← Book details Akwai Lokaci Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 19

Sashe 7

Akwai Lokaci Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

ai basaikince yakarba koya karba koka karya karba sundai fi kusa 'yarsace bai isa yacanja taba kefa duk lokacin dayaga dama zakiyi waje

Zatayi magana Hakeem yarungumota suka fita
Takaici yadami Laila tayi kaman ta hadiyi zuciya ta mutu

Suby tace kai wallahi akwai matsala babba agidan caf

Ashe Laila Bata kashe wayartaba

Meenat ta ce mummyna yanaji hayaniya
Lafiya kuwa kafin Laila tayi magana har suby takarbi wayar takwashe komai tafada mata

Meenat tace nazo koni ko 'yar iskar yarinyar nan

Ta kashe wayar saboda takaici

Husnah da Hakeem tare suka shiga falon mummy
Ganin mummy na falon husnah sai kacaniyar kwace hanunta takeyi

amma Hakeem yaki sake ta
Dahaka suka shiga Husnah tayi saurin zubewa tagaida mummy

Mummy tace zonanki kizauna Husnah kidaina zama akasa keda falon mummynki

Husnah murmushi kawai amma ita bazata iya mummy nasama kujera itama tazauna ba

Mummy tace kukarasa kuyi break fast
Husnah tace mummy ina daddy
Mummy tace yafita sunyi wasu bakine

Hakeem yace OK bakin sun isokenan

Mummy tace ina tunanin haka

Hakeem da Husnah suka yi dining area mummy tasan idan tazauna husnah bazata ci wani abin kirkiba

Yasa ta tashi ta haura sama
Hakeem kuwa kaman jira yake mummy ta fita yajanyo husnah yadaurata kan cinyarsa yana feeding dinta da kanshi

Sai da yatabbatar takoshi yabarta

Kafin shima zaifara cin nashi yadaga spoon zai kai baki sai husnah tarike cokalin

Tace aimunyi alkawarin karwani yashiga ma wani aikinshi
So kadina shiga min nawa

Ta dauki spoon tafara feeding dinshi shima

Hakeem cikin wani shauki yake jinshi mewuyar fassara saboda yadda yaga babynshi tafara sakin jiki dashi sosai tana nuna mishi soyayyar da be taba tunanin zata iya nuna mishi duba ga yanayin kunyarta

Suna gamawa tadauki brief case dinshi tarataya tace oya

Kaje kawa mummy sallama yace inje ina tace office mana

Yace ai ba inda zani jeki dauko mayafinki kawai muje yawo

Cike da murna husnah tace wallahi kaman kasan inason ganin waje

Yayi murmushi yace maza jeki dauko kafin nakirga ashirin

Bai rufe baki ba tayi waje da gudu kaman Bata jin zafin jikinta

Murmushi kawai yayi mummy ce tasauko daga sama tace Ku gama break din yace mungama mummy
Zamu dan zagaya ne taga gari mummy tace yakamata taga gari itama tasan Kaduna

Next page

Your comment is
Needed fans ❤❤

Love u all

📝📝📝📖📖📖
[05/05, 10:18 PM] UMMU AFAN 🌹: 🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗
🎗🎗
🎗
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM

Story & written
By
The special writer

UMMU AFAN

🖊🖊🖊🖊🖊🖊📚

🌹FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION🌹

🌹🌹 (F.C.T.W.A)🌹🌹

🌹HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION🌹

🎗I DEDICATE THIS PAGE TO YOU UMMU HISHAM ina alfahari dake wajen nice comments wallahi Allah yabar zumunci keep it up🎗

🎗AKWAI LOKACI 🎗

🎗PAGE 131 to 135🎗

HAKEEM DA HUSNAH

Hakeem na driven amma hanun daya yana makale da hanun husnah

Wayar Hakeem yadaukara yana gani yaga Ahmad ne

Ahmad yace kai young Prof wai mekake tun tuni baka fito ba

Hakeem yayi murmushi yace ganinan a hanya zuwa amma fa aiki zanzo ba zanbada

Wasu muhimmam takardu ne wa manager yacigaba da kula da komai saina nan da kwana biyar zan koma office

Ahmad yace kai soyayya manya
Wannan irin rawan kai Man
Karka rikita musu yarinya fa

