Sashe 15
Azaad Junaid Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Zo ka zauna Datti zan yi magana da kai"
A natse ya dawo ya zauna daff...da ita.
"Datti indan lissafina ya tafi dai-dai yau kwana goma da daura maka aure, saidai abin da ban fahimta ba har sai zuwa yaushe amaryar taka za ta tare?"
Murmushi ya yi wanda ya tsaya iya fatar bakinsa, ya yi shiru kamar mai nazari kafin ya ce.
"Jadda nayi magana da Hakeem ya ce cikin sati nan za ta tare amma za ki iya bincikarshi da kanki.
"Shikenan tashi ka tafi Allah ya tsare yasa ayi kyakkyawar tafiya"
"Amin thumma amin!
Ya faɗa tare da sa kai ya fita bakinshi d'auke da addu'ar fita daga gida.
***************
Tun daga ranar da Miyya ta ji zance aurenta ta tashi hankalinta, yayin da Aunty Zaliha take bin ta da rarrashi haɗi da nasiha sannu a hankali nasiharta tafara tasiri akanta. Hakan yasaka Aunty Zaliha ta dukufa wajen gyarata idan ka ga yanda Miyya ta dawo da matuk'ar wahala ka iya gane nan take.
Tayi bul-bul k'irjinta ya k'ara cika, fatar jikinta tayi smooth gwanin sha'awa ita kanta sau dama idan ta shiga wanka sai ta 6ata dogon lokaci gaban mirror tana kallon yadda jikinta ya dawo ita kanta tana jin sha'awar kanta balle ga lafiyayye namiji ya yi arba da ita..
Zaune take gaban dressing mirror fitowarta daga wanka kenan, jikinta na fitarda sihirtattace k'amshi saboda ko wanka za tayi sai Aunty Zaliha ta zuba mata kalolin turaruka wanka daban-dabam shiyasa duk idan ta zauna sai tabar k'amshinta. Aunty Zaliha ta shigo rik'e da ma-dai-daci cup tana shigowa Miyya ta 6ata fuska saboda ta riga da tasan kwanan zance.
"Kar6i ki shanye ki bani cup"
Bata yi gardama ba ta amsa ta shanye tass ta mik'a mata cup, aunty Zaliha tana murmushi ta juya ta fita. Miyya ta bi ta da kallo har yau ta kasa daina mamakinta.
*****************
"Hasheem Kaɗai bi lamari nan a natse cikin hikima da dabara, wallahi-tallahi Azaad ya fi ka shu'umanci. Kana dai kallon irin mutuwar k'as-k'anci da Babban Yaya da Alhaji Buba suka yi ko kare gidana bana fatar ya yi irinta.
Ahmadu ya faɗa yana share d'an uban gumin da ya tsatsafo mishi a goshi, ya rasa dalili ko sunan Azaad ya anbata sai ya tsinci kanshi cikin mugun yanayi.
"Mtsss.... Kaɗai Yaya Ahmadu an yi matsoraci ni nan da ka ganni ba Azaad ba ko uwarshi dake lahira da za ta dawo duniya sai na wulak'anta rayuwarta, balle wani k'aramin gwaro irinsa.
Jin furuncinshi yasa Alhaji Abdallah ya girgiza kai sai da ya k'are mishi kallo kafin ya ce.
"Kaɗai bi a hankali kamar yadda Ahmadu ya faɗa Hasheem. Gudun kada allura ta tono galma, da za ku d'auki shawarata da nace mu hak'ura da son ganin baya Azaad, saboda ba tun yau ake ruwa k'asa tana shanyewa ba. Ku duba tsawon lokaci da muka d'auka muna binsa da bi ta da k'uli sai asarar dukiyoyinmu muke yi wurin malaman tsinbo da bokaye a banza. Har ta kai da mun fara rasa rayukanmu, tsakani da Allah banaso nayi mutuwa irinta su Babban Yaya mu je gidan shahararru bokaye har ma da matsafa ko yau ɗinan mu je wurin wani matsafi, da idanuwanku kun ga abin da ya faru ya kira sunan Azaad a madubin tsafinsa a maimakon ya fito shi Kaɗai sai ya fito tare da aljanarsa dake bashi kariya. Dakyar mu kasha saboda haka magani bari kar a fara ni mu dai ri ga da mun fara amma Kuma lokaci bai k'ure mana ba mu rufawa kanmu asiri mu watsar da makaman yak'inmu, ko don gudun mutuwar wulak'anci..
"Dakata Alhaji Abdallah!
Hasheem ya faɗa cikin tsawa tamkar yana yi da sa'anshi.
