← Book details Akwai Lokaci Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 4 OF 19

Sashe 4

Akwai Lokaci Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Yace 'yarkice she is my daughter
Tana aure a kano sunyi tafiya da mijinta

Zakiganta wataran ,ita kadai Allah yabani

Kidage nan da nine months kibani baby kaman ke

Husnah ta boye fuska

Ta yi saurincewa muje kaci abinci

Hakeem yashirya cikin farar jallabiya

Kafin yaja hanunta sukayi dining

Sosai yaci abinci amma fa saida yatabbatar takoshi kafin yafara nashi

Tundaga kan dining din wasa yafara canja salo

Cak yadauketa zuwa bedroom Daga nan kuma sukayi bathroom Dan yin alwala

Hummm

Next page

Your comment is needed fans

Love you all👏👍🤲😘😍❤
[05/05, 8:59 PM] UMMU AFAN 🌹: 🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗
🎗🎗
🎗
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM

Story & written
By
The special writer

UMMU AFAN

🖊🖊🖊🖊🖊🖊📚

🌹FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION🌹

🌹🌹 (F.C.T.W.A)🌹🌹

🌹HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION🌹

🎗I DEDICATE THIS PAGE TO YOU sis Fatima Umar ina alfahari dake wajen comments mai Allah yabar zumunci👏😘 (🎗

🎗AKWAI LOKACI🎗

🎗PAGE to116 to 120🎗

DUK wani taimako da uwa yakamata ta wa 'yarta mummy tama Husnah

Ta hada mata hadaddan tea maikauri da farfesun kayan ciki
Yasha kayan sirrin na mata

Ta lura husnah kunyarta take sosai

Sai ta wayance
Tace ai zazzabi ba dadi husnah bama saimunje asibitiba

Zazzabin nan nayanzu ai sai a hankali
Sannu kinji

Ganin kaman mummy bata gane ba yasata saki jikinta taci abincinta

Tasake komawa bacci a gadon mummy

Ranar dai Husnah taga tattali da gata

Kuma alhamdullila gaskiya taji dadin jikin sosai

Mummy taki tabarta tafito ma ko falo

Laila kuwa tana farfadowa tafara kuka jikin hajiya rukayya

Tana shiga uku hajiya shikenan sun rabani da Abdul

Hajiiya rukayya tace audama sabodashi kike kuka asararrariya

Ni ma dauka saboda dukiyarsa kike kukar wani so ana zaune kalau

Nan sukayita mata fanfo

Hakeem zaune a office sai Ahmad yace amma gaskiya natayaka murna wallahi

Dasamun kan madam yanzu zaka bani labarin yadda zama da mata biyu yake konima zansamu nakara

Hakeem yayi murmushi yace baka da hankali kai kuma wani aure zakayi sha'awar yi

Ahmad yace wallahi ba abun da Aisha ta rageni dashi kawai dai sunna nakeson cikawa

Hakeem yace tonidai baruwana

Nan Hakeem yadauki wayarshi yakira mummy yace mata yajikin Husnah tace
Bansaniba marakunya

Hakeem yayi murmushi yace haba daliba toshikenan ina babyn

Mummy tayi murmushi tace tana bayana

Hakeem sosai yayi dariya Dan yasan mummyn shi da caka magana

Mummy takashe wayarta

Ahmad yace waye balafiya

Hakeem yayi dariya yace Husnah

Yana murmushi ya lumshe ido kawai

Ahmad yace wallahi young Prof kabimusu 'ya a hankali fa she is very young fa

Hakeem yabude idonshi tar yace innan bita a hankali ai bazata saba da mijinta ba kullum tsorona zataji

amma intariga ta saba she is always welcome me

Ahmad yace lalle ma mutumin nan
Allah yataimaki 'yar mutane daba ita kadaibace

aida ka karar musu da yarinya

Hakeem yayi murmushi yace bazaka fahimta bane

Nifa Allah Allah nake ma daddy sugama ganawar nan da shugaban kasa yazo mutafi gida

Ahmad yace taresuke da daddyna ko

Hakeem a suna tare Ahmad yace OK nima barinjirashi kawai muwuce tare

Ahmad yace wallahi kabar yarinya nan nayau dai karka koma Hakeem yayi murmushi yace caf

ai hakan ma ba zai yiwuba

Tashi muje karani nasiya mata waya
Nata ya fashe

MEENAT kwance kan bed dinta suna waya da antynta suby tana ta bata labarin abinda kefaruwa da uwarta

