← Book details Bawan Allah Part 1 Compleete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 1 OF 24

Sashe 1

Bawan Allah Part 1 Compleete Hausa Novel · about 8 min read

[12/12/2017, 5:59 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*

MRS NN ONE

*Bismillahir Rahmanirrahim*
Yaa Allah yadda ka bani ikon farawa lafiya Allah kasa na gama lafiya batare da na kauce hanya ba ALLAHUMMA amin

Bawan Allah labari ne da ke cike da tsantsar tausayi tawwakali talauci da kuma soyyaya wanda bawan Allah labarin wani matashine wan da iya yensa basu karfi yatashi shine ak'ark'ashin kulawar mahaifiyarsa, Ku biyoni domin jin ya labarin zai Kasan ce

® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*

_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_

# [email protected]
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com

Page1⃣

Zaune yake akan dakalin k'ofar gidan su ya jingina da jikin gini daganin alama yana cikin tsananin damuwa hakan yasa har wani yazo yaita sallama bai jishi ba sai da ya dafa kafad'ar sa sannan yace " Haba Abdallah wannan wani irin tunani ne ina ta sallama baka jini ba "

Wanda aka kira da Abdallah yace"uhum Umar kenan ba dole kaga ina tunani ba kafi kowa sanin halin da nake ciki dole nayi tunani "

"Hakane aboki na amma ya kamata ka rage Dan kar ka haifar wa kanka da wata matsalar "cewar Umar

"Ina k'ok'arin ragewa Umar abin ne yafi k'arfi na wallahi"

"Allah ka iya mana ka kawo mana mafita"

"Amin" cewar Abdallah

Umar ne ya ce"ya naga ka zauna ko ba muda wurin zuwa ne yau?

Murmushi Abdallah yayi Wanda da gani bata wuce fuskarshi ba yace" akwai gurin zuwa mana sai dai ba kud'i , dama tunani ni na idan na samu kud'i da safen nan in saima su inna abin da zasu CI , to gashi kuma duk k'ofofi sun kulle"

Umar shiru yayi yana nazarin abokin nashi sannan yace "tashi muje"

"Ina kenan? Cewar Abdallah

"Bakin titi zaka raka ni"

"to" kawai yace sannan ya mik'e sukA d'au hanya,

Suna tafe suna firarsu irin ta abokai kuma aminai suka k'arasa , k'ofar shagon wani me shayi Umar ya ja birki ,

Abdallah ya kalleshi ya ce"me za muyi anan?"

"Tsaya ka sha kallo "ita ce kawai amsar Umar, ya zagaya yayi ma mai shayin magana ya dawo ya ce mawa Abdallah "bismillah" ya nuna masa wata kujera da ba kowa akai ,.

Bai musa ba ya zauna suna zaune a wajen kusan minti biyar ba Wanda yayi magana cikin su , sai ga mai shayi ya kawo musu , tea ne aka had'a musu dai-dai shan talaka da bread ,

Abdallah ya bud'e baki zai yi magana kenan Umar ya katse shi"da kata ustazu bana son wani k'orafi CI abin cin ka" Umar ya k'arike maganar yana janyo nashi kofin

Ba yanda Abdallah ya iya domin baya son ganin b'acin ran abokin nasa Sam ya ja kofin shi tare da bismillah ya fara aikawa cikin shi Wanda rabon shi da abinci tun safiyar jiya ,

Bayan sun natsa ne Umar ya sallami me shayi tare da karb'ar wata Leda a hannun shi sannan suka kamo hanya

"Umar bansan da bakin da zan gode maka ba , nagode da taimakon da kake yi min Allah ya saka maka da alheri Allah ka Nuna min ranar da zan faran ta maka kaima "

"Amin , Abdallah bana buk'atar godiya daga gare ka taya za'a yi na samu kud'i har na iya kashe wa ba tare da kai ba wannan ba mai yuwuwa bane"

"Dole na gode maka aboki na daga kai sai mahaifiya ta kuke gane meke damu na"

"Uhum" kawai Umar yace domin ya san gaskiya Abdallah ya fad'i ,

Da haka suka k'arasa k'ofar gidan su Abdallah dukan su atare suka shiga gami da sallama ,

Mama ce a tsakar gidan tana zauna ita da wata matashiyar yarinya suna zaune akan tabarma kowa da hijab ajikin shi da alama sallah suka idar(salatul duha)

Yarinyar ce ta amsa musu domin Mama addu'a take yi

"Ina kwana yaya Umar?" Cewar. Yarinyar

"Lafiya lau hafsa ya gida?"

"Lafiya lau"inji yarinyar da aka Kira da hafsa

Dai-dai nan Mama tace" maraba da Umar" murmushi yayi sannan yace "yauwa Mama , kun tashi lafiya ?",

Mama ta bashi amsa da "lafiya lau "

Sannan ya juya ya ce ma hafsa " ke karb'a wannan kije Ki had'o"

Hafsa ta karb'a ledar ta wuce D'an k'aramin kitchen d'in su.