"Tun farko ba kidahumancin ku ne ya jawo ba. Na sha faɗa muku bokayenku duk makaryata ne, basu iya komai ba sai gilla k'arya. Ku bani dama za ku ga aiki da cikawa zan nemo professional killers su cika masa aiki kyaftawa gira su turo shi garin da ba a dawowa.
"Shikenan ku je Allah ya bada sa'a saidai inason ku sani a wannan karo kuma a wannan tafiya ba dani ba, saboda gani ga wane ya isa wane tsoron Allah.
Cewar Alhaji Abdallah yana k'arashe magana ya Kade babbar rigarshi ya k'ara gaba, gaba ɗayansu suka bi shi da kallo kafin su sake dawowa da natsuwarsu kan Hasheem, wanda ya fito da karan sigari ya jefa baki yana shirin cinna mata wuta Hajiya Kubra ta dakatar dashi.
"Kar ka sake ka kuna mana sigari anan domin ba so warinta nake yi ba yanzu nan sai ta ɗaga min hankali, ka bari sai ka fita can waje ka kunna abarka.
Ya galla mata harara kana ya yi kwafa tare da cizo la66anshi na k'asa, yana jinjina ranarda duk tashigo hannunshi irin wulak'anci da zai shuka mata dole ya cire sigarin ba don ranshi naso ba.
Ahmadu kan ya kasa yak'i da zuciyarsa sai ya ji kamar ya bi bayan Alhaji Abdallah sai kuma wata zuciya ta kwa6e shi gara ya zauna ayi dashi gudun kada giwa ta faɗi aci nama ba dashi ba. Kuma ai ba wurin boka za a je ba balle Aljanar Azaad ta kashe su.
***************
A yau Hakeem ya yanke shawarar ya faɗawa Miyya gaskiyar al'amarin, saboda yana so ta tare kafin Azaad ya dawo daga business trip ɗin da ya tafi. Shiyasa ya aika kiranta lokaci da sak'on ya risketa sai da taji matsananci faɗuwar gaba.
Tsawon lokaci da ya aika kiranta ta kasa tashi ta je sai tufka da warwara take yi saboda tun daga ranar da taji zancen aurenta dashi take wasan 6oya koda kuskure bata bari suka haɗu ba. Shi kanshi Hakeem yana shakkar yadda zai faɗa mata wannan bak'on al'amarin saboda sun yi wasa da hankalinta ba Kaɗan ba. Amma dole ce tasa su yin hakan.
"Wai Miyya ba za ki fito daga d'akin bane ko sai Abban Rayhan ya zo da kanshi?"
Muryar Aunty Zaliha ce ta dawo da ita daga duniyar tunani da ta lula, cikin sanyi jiki ta fito sanye da dogon hijab har k'asa tana shigowa falon ta sadda kanta k'asa can nesa dasu ta nema ta zauna, ta shiga wasa da babban yatsar k'afarta ta dama. Hakeem ya rasa ta inda zai fara kama bakin zare sai musu- musu yake da baki kamar mai jan casbi, can dai ya yi ta ɗiya maza ya yi gyaran murya kana ya ce.
"Da farkon dai zan fara cewa dake Aslamiyya ki yi hak'uri domin akwai abubuwa da yawa da ya kamata ki sani kafin yau sai dai na 6oye miki ne na bi ki da yadda kika fahimci al'amari ba don komai ba sai don ki sami natsuwa da kwanciyar hankali to Al-hamdu-lillah burina ya cika. Miyya dangane da zancen aurenmu dake ba gaskiya bane amma zancen an d'aura miki aure gaskiya ne. A zahirin gaskiya ba dani aka d'aura miki aure ba da aminina ne kuma d'an uwana Azaad Junaid.
A firgice Miyya ta ciro kanta daga k'asa ta jefawa Hakeem wani irin rikittace kallo mai cike da tarin tambayoyi hakan yasa ya gintse bakinshi ya kasa ci gaba da magana...
*AZAAD JUNAID*
_{The young Billionaire}_
Na
Jeeddah Aliyu
Top Ten Takun Haske Batch:A
*Wannan littafi na kud'i ne yana daya daga cikin top ten takun haske don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya ba domin mallakar littafan mu guda bakwai sai a tuntu6e wannan number* +447894142004
13...
Kallo d'aya za ka yiwa Miyya ka gano ba k'aramin firgici da tashi hankali take ciki ba.
Ta kasa gasgata abin da kunneta ya ji daga bakin Hakeem gani take yi kamar wasa ne yake yi, kawai so yake ya gwadata shiyasa ya bijiro mata da wannan zance mai kama da almara.
