← Book details Akwai Lokaci Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 11 OF 19

Sashe 11

Akwai Lokaci Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sosai take kissing dinshi Dan tasan abinda yake bukata kenan
Batayi aune aune ba taganta yakwantar da ita duk yadda taso yakyaleta yaki
Sai daya samu nutsuwa kafin yabarta
Cak yadauketa tare sukayi wanka suka shirya

Dakanshi yahada mata kayansawarta kala biyu cikin wani Dan karamin jaka mai kyau da sha'awa

~~~~~~~~~~

Husnah kwance falon ummanta kanta akan cinyar umma suna hirarsu

Anty kubra ta shigo falon tace kinsan Allah husnah kikiyayeni fa zaki karyamana cinyar umma ne katuwa dake

Husnah tayi murmushi tace to kwana nawa bangantaba banga ya shamsu ba

ai dole na damu nayi kewarsu saura ya shamsu zaizo shima yasameni yamin alkawarin zai dinga zuwa sosai yana ganina Amman bai cika ba

Husnah tace wallahi danwake zanci da dambu da kuma tuwan alkama

Kubra ta rike baki duk acikin ki kekadai tace sosai makuwa

amma dai yanzu tuwon nake bukata tukun

Anty kubra tace OK bani minti na muna da miya daman tuwon kawai zanmiki

Husnah tace yauwa matan yaya daga ke bawata

Husnah taci tuwo sosai umma da kubra sunyi mamakin

Umma dai murmushi tayi itakadai tasan dalilin murmushinta

Duk abinda takeso shi ake mata agidan su
Yaya shamsu kafin yadawo sai yatambayeta abinda take sha'wa ya taho mata dashi

Ranar da zata tafi tun azahar YOUNG PROFESSOR ABDUL HAKEEM ABUBAKAR

Ya isa kano gidansu husnah yazarce direct danshi jinshi yake kaman bashi da lafiya Dan kwana biyun datayi bata nan

Saida yaci abinci agidan shida ya shamsu kafin suka wa ummu sallama suka fito suka dau hanya

Hakeem yakasa boye zalamrsa akanta saida. Yayi parking a gefen titi
Komeyasa oho

Suna isa Hakeem yayi parking yazago yabude wa husnah kofa duk abinda kefaruwa a idon meenat da suby Dan suna lambun gidan suna hutawa

Takaici Yakama meenat tace wallahi anty suby danasan husnah zata auri daddy Dana wallahi da banbar hajiya taje gurin maganin ba

Yanzu gashi nibada bash itakuma da auren ubana har bayaganin kowa sai ita

Suby tace ai wallahi zamu koya mata hankali basu rufe bakiba Hakeem yadauko bag din husnah da Yakama hanunta suka shiga ciki

Suna zama husnah ta ce wayyo Prince zansha nun tsamiya zansha kuma nagaji dayawa beside ni idan nayi ma balle nashaba

Cikin sauri yazauna kusada da ita yace kobakida lafiya ne Dan naga kincan minfa sosai

Hanu takai ta lakuce hancinshi tace nidai ba abinda yake damuna
Kawai kasamomin kunun tsamiya

Waya yadaga yakira Ahmed yace kana gidane yace a
Hakeem yace kasa Aisha ta min kunun tsamiya zanzo na dauka

Kafin Ahmad yayi magana Hakeem yakashe wayarshi Dan yasan sai yamishi tsiya

Hakeem yajuya yaga hartafara bacci a mota gabadaya ma baccin tayi

Tashi yayi yamatsa kusa da yakura mata ido sosai

Can zuciyarshi tace anya yarinyar lafoyarta kalau kuwa

Yadauki waya yakira family doctor dinsu macen yace tazo da kayan aikinta
Yafada mata abinda yake zargi tace OK tagane gatanan zuwa

Hakeem cikin tsananin farin ciki yayi sujjadar Allah yatabbatar mishi da abinda yake zargi

Next page

Your comments is needed fans

Love all

📝📝📝📝📝📖📖📖📖📖📖
[05/05, 10:18 PM] UMMU AFAN 🌹: 🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗
🎗🎗
🎗
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM

Story & written
By
The special writer

UMMU AFAN

🖊🖊🖊🖊🖊🖊📚

🌹FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION🌹

🌹🌹 (F.C.T.W.A)🌹🌹

🌹HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION🌹

🎗I DEDICATE THIS PAGE TO YOU Aisha Ibrahim ina matukar jin dadin comment din ki wallahi keep it up ina alfahari dake over my sister 😘😘😘😘😘😘🎗