Meenat ta fashe da kuka tace meyasa daddy zai ma mummy haka duk da dadewar dasukayi tare saboda yayi are shine zai wulakanta ta

Suby tace kedai bari kawai ai daddynki ya canja hali sosai

Kuma duk ba laifinsabane akan wannan 'yar figigiyar yarinyar da yakawo ne

Kokefa zaki girmi yarinyar nan

Meenat tace nashiga uku wallahi nazo gidan nan saidai daddy yazaba ko mu ko shegiyar yarinyar

Suby tace gaskiya dai kam tunda ke 'yarsa sace ai watakila yaji maganarki tunda ai duk haukarshi bazai zabi mata yabar 'yaba

Meenat tace munkusa da wowa muna sauka a kano zanyi Kaduna inzo karuwar da ake wa mummyna wulakanci saboda ita

Bayan sunkashe wayar ne
Meenat tacigaba da kukanta

Ita abin ma yamata yawa ga wulakancin da bashir yakemata

Dan idan baidaketa sau biyu to zaikai uku kullum

Baya cin abincinta baya hira da ita

Inya zauna bashida magana saina Asmau Asmau

Tana cikin tunaninta bash yashigo

Yana ganinta yadauko ruwa mai tsananin sanyi a fridge ya kwarama ta tashi ra wan jiki

Tace Dan Allah uncle menamaka ka tsanani haka auren soyayya mukayifa bana kiyayya ba

Bash yamata wani matsaya cin kallo yace wallahi bansan ya akayi har nawa masoyita wulakanci saboda jaka irinki ba wallahi

Ke wai dan uwarki ma ya akayi har naji banason ganin kowa saike ne har na aureki na bar asmau

Meenat ta yi tsilli tsilli da ido

Yace ba magana nake mikiba bazaki ban amsaba yashakota idon meenat yafito tace wallahi ba abinda namaka

Bash yasaketa yace wallahi duk ranar da na tabbatar da abinda nake zargi tattare dake zanbaki mamaki

Mutum daya nakejin kunya shine babanki
Mutumin kirkine

Da Dan uwarkice da kakanki da na Dade da kada ki gida wallahi

amma yanzu zanmiki uziri har na tabbatar da zargina akanki tukun

Maganar auren da babban ki yayi audole yayi aure indai mata irin uwarkice saikace akuya namaga kokarinsa da ya iya hada jini da dabbar matar

Cikin tsawa meenat tace ya isheka haka bashir kamin komai amma karkasa uwata aciki

Kafin ta rufe baki bashir yakai mata duka abakin fas

Aikuwa ta kwalla kara saboda azaba

Yace kuma kifara hada duk wani tsummo karanki

Sati maizuwa zamu koma gida

Yasa kai yafita abinshi

Sosai amina take kuka ba mai rarrashinta
Dadin data jima sati maizuwa zasu bar kasar
Zataje takakkarya wacce tayi kasadar zama kishiyar uwarta

***
Hakeem da daddy sukayi sallama suka shigo

Mummy da Husnah suna hira a falon
Husnah tagaida daddy ya amsa cike da kulawa

Tareda mata yajikin Hakeem kuwa kureta yayi da kallo Dan sake canja mishi tayi wuni daya kawai

Husnah kuwa tana gaida Hakeem tayi sama dakin mummy abinta

Tana shiga bedroom din mummy tafada kan bed abinta

Hakeem kuwa suna gama cin abinci yaki tafiya har daddy ya haura sama

Yazama daga shi asai mummy hafsat mumme tace wai bazaka je ka kwanta bane

Hakeem yasosa keya yace mummy tafito mutafi mana

Mummy ta harareshi tace da tare kuka shigo
Tariga tayi bacci katafi kawai abinka

Hakeem zaiyi magana mummy tace kaga nikam saida safe indan kafita kaja min kofa

Hakeem badan yasoba yaja kafarsa yayi part do shi

Yana shiga ya tarrar da suby da Laila sunkasa sun tsare

Dama abinka da wanda yake wuya

Yanashiga yafara musu masifa
Yace waiku bakuda falo ne kullum kuna falona saboda tsaban fituna ko