Gani ta kasa furta kalma ko d'aya daga bakinta yasa Hakeem ya ci gaba da faɗar
"Azaad mutumin kirki ne abokina ne tun na yarinta nasan shi ciki da waje da yana da wata matsala ko gacci da ba zan nema mishi aurenki ba.
"Innalillahi wa'aina illahim raji'un! Hasbunallahu wal'imal wakil.....Ni kan na shiga uku ni Miyya wai meke shirin faruwa da rayuwata ne?"
"Alkhairi Miyya Alkhairi ne yake bibbiyarki, wallahi-tallahi da Azaad yana da wata matsala ina da tabbacin Abban Rayhan ba zai shige mishi gaba wajen naman aurenki ba...
"Ya isa nace ya isheku haka! an gayamuku rayuwata kwallo ce da za ku dinga jefata raga a duk lokaci da ku kaso?" Ko an gayamuku don banida gata yana nufi ku yi wasa da zuciyata yadda ku ga dama?"
Kasa ci gaba da magana tayi sakamakon wani irin nauyi da k'irjinta ya yi kamar an ɗora mata dutsi, tasa hannu ta dafe saitin zuciyarta da ke bugawa da k'arfin gaske. Aunty Zaliha ta taso da sauri ta ɗagota kana ta mik'ar da ita tsaye. Miyya ta kalli Aunty Zaliha da idanuwanta suka fara komawa jajjaye muryarta na rawa ta ce.
"Sake ni Aunty Zaliha duk abin da ku ka yi min ba zan ga laifinku ba. Domin da Baffana da kakata ba su ba ku k'ofa ba da ba za ku yi wasa da hankalina har haka ba. Ban ta6a jin haushi kasancewata marar gata ba sai yau. Da ina da gata ko Kaɗan ba za ku kwatata rikita min hankali da tunani ba.
"Miyya please Kar ki yi mana mummuna fahimta da fari ki natsu na fahimtar da ke ta yadda za ki fahimci lamarin cikin sauk'i.
"Haba uncle Hakeem ya ka ke magana tamkar kana nufi babu zuciya a k'irjina. Miyasa tun farko ba ka fito min a mutum ba. Sai ka yi amfani da rud'add'iyar hanya ka rud'a zuciya da tunanina?"
A natse ya dawo ya zauna daff...da ita.
"Datti indan lissafina ya tafi dai-dai yau kwana goma da daura maka aure, saidai abin da ban fahimta ba har sai zuwa yaushe amaryar taka za ta tare?"
Murmushi ya yi wanda ya tsaya iya fatar bakinsa, ya yi shiru kamar mai nazari kafin ya ce.
"Jadda nayi magana da Hakeem ya ce cikin sati nan za ta tare amma za ki iya bincikarshi da kanki.
"Shikenan tashi ka tafi Allah ya tsare yasa ayi kyakkyawar tafiya"
"Amin thumma amin!
Ya faɗa tare da sa kai ya fita bakinshi d'auke da addu'ar fita daga gida.
***************
Tun daga ranar da Miyya ta ji zance aurenta ta tashi hankalinta, yayin da Aunty Zaliha take bin ta da rarrashi haɗi da nasiha sannu a hankali nasiharta tafara tasiri akanta. Hakan yasaka Aunty Zaliha ta dukufa wajen gyarata idan ka ga yanda Miyya ta dawo da matuk'ar wahala ka iya gane nan take.
Tayi bul-bul k'irjinta ya k'ara cika, fatar jikinta tayi smooth gwanin sha'awa ita kanta sau dama idan ta shiga wanka sai ta 6ata dogon lokaci gaban mirror tana kallon yadda jikinta ya dawo ita kanta tana jin sha'awar kanta balle ga lafiyayye namiji ya yi arba da ita..
Zaune take gaban dressing mirror fitowarta daga wanka kenan, jikinta na fitarda sihirtattace k'amshi saboda ko wanka za tayi sai Aunty Zaliha ta zuba mata kalolin turaruka wanka daban-dabam shiyasa duk idan ta zauna sai tabar k'amshinta. Aunty Zaliha ta shigo rik'e da ma-dai-daci cup tana shigowa Miyya ta 6ata fuska saboda ta riga da tasan kwanan zance.
"Kar6i ki shanye ki bani cup"
Bata yi gardama ba ta amsa ta shanye tass ta mik'a mata cup, aunty Zaliha tana murmushi ta juya ta fita. Miyya ta bi ta da kallo har yau ta kasa daina mamakinta.
