Sashe 2
Bawan Allah Part 1 Compleete Hausa Novel · about 8 min read
Abdallah da Umar suna iyakar bakin k'ok'arin su wajen ganin sun ciyar da iyayen su amma abin yana fin k'arfin su wataran gwanda ma Umar mahaifin shi da aka raba gado Maman shi ta fara sana'ar k'ulla-k'ulle dashi suke rufa ma Kansu asiri
Lokuta da yawa Malam Kabiru yana musu nasiha akan suji tsoron Allah kada talauci ya sa su rasa imanin su da irin wad'an nan nasihohin kullum Malam ke musu
Da temakon Malam suka samu koyar wa a wata islamiya da ke wata unguwa babbar makaranta ce sai dai albashin ta mai K'aranci ne baya isarsu d'awai niyar su
Wannan shine BAWAN ALLAH kamar yadda mahaifiyar shi me kiran shi dan bats fad'in sunan sakamakon sunan mijin ta kuma sunan d'anta na fari
For comments
08165728746
[12/13/2017, 5:36 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*
*MRS NN ONE💋*
*I dedicated this page to you , masoyana a koda yaushe ina jin dad'in yadda kuke k'arfafamin gwaiwa na Gode Allah ya bar k'auna AMEERT Nd FATIMA (K'awwali)❤*
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
# [email protected]
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
Page 3⃣
*CIGABAN LABARI*
Haka suka k'araci zaga gurare da kasuwwani ba su samu komai ba har la'asar ta gabato , hakan ya sasu koma wa gidan ba Dan sun so ba ,
Da sallama ya shiga gida Mama da hafsa ne suke hirarsu jefi-jefi , suka amsamai sallamar ne ya shiga
Cikin sanyin jiki ya nemi guri gefe ya zauna sannan ya juya ya kalli mahaifiyar sa ya ce
"Kun wuni lafiya Mama?"
"Lafiya lau ya k'ok'ari bawan Allah?" Ta kalli D'an nata cike da tausaya wa
"Alhamdlillah Mama" cewar Abdallah daya ke k'ok'arin tashi , domin kiran sallar da yaji ,
Bayan sunyi sallah shi da aminin nashi islamiyar da suke koyar wa suka je ,
Abdallah shine malamin k'ur'an da tajweed ,
Umar kuwa yana daukan ahdari da tauheed
Suna zuwa kowa yake shiga ajin shi
Bayan sun dawo daga islamiya k'arfe takwas na dare suke zuwa d'aukar karatu wurin Malam Kabiru ,
Yauma kamar kullum sunje karatu Malam ke musu fad'a
" wai yanzun Ku haka zaku zauna ba zaku yi aure ba Ai aure shike sa aga mutum da daraja kullum"
"Insha Allahu idan lokaci yayi za'a yi "cewar Umar
Shiko Abdallah shiru yayi
Malam ya ce "Bawan Allah baka ce komai ba "
Ajiyar zuciya Abdallah yayi sannan ya ce " yanzun Malam a yadda muke d'in nan wa zai d'auki d'iyar sa ya bamu , bayan bamu da abinda zamu ciyar da ita dashi balle kuma sauran buk'atu na duniya "
Malam ya ce "hakane Abdallah amma ai ba'a rasa na Allah"
"Hakane Malam " cewar Umar
"Kuma ni gashi har na fara nema muku aure Dan zaman Ku ahaka baya min dad'i "
Cikin sauri Umar yace " Malam kad'an yi hak'uri zuwa nan gaba kad'an"
Malam yayi murmushi ya ce "Allah ya kaimu "
Abdallah kuwa cewa yayi "duk yadda kayi Malam dai- dai ne"
Nan Malam ya sa musu albarka sannan suka tafi ,
Suna fitowa Umar ya kalli Abdallah ya ce
"Ustaz naga kamar kayi na'am da maganar Malam ne "
Kallon shi Abdallah yayi sannan ya ce " Malam tamkar Uba yake aguri na Dan haka babu zab'in da zai min na bijire masa dole Sana'a zannema "
Umar ya zaro ido"wace irin Sana'a kenan?"