Laila tace au dama akwai inda aka mana iyaka dashi ne agidan

Ya kalleta ya balla mata harara

Ya haura sama

Suby ta kalli Antin tata tace yaufa abin ya motsa miskilancin

Laila ta tabe baki
Hakeem bayan yagama shirin kwanciya

Ba abinda yake tunanin husnah
Da irin farin cikin dayasamu tattare da ita

Wayar da yasiyo mata yadauka yacire yasama a acaji Dan yacika wayace metsadar gaske

****

Washagari da daddare karfe takwas na dare bayan sungama ma dinner

Mummy ta haura sama gurin husnah tace

Tace kinkunta ne husnah tace a mummy

Mummy tace Allah yatashe mu lafiya kafin husnah ta amsa wayar mummy yayi kara taduba taga Hakeem

Nan dai mummy tayi murmushi bayan sungama wayar ta kalli husnah tace kije mijinki na kiranki wai yasayo miki waya

Husnah gabanta yafadi ras tace mummy yabari gobe zankarba
Mummy tace kedai jekikarbo kidawo kiyi kwanciyarki

Husnah tace to mummy tafita zuwa falon mummy baya falo ta wuce sashinsu Dan tasan yanacan

Tana shiga taga su Laila da suby suna kallon Hausa film

Tace sannunku

Duk suka kalleta suka buga mata tsaki

Husnah bata bitakansu ba ta huce zuwa saman gurin kiran mijinta

Suby tace anty yau bakwanankibane naga wannan 'yar talakawar ta haura

Laila tace kwarai kuwa barinje naga ikon Allah

Husnah tana shiga bedroom din taganshi kwance daga shi gajerar wondo

Yana danna waya ganin shigowarta ya kura wa mata ido itadai bata son suhada ido

Tanemi gefe ta zauna tace gani yaya

Yatashi ya ajiye wayar agefe
Yakamota yace wai guduna name kikeyi ne baby
Husnah tayi shiru yace bazaki magana ba ko

Kafin husnah dake kwance kan kirjin Hakeem tayi magana Laila tashigo dakin ko sallama babu

Hakeem yace o my GOD wai yaushe zakiyi hankali ne

Laila bance karkisake shigo min daki a wannan lokacin ba

Laila tace taya za ayi nayi tunanin yin sallama bayan kana kokarin cin amanata

Hakeem kalleta yace kamanya cin amanarki dawata kika kamani koda matata

Tace duk da matarka ce ai yakamata kasan yau kwanana ne

Yace OK dama abin kenan

Saikije kifara kirgawa daganan zuwa 5 day's saikufara raba kwana Dan ita yanzu take amarya Kinga kuwa sai ta min 7 day's kafin kufara raba kwanan

So fita kiban waje ganin da gaske yakeyi
Ta juya hade da banka wa wa husnah harara

Ta banko kofar tayi waje
Hakeem yabita da kallon takaici

Ya dawo kan husnah yace nadawo kanki kekuma meyasa jiya kika gudu dakin mummy

Husnah tace nima fa gigin baccine bani najeba

Hakeem yayi murmushi yace ko

Tadaga kai sama ya dauko wayarta da yasayi mata yabata cikin nuna jin dadi da wannan kyautar da yayi mata tace Allah yakara budi

Bata gama godiyar ba ya hade bakinsu guri daya yashiga sarrafata

Duk yabi yagigitata da salon soyayyarsa kafin yatashi yaje yasamusu key a can kofar falon

Yauma fa basauki husnah takwashi kashinta a hanu saidai da sauki zafin bakan nafarko ba

Sosai tasha tattali itakuma sai shagwaba take zabawa son ranta

Da asuba bayan yadawo daga sallar asuba sunyi karatun alkur'ni maigirma

Yajata kan bed yace baby kinbani komai arayuwata ba abinda zance saidai Allah yabar minke mutukaraba
Yadauko wasu files da takardu acikin yace karba wanna tace nameye wannan

Yace tukwicin first night dinki ne

Tabude taga takardun company ne da takardun gidaje guda biyu

Saikuma mukullin motoci guda biyu

Sai kuma kufi a account har Naira million goma

Husnah ta tashi daga kwanciyar datake
Chapter 4 · 0% Book details