*****************
"Hasheem Kaɗai bi lamari nan a natse cikin hikima da dabara, wallahi-tallahi Azaad ya fi ka shu'umanci. Kana dai kallon irin mutuwar k'as-k'anci da Babban Yaya da Alhaji Buba suka yi ko kare gidana bana fatar ya yi irinta.
Ahmadu ya faɗa yana share d'an uban gumin da ya tsatsafo mishi a goshi, ya rasa dalili ko sunan Azaad ya anbata sai ya tsinci kanshi cikin mugun yanayi.
"Mtsss.... Kaɗai Yaya Ahmadu an yi matsoraci ni nan da ka ganni ba Azaad ba ko uwarshi dake lahira da za ta dawo duniya sai na wulak'anta rayuwarta, balle wani k'aramin gwaro irinsa.
Jin furuncinshi yasa Alhaji Abdallah ya girgiza kai sai da ya k'are mishi kallo kafin ya ce.
"Kaɗai bi a hankali kamar yadda Ahmadu ya faɗa Hasheem. Gudun kada allura ta tono galma, da za ku d'auki shawarata da nace mu hak'ura da son ganin baya Azaad, saboda ba tun yau ake ruwa k'asa tana shanyewa ba. Ku duba tsawon lokaci da muka d'auka muna binsa da bi ta da k'uli sai asarar dukiyoyinmu muke yi wurin malaman tsinbo da bokaye a banza. Har ta kai da mun fara rasa rayukanmu, tsakani da Allah banaso nayi mutuwa irinta su Babban Yaya mu je gidan shahararru bokaye har ma da matsafa ko yau ɗinan mu je wurin wani matsafi, da idanuwanku kun ga abin da ya faru ya kira sunan Azaad a madubin tsafinsa a maimakon ya fito shi Kaɗai sai ya fito tare da aljanarsa dake bashi kariya. Dakyar mu kasha saboda haka magani bari kar a fara ni mu dai ri ga da mun fara amma Kuma lokaci bai k'ure mana ba mu rufawa kanmu asiri mu watsar da makaman yak'inmu, ko don gudun mutuwar wulak'anci..
"Dakata Alhaji Abdallah!
Hasheem ya faɗa cikin tsawa tamkar yana yi da sa'anshi.
"Tun farko ba kidahumancin ku ne ya jawo ba. Na sha faɗa muku bokayenku duk makaryata ne, basu iya komai ba sai gilla k'arya. Ku bani dama za ku ga aiki da cikawa zan nemo professional killers su cika masa aiki kyaftawa gira su turo shi garin da ba a dawowa.
"Shikenan ku je Allah ya bada sa'a saidai inason ku sani a wannan karo kuma a wannan tafiya ba dani ba, saboda gani ga wane ya isa wane tsoron Allah.
Cewar Alhaji Abdallah yana k'arashe magana ya Kade babbar rigarshi ya k'ara gaba, gaba ɗayansu suka bi shi da kallo kafin su sake dawowa da natsuwarsu kan Hasheem, wanda ya fito da karan sigari ya jefa baki yana shirin cinna mata wuta Hajiya Kubra ta dakatar dashi.
"Kar ka sake ka kuna mana sigari anan domin ba so warinta nake yi ba yanzu nan sai ta ɗaga min hankali, ka bari sai ka fita can waje ka kunna abarka.
Ya galla mata harara kana ya yi kwafa tare da cizo la66anshi na k'asa, yana jinjina ranarda duk tashigo hannunshi irin wulak'anci da zai shuka mata dole ya cire sigarin ba don ranshi naso ba.
Ahmadu kan ya kasa yak'i da zuciyarsa sai ya ji kamar ya bi bayan Alhaji Abdallah sai kuma wata zuciya ta kwa6e shi gara ya zauna ayi dashi gudun kada giwa ta faɗi aci nama ba dashi ba. Kuma ai ba wurin boka za a je ba balle Aljanar Azaad ta kashe su.
***************
A yau Hakeem ya yanke shawarar ya faɗawa Miyya gaskiyar al'amarin, saboda yana so ta tare kafin Azaad ya dawo daga business trip ɗin da ya tafi. Shiyasa ya aika kiranta lokaci da sak'on ya risketa sai da taji matsananci faɗuwar gaba.
Tsawon lokaci da ya aika kiranta ta kasa tashi ta je sai tufka da warwara take yi saboda tun daga ranar da taji zancen aurenta dashi take wasan 6oya koda kuskure bata bari suka haɗu ba. Shi kanshi Hakeem yana shakkar yadda zai faɗa mata wannan bak'on al'amarin saboda sun yi wasa da hankalinta ba Kaɗan ba. Amma dole ce tasa su yin hakan.