🎗AKWAI LOKACI 🎗

🎗PAGE 143 to 145🎗

Bayan gwaje gwaje da likita tawa Husnah ta tabbatar mishi husnah tana dauke da cikinshi

Cikin tsanin farin ciki hakeem yace alhamdulillah Allah nagode maka da cika min burina cikin gaggawa

Allah kasauketa lafiya likita tayi murmushi tace gaskiya wannan babyn zaiga gata prof irin wannan doki da murna haka

Yayi murmushi tare da rungume husnah ajikinshi tunda likitar tafada cewan ciki ne da ita
Ta rufe Idan kaman me bacci
Ita kanta takasa sanin meyasata jin kunyar

Hakeem yace wa likita kizuba ido kiyi kallo aranar da Queen dina ta haifamin baby a ranar zan yi abinda za bakowa mamaki
Kuma kema fa baza abarki ba zaki ga goron albishir a account din ki

Likita tayi murmushi tace kai amma nagode Allah yafito mana da wannan babyn lafiya

amma Yakama ka kawota hospital gobe Dan mumata scanning a tabbatar cikin wata nawa ne Dan kasan lokacin da zakafara tsammanin babayn ka

Hakeem yace ai bazan bari sai gobe ba yanzu zamu biki muje Nagani da idona

Doctor tayi murmushi tace ina jiranku to

Hakeem cak yadauki Husnah zuwa bedroom yasamata kataton hijabinta

Sannan kuma ya sunkuya wai ta hau baya

Husnah taga dagaske yakeyi fa
Taware tace a a Dan Allah Prince kabarni maka ganin bamu kadai bane

Hakeem yace ai ni mutane da maganarsu bai cika damuna ba ko agaban mummy zan iya goyanki ballantana 'yata

Husnah tace naji inkai bazaka ji kunya ba aini zanji
Ta kwasa dagudu tabar dakin
Yafito hankalinshi a tashe yace Dan Allah baby kidaina gudu karki samin baby yagaji

Husnah tatsaya cak taki juyowa
Ya tako ya iso har gurinta yajanyota jikinshi yace oya mutafi ko kinga doctor tana jiranmu a waje

Cikin shagwaba husnah tace tun ba aje ko ina ba kafara nuna min iyakata ko
Shine zaka ce wai kar babyn ka yagaji
Wato ma bani bace damuwarka babyn ne ko

Cikin murmushi Hakeem yajuyo da ita suna fusakanta juna yace Haba baby kema kinsan you are my one and only

Taya za ayi nace bandamu damu da lafiyarkiba

ai dake da abinda yake cikin ki
Inkincire mummy da daddy to kune rayuwata kune komai nawa

Husnah tace nidai banyarda ba
aikuwa sai ganin prof tayi gwiwa biyu agabanta

Cikin sauri itama tayi kasan takama hanunshi tace la nifa wasa nakema

Yayi murmushi yaja hancinta yace kinji tsoro kenan tace sosaima wace dasa zuciyata kneeling a kasa ai dole tsoro yakamani yayi murmushi yatashi yadagota cak

Dakyar tabashi hakuri yabarta ta tayi tafiya da kanta

Bayan scanning da akayi wa husnah aka ta babbatar musu da tana dauke da cikin sati bakwai wato getting to two months kenan

A gurin Hakeem yadauki wayarshi yakira mummy da daddy yasanar dasu

Mummy kaman tayi tsuntsuwa tazo taga 'yarta husnah haka take ji

Tayi murna sosai haka ma daddy

Dan mummy hafsat kam ma cewa tayi tundaga can zata fara sayayyar kayan jarirai

Daga hospital sai gidan su Aisha da Ahmad Hakeem yayi dasu

Suna zuwa kuwa Aisha takawo mai kunun tsamiyar dakan yazauna kan carpet ya hada mata sosai tasha kuwa duk sunyi mamaki

Ahmad yace amma natayaka murna abokina Allah yaraba lafiya

Aisha da itama haihuwar ko yau ko gobe

Tayi murmushi tace Allah sarki 'yar kanwata Allah yasaukemu lafiya ko

Husnah tace anty nifa bani da komai

Wasa fa yaya yake muku
Aisha da dariya yaso barke mata tace sosai Nagani kuwa

Wannan tulun kunun da kika shanye ai kowa yasan bake kadai bace

Husnah tayi murmushi tace ai saboda ina sone shiyasa

Hakeem yace sannu da kokari madam kema kina fama da kanki mun hada kida aiki

Tace bakomai wallahi bana ma son zaman

Nan Ahmad da Hakeem sukafita

