← Book details Akwai Lokaci Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 15 OF 19

Sashe 15

Akwai Lokaci Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Husnah tace banida bakin dazan gode maka akan yadda kake kula da mu gabadayanmu
Allah yakara arziki my Prince

Hakeem yace nifa banason wannan godiyar da kike min
Dan komai nawa nakine kina da damar dazakiyi yadda kikeso da komai nawa nariga nasa hanu

Nan dai suka shirya sukatafi shopping

Sai dare suka dawo

Washagari meenat tace itama zata Hakeem yace tashirya suje suyi kwana biyun

Husnah taji dadi kuwa dazuwan meenat

*****

Sun isa kano wurin la'asar
Ya shamsu da anty kubra suka taresu suna murnar ganin su

Meenat tadurkusa har kasa tagaida ya shamsu
Yace a a mutanen Kaduna yasu mummyn meenat tace lafiya kalau suke

Husnah tace kai anty kubra wannan irin kyau wallahi komawa baby kikeyi

Anty kubra tayi murmushi tace keba kiga yadda kika koma ba ko

Anty kubra ta ruko hanun meenat tace meenat sannun dazuwa kinji husnah ta tareni dashirme hanun meenat rike da hanun anty kubra suka Shiga

Umma tayi murna sosai da zuwansu

Abinci kala kala a ka saukesu dashi

Meenat dai takasa sakewa kwatata

Washagari husnah nazaune a falo itada umma meenat da anty kubra kuma suna kitchen suna abinci
Sungama suka jera komai kafin nan kuma kowacce tawuce wanka

Meenat dakin dasuka sauka tawuce
Itada husnah ne dakin anan suka sauka

Bayan salar isha abba da yashamsu sunshigo husnah sai shagwaba takeyi yadda ranta yakeso kowa naji daita

anzauna za afara cin abinci
Sai umma tace Husnah tashi kikira amina tazo taci abinci itama cikin mutane
Narasa takasa sakin jikinta ai komai yawuce tunda anzama daya

Husnah ta tashi zataje kiran meenat

Kubra tace zauna abinki zankirata

anty kubra ta na Sakai cikin dakin tadawo dabaya tatsaya turus

Kunnenta takunnenta sosai

Meenat dabatasan anshigo ba tace ya Allah narokeka kacire min son Wanda nasan bazan taba samunshi ba ya Allah nasan ya shamsu yafi karfina
Ba abinda zaiyi dani yana da mata kamar wacce yake da ita

Nasan yafi karfina ya Allah kai kajarrabeni da kaunarsa Allah ka yaye min

Allah natuba Allah kacire minshi acikin arayuwata ya Allah

Tana kuka mecin rai

Anty kubra kasa jurewa tayi cikin tsananin tashin hankali tajuya zata koma dabaya

Sai kuma tayi tunanin to idan antambayeta mezatace

Sai kawai ta daure tashiga dakin aikuwa meenat naganinta tace sannu anty

Kubra tace yauwa kanwata kifito muci abinci kinji

Meenat tayi murmushi tace to anty

Da daddare anty kubra kasa bacci tayi tana ta tunanin abinda kunnenta yaci mata

Can tayi tunin haba kubra kiduba fa gidan nan basu da wadatar yara umma zataso taga 'ya'yan shamsu amma bawanda yataba maganar rashin haihuwarta kowa nuna mata kauna yakeyi

Kuma tabbas sunje asibiti an tabbatar itace da matsala

Dan meyasa zata zama meson kanta dayawa Yakama itama tarama hallacin da mijinta da iyayenshi suke mata arayuwa

Kuma ai meenat ta shiryu ta tabbatar zasuyi zama na girmama juna

Sai dai kuma ta yaya zata hada wannan Abu bayan tasan balalle bane su amince mata

Juyawa tayi takalli yaya shamsu dayake baccinsa

Take tausayinsa yakamata tasan yana balain son yara
Kuma gashi ita bata halin bashi wannan farincikin

Tana da yakinin ya shamsu bazai taba juya mata baya ba koda ya auri meenat ta Haifa mishi yara

Tayi murmushin dole tace meenat Allah zaibaki abinda kikeso fatana Allah yasa muzauna lafiya

Kubra ta Dan taba ya shamsu kadan yatashi yace a a honey mekike yi baki kwanta ba