"Wai Miyya ba za ki fito daga d'akin bane ko sai Abban Rayhan ya zo da kanshi?"
Muryar Aunty Zaliha ce ta dawo da ita daga duniyar tunani da ta lula, cikin sanyi jiki ta fito sanye da dogon hijab har k'asa tana shigowa falon ta sadda kanta k'asa can nesa dasu ta nema ta zauna, ta shiga wasa da babban yatsar k'afarta ta dama. Hakeem ya rasa ta inda zai fara kama bakin zare sai musu- musu yake da baki kamar mai jan casbi, can dai ya yi ta ɗiya maza ya yi gyaran murya kana ya ce.
"Da farkon dai zan fara cewa dake Aslamiyya ki yi hak'uri domin akwai abubuwa da yawa da ya kamata ki sani kafin yau sai dai na 6oye miki ne na bi ki da yadda kika fahimci al'amari ba don komai ba sai don ki sami natsuwa da kwanciyar hankali to Al-hamdu-lillah burina ya cika. Miyya dangane da zancen aurenmu dake ba gaskiya bane amma zancen an d'aura miki aure gaskiya ne. A zahirin gaskiya ba dani aka d'aura miki aure ba da aminina ne kuma d'an uwana Azaad Junaid.
A firgice Miyya ta ciro kanta daga k'asa ta jefawa Hakeem wani irin rikittace kallo mai cike da tarin tambayoyi hakan yasa ya gintse bakinshi ya kasa ci gaba da magana...
*AZAAD JUNAID*
_{The young Billionaire}_
Na
Jeeddah Aliyu
Top Ten Takun Haske Batch:A
*Wannan littafi na kud'i ne yana daya daga cikin top ten takun haske don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya ba domin mallakar littafan mu guda bakwai sai a tuntu6e wannan number* +447894142004
13...
Kallo d'aya za ka yiwa Miyya ka gano ba k'aramin firgici da tashi hankali take ciki ba.
Ta kasa gasgata abin da kunneta ya ji daga bakin Hakeem gani take yi kamar wasa ne yake yi, kawai so yake ya gwadata shiyasa ya bijiro mata da wannan zance mai kama da almara.
Gani ta kasa furta kalma ko d'aya daga bakinta yasa Hakeem ya ci gaba da faɗar
"Azaad mutumin kirki ne abokina ne tun na yarinta nasan shi ciki da waje da yana da wata matsala ko gacci da ba zan nema mishi aurenki ba.
"Innalillahi wa'aina illahim raji'un! Hasbunallahu wal'imal wakil.....Ni kan na shiga uku ni Miyya wai meke shirin faruwa da rayuwata ne?"
"Alkhairi Miyya Alkhairi ne yake bibbiyarki, wallahi-tallahi da Azaad yana da wata matsala ina da tabbacin Abban Rayhan ba zai shige mishi gaba wajen naman aurenki ba...
"Ya isa nace ya isheku haka! an gayamuku rayuwata kwallo ce da za ku dinga jefata raga a duk lokaci da ku kaso?" Ko an gayamuku don banida gata yana nufi ku yi wasa da zuciyata yadda ku ga dama?"
Kasa ci gaba da magana tayi sakamakon wani irin nauyi da k'irjinta ya yi kamar an ɗora mata dutsi, tasa hannu ta dafe saitin zuciyarta da ke bugawa da k'arfin gaske. Aunty Zaliha ta taso da sauri ta ɗagota kana ta mik'ar da ita tsaye. Miyya ta kalli Aunty Zaliha da idanuwanta suka fara komawa jajjaye muryarta na rawa ta ce.
"Sake ni Aunty Zaliha duk abin da ku ka yi min ba zan ga laifinku ba. Domin da Baffana da kakata ba su ba ku k'ofa ba da ba za ku yi wasa da hankalina har haka ba. Ban ta6a jin haushi kasancewata marar gata ba sai yau. Da ina da gata ko Kaɗan ba za ku kwatata rikita min hankali da tunani ba.
"Miyya please Kar ki yi mana mummuna fahimta da fari ki natsu na fahimtar da ke ta yadda za ki fahimci lamarin cikin sauk'i.
"Haba uncle Hakeem ya ka ke magana tamkar kana nufi babu zuciya a k'irjina. Miyasa tun farko ba ka fito min a mutum ba. Sai ka yi amfani da rud'add'iyar hanya ka rud'a zuciya da tunanina?"