" zanyi tunani idan na yanke shawara zan gaya maka zuwa gobe da safe" cewar Abdallah yana k'ok'arin shigewa gida
"Allah ya jisshemu alkhairi " Umar ya fad'a da D'an k'ar fi ,
Suka yi sallama kowa ya shige gida
*DA SAFE*
Yauma kamar kullum ba komai agidan suna zaune sai ruwa da suke D'an sha jefi-jefi ,
Shiko Abdallah yana can d'akin shi kwance kan shamulokin katifar shi yana ta tunanin sana'ar k'arfin da zaiyi , idan yace wannan ya ce A'Ah daga k'arshe dai ya yanke shawarar yin sana'ar wanki da guga , wannan shawarar ya tsayar Dan haka ya mik'e ya saka rigar shi ya fita tsakar gida
Bayan sun gaisa ne sai ga Umar ya shigo da kwanon sha , a hannun shi ya d'ire a gaban Mama ,bayan sun gaisa Mama tace
"Umar me muka samu ne?"
"Murmushi yayi yace "koko ne Mama "
Mama tace "an gode Allah ya saka da alheri"
"Amin " dukkan su suka ce
Bayan sun gama shan kokon ne Umar yace " Abdallah wai wace Sana'a zamu fara ne"
Abdallah yayi gyaran murya yace "wanki da guga"
Umar ya zaro manyan idanun nan nashi ya ce "wanki da guga?"
"Eh, Kasan dalilin da ya sa na zab'e ta?"
Umar yace "A'ah"
"Saboda ita kad'ai ce samu yi ba tare da mun kashe ko sisi ba "
"Hakane Abdallah Allah ya taimake mu "
Dukan su suka amsa da "Amin"
Mama ma fatan alheri ta musu ,
Cikin sa'a kuwa suka samu kasuwa , da yake gidan su Abdallah akwai rijiya kuma ba yara nan suke taruwa suyi sana'ar su ,
Da yake basu sa ha'inci a sana'ar suba hatta masu hannu da shuni na kewayen su suna kawo musu ,
Hafsa ce zaune tana tsintar wake zata dafa musu garau-garau , nan k'awarta Ummi ta shigo tare da sallama , Ummi akwai ta da son barkwanci ta cewa hafsa
"Ah k'awata yaushe aka fara shiga kitchen?"
Wata harara hafsa ta aika wa Ummi sannan ta ce "kefa 'yar rainin wayau ce wallahi yau kika fara ganina nayi girki?"
Ummi tayi dariyar mugunta tace "to aike hafsa abinshi naki ne na ganin dama sai Mama tace kiyi kike yi"
Hafsa ta tuntsire da wata dariya tace " kamar ko kin sani"
Suka tafa Ummi tace "AI na sanki ne k'awata, ina Mama ,"
Hafsa tace "Mama taje gidan su yata Umar Gwago ce bats jin dad'i"
"Subhanallah Allah ya bata lafiya "cewar Ummi
Hafsa ta amsa da "amin"
Nan Ummi ta taya ta suka gama sukayi shirin islamiyya
[12/14/2017, 9:58 AM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*
*MRS NN ONE💋*
*Dedicated to Rabi'atu Baba Paki😘 ina yinki mumcy irin dayawa d'in nan*
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
# [email protected]
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
4⃣
Lokaci ya ja su Abdallah nayin wankin da guga suna samun na rufin asirin su , daga baya wani k'anin MAMAN Umar ya saman ma Umar tsaran shagon abokin shi acikin kasuwa , to daga nan Umar ya bar wanki da guga sai Abdallah kad'ai keyi , da haka idan ya cire kud'in da zasu CI abinci sai ya saka sauran a asusu saboda wasu idan yayi musu aiki over payment suke mishi,
Yanzun watan Abdallah shida yana wanki da guga wata , wata rana Malam ya aika a Kira shi , bai b'ata lokaci ba ya je,
Bayan sun gaisa Malam ya ce" Abdallah ya maganar aure?"
Wata irin muguwar fad'uwar gaba yaji amma sai ya d'aure ya ce"yanzun Malam akwai Wanda zai iya bani 'yarsa na aura yadda nake d'in nan?"
Malam yayi murmushi yace "sosai ma kuwa Dan an dad'e ma da baka sadaki kwai ake jira a d'aura aure"
Cikin firgici Abdallah ya d'ago ido ya kalli Malam
Malam yace " sosai ma kuwa idan kana da naira dubu bakwai ka kawo amatsayin sadaki , "
Gaba d'aya Abdallah ya diri-rice ya rasa me zai ce ,
Malam yace cikin sanyi murya "Abdallah dalilin da yasa na matsu kayi aure shine na dad'e ina lura da yanayin ka , sannan kuma ahalin yanzun da kake cike kana buk'atar mace ta gari da zata zamo natsuwa a gareka shiyasa kaga na damu"
Ajiyar zuciya Abdallah yayi Dan yasan zancen Malam gaskiya ne "Insha Allah bazai gagara ba , nagode Malam Allah ya saka da alkhairi ya k'ara girma "
"Amin "cewar Malam
Sannan sukayi sallama akan zai kawo sada kin gobe ,
Abdallah na koma wa gida ya sanar ma da Mama yadda suka yi da Malam , tayi murna sosai hafsa na d'aki na kwance ta fito tana "Mama lafiya?",
Abdallah ya turb'une fuska alamar be son raini yace" ke waye sa'anki a nan? dallah can koma d'aki"
"Haba Bawan Allah wannan ba 'yar uwar ka bace ai ya chanchanci taji abin alherin da yake shirin samun mu"
"Mama ni dai raini ne bana so" yana gama fad'in haka ya nufi k'ofar d'akin shi ya tura ya shiga ya fad'a kan shamulokin katifar shi yana tunani ,
"Shin ta ina za'a kawo wani mahaluki d'akin nan ya iya zama , ballan tana kuma Amarya?"