Sai alokacin Abdallah yayi magana " haba Umar kaima fa ba kud'in nan kake da shi ba amma sai kai ta wani wahala"

"Umar ya turb'une fuska yace "yan zun Dan nayi ma Mamana wani Abu shine wahala to ni Neman albarka nake nema " yadda ya k'arike maganar kamar yayi fushi basu yi aune ba sai jinshi suka yana fad'in " nabar Ku cikin amincin ubangiji"

Aiko Abdallah ya zabura ya bishi , da k'yar ya shawo kanshi ya tsaya ya saurare shi , nan ya bashi hak'uri tare da tambayar ina ya samu kud'i

"Acikin Raguna nane tun jiya d'aya bata da lafiya yau da safe da naga asara zanyi shine na yanka ta na kai kasuwa abanza mahauta suka siyeta dubu tara "ya k'arike maganar cikin takai CI

"To amma Umar ai kana da hidima"Cewar Abdallah

"Kaga gida uku na raba kud'in biyu naba umma narik'e d'aya nida aboki na "

Ajiyar zuciya Abdallah yayi sannan yace "Allah ya Sanya ma kud'in albarka"

"Amin" cewar Umar sannan suka bazama cikin gari

For comment 08165728746
[12/13/2017, 8:32 AM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*

*MRS NN ONE*💋

Dedicated to PURE MOMENT OF LIFE WRITERS

® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*

_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_

# [email protected]
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com

Page 2⃣

WAYE ABDALLAH

Abdallah d'ane ga Abdallah asalin mahaifin shi D'an wani k'auye ne ahanyar jos ya baro gida sakamakon rasuwar iyayen shi kuma shi kad'ai iyayen shi suka Haifa , alokacin da ya baro gida yana da matar aure me suna Hindatu itama auren zumunci akayi musu da ita , Abdallah ya tattara yan k'wandalolin da ya ke dasu ya taho garin zazzau domin Neman kudi , yasamu wani D'an k'aramin gida yasiya suka zauna shi da matarshi Wanda har zuwa wannan lokacin bata da ciki , yakan fita kullum ko zai samu abin yi amma babu rannan kawai sai ya yanke shawarar bari yaje bakin kasuwa ko dako yayi , to ahaka yake samu yana ciyar da matar sa duk da ba kullum ake samu ba,

Kasan ce warsa shida matarshi basu da hayaniya yasa suka zauna lafiya da mutanen unguwar , gidan da ke kallon gidan Abdallah gidan wani malami ne mai suna Malam Kabiru mai almajirai wani lokacin idan Abdallah ya dawo k'adugo yakan zauna yayi karatu awajen shi Kasan cewar shi mutum mai son karatu , akwana a atashi ba wuya sherar su Abdallah biyar agarin Zaria , suna rayuwar su yau samu gobe rashi , Akwai wani mak'ocin Abdallah wani tsanin gidan shi Dana mak'ocin gida biyar ne sunan sa Jafar shima dai rufin asirine kawai gareshi shiyasa abotar su tazo d'aya da Abdallah ,

Wata rana sai suka yanke shawarar suje su nemi aiki gidan bulo ko ruwa ne surunk'a d'ebowa , aiko basu sha wahala ba tunda sunsan me gidan bulo d'in ,

Kwanci tashi ba wiya har suma aka koya musu yadda Zasu had'a bulo wata ,

Wata rana Hindatu ta tashi da zazzab'i ciwon kai da jiri sai ranar sanyi take , akwai wani PHC asaman layin su nan ya kaita gwanjin farko aka tabbatar mai da tana da ciki murna kuwa ba'a fad'uwa tunda ga lokacin ya koma bata kulawa na musamman Dan duk wani aikin gidan shi yake yi

Alokacin da cikin Hindatu yakai wata takwas ya shigo mata da wani madai-daicin rago tayi murna sosai tare da godiya , bayan sati biyu Abdallah yaje gurin aikin shi sai man injin d'in ya k'are be jira kowa ba ya d'auko mai ya shiga d'urawa yana cikin haka ne wani noti ta k'asan injin d'in ya fita yana gama d'ura man ya cire rigarshi ya kwanta ta k'asa saida ya lek'a ya ga Ashe ma notin ba d'aya bane kafin ya gama tunanin da zai yi injin d'in ya fad'o masa a k'irji bai sake sanin inda kanshi yake ba sai dai ya farka ya ganshi gaban Hindatu ta na ta faman kuka k'irjin shi duk an d'aura mai su da farin bandeji da k'yar ya iya d'aga hannu ya bubbuga mata bayan ta , sai sannan ne ta juyo tace mishi sannu Malam d'aga mata kai yayi dan ya kasa magana k'irjin shi ya mishi nauyi sosai , tunda ga ranar baya iya komai idan ya fara tari haka yake fitar da jini guda guda , ranar wata juma'a kuwa Abdallah ya rasu , Allahu Akbar mutane sunji mutuwar shi sosai musamman ma abokan shi guda biyu Malam Jafar da Malam Kabiru,

Bayan rasuwar Abdallah da sati d'aya Hindatu ta haihu tare da taimakon matan Malam Kabiru da Jafar , matar Jafar lokacin tana da goyon yaron ta Umar D'an wata biyar ,

Hindatu ta haifi d'anta namiji yaro sak kamar shi da Baban shi dangin ta da suka zo sunso su maida ta gida amma fir ta k'i hakan yasa suka hak'ura suka barta mak'otan nan nata su ke ciyar da ita , ranar bakwai yaro yaci suna Abdallah .

Haka rayuwa ta cigaba da garama Hindatu idan mak'otanta sun samo su bata randa basu samu ba kuma kowa ya sha ruwa ya kwanta ,

Lokacin da Abdallah ya kai shekara bakwai Malam Jafar ya had'a shi da Umar ya sasu amakaran tar boko ta gwamnati ,

Abdallah da Umar sun taso cikin son junan su da tausayin iyayen su wani lokacin da Kansu suke zuwa bakin kasuwa suyi dako su sami 'yan kud'i su kaima iyayen mata sukuwa suyi ta sa musu albarka

Tun suna k'anana suke zuwa d'aukar karatu wajen Malam Kabiru har suka sauke bayan sun sauke sai ya sa musu littafai

Suna SS3 mahaifin Umar ya rasu anan karatun su na boko ya tsaya ,
Chapter 1 · 0% Book details