Hakeem yace zamu karaso gidan naku ma kasanar da madam Aisha

Ahmad yace a haba kace muna da Mayan baki kenan
To barin koma gidan najiraku

Hakeem yace OK saimun karaso

Ya kashe wayar ya kalli Husnah dake ta chat a wayarta

Yace kedawaye tace nida anty kubra ne wallahi

Saida suka jajja wurarn shakatawa na kaduna kafin suka wuce gidan Ahmad

Suna zuwa Aisha ta karbi husnah hanu biyu taja hanunta tace kinga zo muwuce can ciki

Su suzauna abinsu anan

Ahmad yace indai akayi gulmam mu Allah nagani dake da kanwarkin nan

Husnah tayi murmushi Bata ce komai ba
Aisha tace Ashe kunsan Baku da gaskiya kenan shiyasa kuke tunanin za ayi gulamarku

Suka wuce abinsu suna dariya

Ahmad yakalli Hakeem yace kai mutumina gaskiya balalle nan da wata daya mugane kaba gaskiya duk kawani canja gawani kyau da fresh

Hakeem yace kai dai duk aikin babyna ne
Kasan Allah Dana San haka aure yake da ban tsaya batawa kaina lokaci wajen gwada taba

Kaga wakila da yanzu tana shirin Haifa min baby

Ahmad yace yanzu baka tunanin kuma 'yata tadawo taga ubanta yana cin soyayya da kawarta yazakayi kenan

Hakeem yayi murmushi yace koda meenat da Husnah kawayene ba ruwana da alakarsu

Ballantana ma Husnah tanuna min ba kawarta bace suna dai gaisawa kadan
Kasan meenat gaba daya uwarta ta Bata ta
Kaga kuwa ballebane suhada hanya da Husnah

Ahmad yace to da saukima tunda ba kawarta bane
Allah ya rufa asiri

Hakeem yace ko kawarta ce baruwana
I love my wife more than her expectation

Ahmad yace wallahi mutumina meenat ta ruda ka dayawa fa gaskiya ta ciri tuta acikin mata

Hakeem yace bakadan ba

Aisha ta kai musu abinci dining

Kafin tadauki nasu da Husnah ta wuce da shi ciki

Hakeem yace madam kikula min da ita fa dan bata son cin abinci sanayi dagaske take cin abinci

Aisha tayi murmushi tace karka damu zataci sosai indai nice

Yayi dariya yace yauwa maman twins
Tace kai Allah ya amshi bakin ka tawuce

Ahmad yace kasan yadda Aisha takeson twins kuwa

Nan dai sukayi hirarsu sai wajen karfe biyar suka koma gida

Husnah tace oyoyo mummyna nayi missing dinki wallahi
Mummy tayi murmushi tace nima wallahi ina zaune Dan wunin da kikayi bakya nan duk sainaji ba dadi

Hakeem yayi murmushi yace wato ma mummy batani ma kikebako

Mummy takalleshi tace au dama ka shigo ne ai banganka ba ma

Husnah dariya tayi tafaki idon mummy ta mishi gwalo

Hakeem yace mummy kinga kinja tana min gwalo ko

Wato nine baki gani ba ko

Mummy tace danaganka ai Dana kulaka Husnah da mummy sukayi dariya

Husnah ta tashi tace mummy ga tsarabarki nan keda daddy taga rakene aka gyarasu sunyi kyau da sha'wa

Mummy ta ce kai kaman Kinsan ina matukar son rake allah yamaki albarka Husnah tace amin mummy na

Hakeem yace tunda ni baki ganniba basai nabaki naki tsarabar kenan

Mummy tayi murmushi tace a naji tunda 'yata tabani ai wadatar Husnah tayi dariya

Hakeem yayi murmushi yace wakike wa dariya husnah tace nida kujera nefa badakai ba

********

Bayan sati biyu shakuwa soyayya da kuma wayewa duk sun bayyana ajikin husnah ga uba kyau da Hutu
Bata kara kiba ba amsa fa tayi wani fresh da bulbul da ita gwanin sha'wa ga uwa uba soyayyar mijinta Dana surukanta

Hakeem kuwa Wanda yasanshi ada yaganshi yanzu balalle yaga neshi ba saboda kwanciyar hankali da yasamu

Ga bunkarsar arzikinsa ta kota ina
Samun karuwa yakeyi

******

Meenat zaune satinsu kusan daya da dawowa amma bashir ya hanata zuwa Kaduna

Yace saiyaga dama zataje

Tana zaune hajiya rukayya tazo gidanta meenat nakwance kan cinyarta tana kuka hajiya rukayya Tace yanzu wannan yaro haka zaimana dubi dan Allah yadda kikabi kikarame