Tace katashi muyi magana Dan Allah

Dayake ya shamsu yana matukar bawa kubra muhimmanc acikin rayuwarsa

Yatashi yace Allah yasa lafiya kubra tayi murmushi tace
Alkairi nema

Next page

Your comment is needed Fan's

Love you all

📝📝📝📝📝📖📖📖📖📖
[06/05, 11:18 AM] UMMU AFAN 🌹: 🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗
🎗🎗
🎗
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM

Story & written
By
The special writer

UMMU AFAN

🖊🖊🖊🖊🖊🖊📚

🌹FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION🌹

🌹🌹 (F.C.T.W.A)🌹🌹

🌹HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION🌹

🎗I DEDICATE THIS PAGE TO YOU MAMAN MUFIDA
Ina alfahari dake wallahi kina kasheni da wannan nice comments din naki Allah yabar kauna🎗😘😘😘😘😘

🎗AKWAI LOKACI 🎗

🎗PAGE 153 to 155🎗

YA SHAMSU yace inajinki honey

Kubra tace wallahi inasha awar naga yara agidan
Koda kuwa bani zan haifesu ba inason ganinsu

Ya shamsu yace bangane mekike fada ba kubra

Kubra tace nazauna nayi tunani
Halaccin da kukayi min a rayuwa Dan me nima bazanso abinda zai faranta ran ka Dana su umma ba

Wallahi koba afadamin ba nasan yadda kakeson yara
Koba kaiba ma su umma fa girma ya kamasu zasuso suga yaranka kafin sukoma ga mahallincinsu

Saboda son dasukeyi min da nuna kulawa agareni yasa bantaba jin umma tayi magana akan rashin haihuwataba

Kuma nasan dole abin zai dameta

Kaga idan har nacika masoyiyarka ta gaskiya dole ne nayi kokarin ganin farin ciki arayuwarka idan har INA da damar hakan

Ya shamsu yace duk meyakawo wannan maganar kubra mekike nufi kenan

Kubra tace ina nufin kayi aure Dan Allah muna bukatar muga yara acikin gidan nan
Dan Allah karki yadda da bukatuna
Kayi tunani mai kyau akan magana bakai zaka duba ba su umma zaka duba

Ya shamsu Wanda mamakin kubra yakeyi tubaran
Yace anya kina cikin hankalinki kuwa kubra
Meyasameki

Bantaba ganin macen datake jawa kanta kishiya ba saike
Kokuma kindaina sonane yasa kike fatan nakawo wata cikin rayuwarmu

Please banason sake jin wannan maganar a bakinki Dan Allah bana samum sabani dake amma akan wannan zan baki mamaki

Kubra tasauka kasa tazuba gwiwarta akasa tana kuka tana rokanshi akan yacika mata burinta

Yaga abin nata ma dagasake ne yafita daga dakin yakoma dayar dakin yasaka key

Kubra kuwa ganin yabar mata dakin
Yasa tama rasa tunanin dazatayi

ahaka bacci yadauketa rana nafarko dasuka fara raba shimfida kenan da mijinta

Washagari da safe bayan sungama karyawa meenat tace zata ta kwanta Dan tana komawa baccin safe falon yarage daga husnah sai umma sai anty kubra

Umma ta lura da kubra yau kaman bata lafiya takasa yinshiru tace khadijah lafiya kuwa

Kubra tayi murmushi tace umma ina da magana amma keda Abba nakeson magana daku

Umma da husnah suka kalli juna Dan basu taba ganin kubra cikin wannan halin ba

Umma tace to kutashi mutafi can falon abban naku sai kiyi maganar acan

Tare umma da kubra suka wuce sukabar husnah da damuwar rashin sanin maganar da kubra zatayi

Can husnah tace kodai fada sukayi da yaya shamsu
Tace haba ya shamsu me anty kubra zata maka da har zai kasata adamuwa irinhaka

Haka ta tashi ta wuce part dinsu anty kubra tanazuwa tasamu ya shamsu a falo yana kwance fuskarshi nakallon sama husnah tashiga

