ina tabbatar maka karamar Bilkisu ce.....da ace Bilkisu na fara aure a rayuwata babu macen da zan kara aure".
Waziri Ibrahim bai san sanda yayi dariya ba, yau mai Askira ya saki layi sabida soyayyar Fulani Bilkisu, ya manta ko da wa yake magana....
A take ya dau waya ya fara aiwatar da umarnin sarki.
Kafin karfe 2 na rana duk wani da ya kwana ya tashi a garin Askira mace ko namiji ya samu gayyatar daurin auren Yarima Sageer da Sa'adatu, banda Sa'aden da uwarta dake kule kowacce a dakin ta zuciya babu dadi, ita Sa'ade halin da ta ga Fulani a ciki ne ya hanata kwanciyar hankali, tun jiya data shige daki ta rufe bata kara fitowa ba, sannnan daga ita har Fanna da Zarah tace bata bukatar ganin kowa. Abinci ma tace bata bukata tanada cake da friuts a firjin gefen gadon ta.
Duk tunanin Sa'ade yafi bata matsala suka samu tsakanin ta da Askirama.
Wajejen karfe daya Fanna ta shigo ta samu Sa'ade dake kwance a gado tun safe, waya take da Sa'id yana gaya mata yadda garin Abuja ya zame masa boring saboda rashin ta, maimakon tayi dariya ta bashi amsa cikin raha yadda suka saba sai tace "Sa'id, ina cikin damuwa, mamana ta shige daki ta kulle tun jiya tace kada wani daga cikinmu ya je inda take" Sa'id yace "manya kanyi irin wannan a lokacin da suke so su kebe don su samu suyi tunani ko neman mafita kan wani mhimmin al'amari da ya shafe su, so karki damu tunda kinsan lafiyar ta kalau, ita da kanta in ta samu saukin al'amuranta zata neme ku......." Fanna ta ce "ranki ya dade....ranki ya dade!" Ta cire wayar daga kunnen ta ta dubi Fanna, Fanna ta ce "lokacin sallah ya yi, ga kuma abincin ki". Sa'ade ta yamutsa fuska ta ce "maida abincin nan" "me yasa bazaki ci ba?" Inji Fanna cikin damuwa, uwa ta ki ci, 'yar ma tun safe ta ki cin komai duk sun sa ta a damuwa....Lokacin yayi daidai da bugawar dakikar agogo karfe biyu da rabi na rana, ya tafi tare da bugun zuciyar SA'ADE.... ba tareda ta sani ba, ta zama karkashin igiyoyin Yareema Sageer har guda uku.
"An daura auren Yarima Sageer Yusuf Askira da Sa'adatu Hashim Askira akan sadaki lakadan ba ajalan ba.....". Abinda Fanna ta ji kenan data sako kafarta a kitchen don dawo da kayan abincin da Sa'ade ta ki ci, amma bata yarda tasu Sa'adatun bace don wani abu makamancin wannan bai taba zuwa mata a rai ba, Yarima mijin baturiya wacece zata yi gigin shiga gidan sa? Ai sai mai tsautsayi, matar da aka ce har kwalba take dagawa. Don haka ta tausayawa koma wacece wannan Sa'adatun da aka aurawa Yarima. Don daula zata samu zata shigeta iya shiga....amma tabbas ta hadu da gamon ta.
Abinda Fanna ke ta fada a ranta kenan tana cigaba da ayyukan ta a kicin.

Yarima yana dakin Awaisu na gidan Waziri a wannan lokacin, shima Awaisun ya zo sakamakon kiran gaggawa da Waziri yayi masa. Ya kuma gaya masa ko me kenan amma yace kada ya bari Yarima ya sani har sai an gama daurin aure, mai martaba zai gaya masa da kansa.
Awaisu, kamar zai suma don dadi da farin cikin jin wadda aka zabawa Yarima, once or twice, Yarima ya taba yi masa maganar Sa'ade, yace ta iya girki sannan ga ta da hankali. Daga wannan bai kara cewa komai akan ta ba. Ya tabbata ko baya son ta zai karbeta tunda har yana yabon ta, sannan uwarta mutuniyar sa ce (Fulani Bilkisu). Bazai bada mata kasa a ido ya ce baya son 'yar data fito daga hannun ta ba. Yarinyar kawai yake tausayawa zama da Sultana amma zai nemi Yarima da ya raba musu gida don a zauna lafiya.
Shi dai Yarima ya ga Awaisu sai shiri yake cikin farar shadda excelcior, yana yi yana bin waka a radio da alama cikin nishadi yake, ya ce Asiya tana jirana a cikin gida don haka na sallameka inada daurin aure a fada inna gama da ita". Yarima ya kulu da wannan kora da Awaisu yayi masa yace "ni kake kora? Daurin auren wa?" ALLAH ya taimaki Yarima wane ni in kore ku! Amma don Allah ka kara gaba ko in bar maka mukullin dakin in ka gama hirar ka rufe, inada daurin aure muhimmi". Daga haka ya sanya hularsa da takalmi ya fesa turare, ya dubi Yarima yana murmushi ganin kallon takaicin da yake masa.... dariya yayi a rans yace ka kuma zama namiji malam, a da muna maza ne tunda mai jan kunne kake aure, yanzu ne zaka san ka yi aure da matan usli da suka amsa sunan mata....
Yayi ficewar sa ya barshi kwance a gadon sa da baki sake, yana mamakin Awaisu ne yau yayi masa wannan wulakancin? Daurin auren da zai je ya fi shi Sageer muhimmanci???
****
Chapter 18 · 0% Book details