Waike kina auren mekudi ina wallahi dasake dole zamuyi maganinsa
Zaidawo kamar yadda yake da sai abinda kikace mishi

Meenat tace yauwa hajiyata daman nasan zakimin komai wallahi bashir yacanja sosai

Hajiya rukayya tace yanzu yaudin damukayi zanbiyo tanan mutafi Kaduna dake baibariba

Meenat tace yaki wallahi yace idan nasa kafa natafi karnadawo mishi gida

Hajiya rukayya tadafe kirjin har abin yakai haka

a a gaskiya dole mutafi yau dan nayi niyar tafiya dake

Meenat tace tayaya hajiya ai yakine

Hajiya tayi murmushi tace badai yana ganin kiman baban ba
Meenat tadaga kai sama tace kwarai kuwa

Hajiya rukayya tace to kyale nidashi

Bashir yadawo gida daga office
Yagaji sosai yanashigowa falon yaga hajiya rukayya ya tamke fuska sannan yace sannu hajiya zaiwuce hajiya rukayya tace bakaji ba bashir

Yace inajinki tace mahaifinta akakwantar a asibiti yau kwana daya kenan
Shine nake nema mata izinin zuwa dubashi dan nima can na nufa yanzu

Bashir ta ambaci mahaifintane balafiya yasa yace Allah sarki zata iya zuwa zanzo jibi na dubashi sai mudawo tare

Meenat cikin zumudi tace nagode ya maka mata harara yawuce bedroom dinshi

Meenat tace ajedai tunda kabarni aishikenan

Nan suka shirya sai kaduna

****

Laila da suby da masu aikinsu suna ta shirshiryen zuwan su meenat gida ya kaure da kamshi ta kota ina

Husnah kuwa tana can part din mummy tana tayata shirya kayanta cikin akwati zasuyi tafiya zuwa madina

Dan duk azumi acan dadi yake yi har sallah ma sai bayan sallah suke dawowa

Husnah ta kalli mummy ta ce yanzu mummy gobe warhaka fa kuna can ko
Mummy ta ce sosaima

Tace yaufa 'yarki tana hanya
Husnah tace haka yaya yafada min allah yakawosu lafiya mummy ta ce amin

Next page

Your comment is needed fans

Love u all

😘😘😘

📖📖📝📝
[05/05, 10:18 PM] UMMU AFAN 🌹: 🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗
🎗🎗
🎗
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM

Story & written
By
The special writer

UMMU AFAN

🖊🖊🖊🖊🖊🖊📚

🌹FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION🌹

🌹🌹 (F.C.T.W.A)🌹🌹

🌹HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION🌹

🎗I DEDICATE THIS PAGE TO YOU AGAIN MY SWEET TWINS SISTER UMMY KHALEEL ( HAJARA)🎗
Ina alfahari dake wallahi kina kashani da wannan nice comments din naki Allah yabar kauna🎗😘😘😘😘😘

🎗AKWAI LOKACI 🎗

🎗PAGE 136 to 137🎗

HUSNAH tana gamawa mummy komai ta koma sashinta

Tana shiga kara gyara dakinta sosai kasacewan yau itace da prof kuma asabarce

Tafesa wanka tazauna tana shafa mai itakai take ta jin dadi saboda yau meenat zatazo taganta amatsayin matar ubanta

Tayi murmushi itakadai ta tashi taje wajen English wear's dinta

Tazabo wasu Riga da wondo

Wandon Jean's me adon pink flower ajikinshi

Sai rigar shima pink tayi matukar kyau ita da kanta sai data yaba da kayan

Ta dauko pink ribbon dinta tagyara gashinta yayi kyau sosai kamar wata 'yar india kwalliya tayi Normal amma fa Wanda tayi dominshi ta tabbatar zai yaba sosai

Kara fesa turare tayi kafin nan tadauki chocolate din ta da katuwar Teddy dinta Wanda Prof yasaimata a super market dasuka fita kalakala tasaya masu kyau sosai manya kuma

Tafito a daga part dinta ta kullo ta haura sama tasauko saukowarta taga su Laila ansha kwalliya itada suby an harde a kujera
Chapter 7 · 0% Book details