Husnah tayi sallama ya shamsu ya amsa tare dayin yaken dole

Husnah tace ya shamsu wai meke faruwa kaida anty kubra ne

Yatashi da sauri yace tafada miki wani abunne

Husnah tace a a amma yau bata cikin walwala kuma tace tanada magana da Abba

Ya shamsu yace ita kubaran yanzu tana ina husnah tace suna falon Abba

Dasauri ya shamsu yafita yayi hanyar falon Abba yanazuwa yace kubra wai meyasa bakya jin maganane Dan Allah

Abba yace karaso mana ubana yafi nakowa sham sudden
Ya shamsu yashiga yasamu guri yazauna

Abba yayi gyaran murya yace matarka tasamemu da wata magana wacce da bamu amince da itaba sabida ganin rashin dacewar hakan amma kuma tafimu hujja da da dalilu masu yawa

Ya shamsu yadaga kai yace Abba yanzu inbanda shirme irin na kubra ta ina zanfara Neman matar aure

Abba yace ai har matar ma tariga tasama maka ita

Dasauri yadago kai yakalli kubra wacce tamaida kanta kasa

Yace bangane tasamamin matar aureba
Abba yace wannan yarinya amina

Ya shamsu yace amina kuma wacece wannan kuma

Husnah dake bakin kofa tace meenat kenan

Duk suka kalleta anty kubra tace a itanake nufi
Na tabbatar a yanzu duniya ta mata karatun tanutsu zata zauna lafiya

Kuma meenat bakowa takeso sai yayanki
Tana son ya shamsu kobadan itaba ai zamu duba babanta da kakaninta tashiryu duk abinda tayi da ina da tabbacin yarinta ce amma yanzu hankali yazo mata Dan Allah ke ma husnah kifahimce ni

Husnah tace yanzu anty kubra dakanki kikeson janyo meenat ajiki bayan munsan ta musan halinta

Anty kubra tace sanin da kika ma kuma kema na San kinyarda meenat ta canja

Abba yace duk kuzauna mufahimci juna

Nan Abba yayita musu nasiha
Sannan kuma yanuna musu faidar yin abinda kubra tace

Umma tace gaskiya khadija samun mace irinki awannan zamani maison farinciki Wanda take taredashi koda ita zata rasa nata farincikin

Kai kuma shamsu idan wannan aure dazaka yi zaisa kubra tayi farinciki to kaje kanemi auran amina

Abba yace wannan banyarda kabata wa kubra ba shamsu a rayuwar ka mace ce tagari
Wacce samun irinta a rayuwa sai antona

Kubra tace nagode dakuka fahimceni

Abba yace Allah yamiki albarka yabaku masuyi muku abinda kukamana

Anty kubra ta tashi tafita

Abba yakai kallonshiga shamsu dayayi suman zaune

Abba yace abinda yakamata yarinyar tayi a yanzu tabbas lokaci yayi dayakamata karamawa kura aniyarta ba abinda zamuce ga wannan yaro Abdul Hakeem da iyayensa saidai Allah yasaka musu da gidan aljanna

Kaduba yadda suke kula da 'yar uwarka ba abinda tanema tarasa

Baka tunanin hanyar dayakamata kaima kamishi wani Abu dazaiyi jidadi a rayuwarshi

To Allah ne yabaka damar dazaka sakamasa shima shine ka auri yarinyar nan amina kariketa kamar yadda yake rike maka naka 'yar uwar

Nan dai su Abba sukayi ta fahimtar dashi faidar yin hakan

Da daddare kubra da yashamsu sunyi shirin kwanciya

Sunkwanta kubra kallon kayan da akaturo mata nasiyarwa ne wata kawarta ce take kawowa daga Dubai

Ya shamsu yakarba yana kallo shima yace kai amma sunyi kyau wanne kikazaba

Kubra tayi dariya tace daga ganin Abu a waya kuma saina hau zaba kawaidai ita tafara nunamin ne inga irin kayan data saro kuma nagani kaga nace mata ma sunyi kyau sosai

Yace hakane to ninace kizaba muku masu kyau keda asmau

Kubra tace a a fa wallahi bada niyar kasayamin nabude kaganiba kawaidai nabudene Dan nasan ta turo sai dai nazabawa

Husnah dai tunda kayi niyya saya

Ya shamsu yace kizaba muku banason musu

Kubra tace to ai kabari muji kudinko
Ya shamsu yace bakyajin magana ko

Kubra tayi murmushi tace shikenan angama rankayadade
Chapter 15 · 0% Book details