Mik'e wa yayi zaune yace "ya Allah ga Bawan ka nan mak'ask'anci daga cikin bayin ka ya Allah ka taimake mu ya Allah kafi kowa sanin halin da muke ciki " wasu k'walla masu zafi da tuk'uk'i a zuciya suka zubo mai ,
Da k'yar ya had'iye wani Abu mai kama da dutse a wuyan shi ya koma ya kwanta ,
Chan kuma yayi zumbur ya mik'e ya nufi gana most go d'in kayan shi ya ciro wani gwangwani , nan ya bud'e kud'i ne a ciki , nan ya hau k'irgawa , naira dubu takwas da d'ari biyar ne , ajiyar zuciya yayi sannan ya mai da kud'in ya ajiye , da yamma bayan sun had'u da Umar a islamiyya yake gaya mishi yadda suka yi da Malam
Umar sai da yayi dariya mai isarsa sannan ya ce " wato kai yanzun aure za'a maka ?, auren ma na dole"ya k'ara k'yalk'yale wa da wata dariya har yana rik'e cikin shi
Abdallah da yaga abin na Umar da rainin wayau aciki kawai sai ya mik'e ya fice ya bashi wuri ,
Umar ya biyo shi yana "ustaz tsaya mana ya muna magana zaka gudu kuma"
Abdallah be kula shi ba sai ma ture hanun Umar da yayi a kafad'ar shi cikin fushi ya k'ara sauri,
Umar na ganin haka ya ce "yau maza sun yi fushi , sai naje biko"
Abdallah kuwa yana shiga afusace ba kowa a tsakar gidan sai wani bokiti da aka cika shi da ruwa aka aje ,
Lokuta da yawa Malam Kabiru yana musu nasiha akan suji tsoron Allah kada talauci ya sa su rasa imanin su da irin wad'an nan nasihohin kullum Malam ke musu
Da temakon Malam suka samu koyar wa a wata islamiya da ke wata unguwa babbar makaranta ce sai dai albashin ta mai K'aranci ne baya isarsu d'awai niyar su
Wannan shine BAWAN ALLAH kamar yadda mahaifiyar shi me kiran shi dan bats fad'in sunan sakamakon sunan mijin ta kuma sunan d'anta na fari
For comments
08165728746
[12/13/2017, 5:36 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*
*MRS NN ONE💋*
*I dedicated this page to you , masoyana a koda yaushe ina jin dad'in yadda kuke k'arfafamin gwaiwa na Gode Allah ya bar k'auna AMEERT Nd FATIMA (K'awwali)❤*
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
# [email protected]
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
Page 3⃣
*CIGABAN LABARI*
Haka suka k'araci zaga gurare da kasuwwani ba su samu komai ba har la'asar ta gabato , hakan ya sasu koma wa gidan ba Dan sun so ba ,
Da sallama ya shiga gida Mama da hafsa ne suke hirarsu jefi-jefi , suka amsamai sallamar ne ya shiga
Cikin sanyin jiki ya nemi guri gefe ya zauna sannan ya juya ya kalli mahaifiyar sa ya ce
"Kun wuni lafiya Mama?"