~~~~~
Bayan sati biyu duk wannan abinda kefaruwa na maganar cikin nan baizo kunnen su Laila ba

Husnah zaune a falonta mai kamshi da sanyun Ac

Kaman daga sama taji murya kaman na anty kubra

Da sauri ta tashi taduba anty kubra ce kuwa tasha kyau cikin wani tsaddan less Dan shima ya ashamsu yanzu kudi yazauna mishi sosai shiyake juya dukiyar husnah Wanda tabashi ragamar komai a hanunshi

Kuma shiyazama manager a company Hakeem

Husnah tayi tsalle ta rungume anty kubra tace wayyo anty na wallahi naji dadin ganin

Anty kubra tace kai Husnah bakida hankaline wayafa miki meciki tana tsalle haka husnah tarufe ido tace anty nifa banida komai

Kubra tace ai Allah zata sake magana husnah taja sukayi part dinta

Laila dake zaune jin abinda anty kubra tace
Ya mugun daga mata hankali sosai

Tace kai ina karya ne wallahi ba zaki taba haihuwa gidan nan ba matsuyaciya

Meenat ce tafito daga part dinsu
Dauke da glass cup a hanunta na drink

Sai mummynta na hawaye
Sai Takaraso a tace meyafaru kuma mummy

Suby tace wannan 'yar talakawar ce wai cike ne da ita

Meenat batasan sanda tasaki cup din hanunta ba
Tace karya takeyi wallahi bata isa ta haifi wannan Dan iskan cikin nata agidan nan ba

Tayi hanyar dakin husnah suby tayi saurin tarota tace inazaki

Meenat kibarni naje anty suby wallahi sai namata dukan dazaisa cikin yazube inga tafadi

Suby tace idan kikayi haka daddynki zai dauki babbar mataki akanki

Kibari mubiyo musu tabayan gida
Ina tabbatar muku husnah bazata haifi cikin nan ba

Nan dai suby taringa basu shawarwari

Husnah takawo wa anty kubra gashashshan namar kaza da drink saikuma fruit

Ta zauna kusada anty kubra
Anty kubra tace anya wannan husnah ummace kuwa
Kinganki kuwa kinyi fresh dake kaman ba mai cikiba

Husnah tayi murmushi kafin tayi magana wayarta yayi kara tana dubawa taga Prince ne cikin shagwaba ta amsa sallamar

Anty husnah baki kawai tasake tana kallon husnah yadda tazage tana soyayya da mijinta ba alamar kunya cikin kawarewa da iya wa Hakeem yace to ya antyn mu
Husnah tace LA ya akayi kasan tazo yayi murmushi yace karkidamu ki isar min da gaisuwa na kafin mukaraso yanzu

Husnah tace kukaraso kaida wa kuma
Yace naki fada yayi murmushi yace bani baby na muyi hira naji abinda take bukata

Murmushi husnah tayi tace anty nan
Yace kibani baby muyi hira
Taga dagaske yake
Tayi murmushi ta kashe wayar

Sai da tagama taga anty kubra tazuba mata ido

Kubra tace anya wannan Husnar ummace kuwa towai Husnah ina kunyar ne wannan soyayya haka
ai sai kisa yakasa aikin

Husnah tayi murmushi tace anty kenan wallahi tun inajin kunyar ya Hakeem wallahi har na daina

Dan shi baruwanshi ko agaban waye baya kunyan nuna min soyayya

Anty kubra tayi murmushi tace to ai gwamma dai da kika nuna mishi kema kwararriya ce fanni kula miji kar kiyarda kece zaki kunyar wasu
Chapter 11 · 0% Book details