"Lafiya lau ya k'ok'ari bawan Allah?" Ta kalli D'an nata cike da tausaya wa
"Alhamdlillah Mama" cewar Abdallah daya ke k'ok'arin tashi , domin kiran sallar da yaji ,
Bayan sunyi sallah shi da aminin nashi islamiyar da suke koyar wa suka je ,
Abdallah shine malamin k'ur'an da tajweed ,
Umar kuwa yana daukan ahdari da tauheed
Suna zuwa kowa yake shiga ajin shi
Bayan sun dawo daga islamiya k'arfe takwas na dare suke zuwa d'aukar karatu wurin Malam Kabiru ,
Yauma kamar kullum sunje karatu Malam ke musu fad'a
" wai yanzun Ku haka zaku zauna ba zaku yi aure ba Ai aure shike sa aga mutum da daraja kullum"
"Insha Allahu idan lokaci yayi za'a yi "cewar Umar
Shiko Abdallah shiru yayi
Malam ya ce "Bawan Allah baka ce komai ba "
Ajiyar zuciya Abdallah yayi sannan ya ce " yanzun Malam a yadda muke d'in nan wa zai d'auki d'iyar sa ya bamu , bayan bamu da abinda zamu ciyar da ita dashi balle kuma sauran buk'atu na duniya "
Malam ya ce "hakane Abdallah amma ai ba'a rasa na Allah"
"Hakane Malam " cewar Umar
"Kuma ni gashi har na fara nema muku aure Dan zaman Ku ahaka baya min dad'i "
Cikin sauri Umar yace " Malam kad'an yi hak'uri zuwa nan gaba kad'an"
Malam yayi murmushi ya ce "Allah ya kaimu "
Abdallah kuwa cewa yayi "duk yadda kayi Malam dai- dai ne"
Nan Malam ya sa musu albarka sannan suka tafi ,
Suna fitowa Umar ya kalli Abdallah ya ce
"Ustaz naga kamar kayi na'am da maganar Malam ne "
Kallon shi Abdallah yayi sannan ya ce " Malam tamkar Uba yake aguri na Dan haka babu zab'in da zai min na bijire masa dole Sana'a zannema "
Umar ya zaro ido"wace irin Sana'a kenan?"
" zanyi tunani idan na yanke shawara zan gaya maka zuwa gobe da safe" cewar Abdallah yana k'ok'arin shigewa gida
"Allah ya jisshemu alkhairi " Umar ya fad'a da D'an k'ar fi ,
Suka yi sallama kowa ya shige gida
*DA SAFE*
Yauma kamar kullum ba komai agidan suna zaune sai ruwa da suke D'an sha jefi-jefi ,
Shiko Abdallah yana can d'akin shi kwance kan shamulokin katifar shi yana ta tunanin sana'ar k'arfin da zaiyi , idan yace wannan ya ce A'Ah daga k'arshe dai ya yanke shawarar yin sana'ar wanki da guga , wannan shawarar ya tsayar Dan haka ya mik'e ya saka rigar shi ya fita tsakar gida
Bayan sun gaisa ne sai ga Umar ya shigo da kwanon sha , a hannun shi ya d'ire a gaban Mama ,bayan sun gaisa Mama tace
"Umar me muka samu ne?"
"Murmushi yayi yace "koko ne Mama "
Mama tace "an gode Allah ya saka da alheri"
"Amin " dukkan su suka ce
Bayan sun gama shan kokon ne Umar yace " Abdallah wai wace Sana'a zamu fara ne"
Abdallah yayi gyaran murya yace "wanki da guga"
Umar ya zaro manyan idanun nan nashi ya ce "wanki da guga?"
"Eh, Kasan dalilin da ya sa na zab'e ta?"
Umar yace "A'ah"
"Saboda ita kad'ai ce samu yi ba tare da mun kashe ko sisi ba "
"Hakane Abdallah Allah ya taimake mu "
Dukan su suka amsa da "Amin"
Mama ma fatan alheri ta musu ,
Cikin sa'a kuwa suka samu kasuwa , da yake gidan su Abdallah akwai rijiya kuma ba yara nan suke taruwa suyi sana'ar su ,
Da yake basu sa ha'inci a sana'ar suba hatta masu hannu da shuni na kewayen su suna kawo musu ,
Hafsa ce zaune tana tsintar wake zata dafa musu garau-garau , nan k'awarta Ummi ta shigo tare da sallama , Ummi akwai ta da son barkwanci ta cewa hafsa
"Ah k'awata yaushe aka fara shiga kitchen?"
Wata harara hafsa ta aika wa Ummi sannan ta ce "kefa 'yar rainin wayau ce wallahi yau kika fara ganina nayi girki?"
Ummi tayi dariyar mugunta tace "to aike hafsa abinshi naki ne na ganin dama sai Mama tace kiyi kike yi"
Hafsa ta tuntsire da wata dariya tace " kamar ko kin sani"
Suka tafa Ummi tace "AI na sanki ne k'awata, ina Mama ,"
Hafsa tace "Mama taje gidan su yata Umar Gwago ce bats jin dad'i"
"Subhanallah Allah ya bata lafiya "cewar Ummi
Hafsa ta amsa da "amin"
Nan Ummi ta taya ta suka gama sukayi shirin islamiyya
[12/14/2017, 9:58 AM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*
*MRS NN ONE💋*
*Dedicated to Rabi'atu Baba Paki😘 ina yinki mumcy irin dayawa d'in nan*
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
# [email protected]
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
4⃣
Lokaci ya ja su Abdallah nayin wankin da guga suna samun na rufin asirin su , daga baya wani k'anin MAMAN Umar ya saman ma Umar tsaran shagon abokin shi acikin kasuwa , to daga nan Umar ya bar wanki da guga sai Abdallah kad'ai keyi , da haka idan ya cire kud'in da zasu CI abinci sai ya saka sauran a asusu saboda wasu idan yayi musu aiki over payment suke mishi,
Yanzun watan Abdallah shida yana wanki da guga wata , wata rana Malam ya aika a Kira shi , bai b'ata lokaci ba ya je,
Bayan sun gaisa Malam ya ce" Abdallah ya maganar aure?"
Wata irin muguwar fad'uwar gaba yaji amma sai ya d'aure ya ce"yanzun Malam akwai Wanda zai iya bani 'yarsa na aura yadda nake d'in nan?"
Malam yayi murmushi yace "sosai ma kuwa Dan an dad'e ma da baka sadaki kwai ake jira a d'aura aure"
Cikin firgici Abdallah ya d'ago ido ya kalli Malam
Malam yace " sosai ma kuwa idan kana da naira dubu bakwai ka kawo amatsayin sadaki , "
Gaba d'aya Abdallah ya diri-rice ya rasa me zai ce ,
Malam yace cikin sanyi murya "Abdallah dalilin da yasa na matsu kayi aure shine na dad'e ina lura da yanayin ka , sannan kuma ahalin yanzun da kake cike kana buk'atar mace ta gari da zata zamo natsuwa a gareka shiyasa kaga na damu"
Ajiyar zuciya Abdallah yayi Dan yasan zancen Malam gaskiya ne "Insha Allah bazai gagara ba , nagode Malam Allah ya saka da alkhairi ya k'ara girma "
"Amin "cewar Malam
Sannan sukayi sallama akan zai kawo sada kin gobe ,
Abdallah na koma wa gida ya sanar ma da Mama yadda suka yi da Malam , tayi murna sosai hafsa na d'aki na kwance ta fito tana "Mama lafiya?",
Abdallah ya turb'une fuska alamar be son raini yace" ke waye sa'anki a nan? dallah can koma d'aki"
"Haba Bawan Allah wannan ba 'yar uwar ka bace ai ya chanchanci taji abin alherin da yake shirin samun mu"
"Mama ni dai raini ne bana so" yana gama fad'in haka ya nufi k'ofar d'akin shi ya tura ya shiga ya fad'a kan shamulokin katifar shi yana tunani ,
"Shin ta ina za'a kawo wani mahaluki d'akin nan ya iya zama , ballan tana kuma Amarya?"
Mik'e wa yayi zaune yace "ya Allah ga Bawan ka nan mak'ask'anci daga cikin bayin ka ya Allah ka taimake mu ya Allah kafi kowa sanin halin da muke ciki " wasu k'walla masu zafi da tuk'uk'i a zuciya suka zubo mai ,
Da k'yar ya had'iye wani Abu mai kama da dutse a wuyan shi ya koma ya kwanta ,
Chan kuma yayi zumbur ya mik'e ya nufi gana most go d'in kayan shi ya ciro wani gwangwani , nan ya bud'e kud'i ne a ciki , nan ya hau k'irgawa , naira dubu takwas da d'ari biyar ne , ajiyar zuciya yayi sannan ya mai da kud'in ya ajiye , da yamma bayan sun had'u da Umar a islamiyya yake gaya mishi yadda suka yi da Malam
Umar sai da yayi dariya mai isarsa sannan ya ce " wato kai yanzun aure za'a maka ?, auren ma na dole"ya k'ara k'yalk'yale wa da wata dariya har yana rik'e cikin shi
Abdallah da yaga abin na Umar da rainin wayau aciki kawai sai ya mik'e ya fice ya bashi wuri ,
Umar ya biyo shi yana "ustaz tsaya mana ya muna magana zaka gudu kuma"
Abdallah be kula shi ba sai ma ture hanun Umar da yayi a kafad'ar shi cikin fushi ya k'ara sauri,
Umar na ganin haka ya ce "yau maza sun yi fushi , sai naje biko"
Abdallah kuwa yana shiga afusace ba kowa a tsakar gidan sai wani bokiti da aka cika shi da ruwa aka aje ,