← Book details Akwai Lokaci Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 6 OF 19

Sashe 6

Akwai Lokaci Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tace baka isaba sainaji lafiyar 'yata

Hakeem yayi murmushi ya Sosa keya yace bata lafiya

Daddy ashsha yajikin nata

Hakeem yace dasauki dama zazzabine kawai yamasauka bacci matakeyi

Mummy tayi salati tareda maka wa prof harara tace ashe baka da hankali zazzabinne kawai

Barinje nadubo 'yata

Ta wuce su tayi part dinsu surukanta

Tana shiga falon tagansu sunata ciyeciye ana shewa

Tace to su yaya rukayya ne agidan namu

Suka washe baki sukace sunzo duba suby ne bataji dadi ba

Mummy hafsat takebe baki tace to Allah yasauwaka

Tawuce zuwa kofar Husnah taji ta a kulle da key

Hajiya rukayya tayi sauri tace aibata sauko daga samanba nima yanzu nakeson nayi magana nace wannan irin bacci ai yayi yawa

Mummy hafsat tace au anan ma kuka kwana kenan da harkukasan lokacin data haura saman

Duk sukayi shiru kaman ruwa yacinyesu

Mummy hafsat tace Allah yasawaka zata hau saman

Saitaji hajiya rukayya nacewa waike hafsat mekika dauki kankine karfa kimanta yaron nan nima danane kamar yadda yake danki

Saboda haka Dan Nazo gidan Dana bazaki zageniba

Mummy hafsat tayi murmushi tace kudai abin kunya baya karemuku wallahi
Haba mutane saikace wasu hallittu nadaban

Hajiya rukayya ta taso cikin zafin rai tadaga hanu zata mari mummy hafsat

Hajiya suwaiba tace ke rukayya karkikuskura kimareta
Tasauke hanunta tace kinci darajar hajiya dayau natsinka miki Dan innuna gaba nake mijinki ma balleke

Mummy hafsat tayi murmushi tace dakinsake hanunki jikina dakingane kuskurenki
Bazan kiraki da shasha ba
Saboda darajin mijina dasainace shasha kawai

Tayi wucewarta saman tabar hajiya rukayya da cizon

Laila tace wallahi abin matar nan fa yafara isata ya agabanmu zata zagi uwarmu

Hajiya suwaiba tayi gyaran murya tace duk kubarta aiduk Takamarsu dai 'Dan ne aiko
Zamuyi gaggawar kawardashi kaman yadda mukawa kakarsa amina

Daga kunga sunshigo hanunmu saimu maidasu bayinmu
Hakadai suka ta kulle kellensu

Mummy hafsat tana shiga falon direct bedroom tawuce India take tunanin zata same husnah

Tanashiga taganta kwance tana bacci mummy takarasa kusa da kanta ta taba goshinta taji zafi rau

Mummy tace subhanalla ashejikin yayi zafi haka mazata shi mutafi asibiti

Husnah cikin bacci taji kaman
Muryan mummy

Tana bude ido kuwa ta tashi da sauri tace sannu mummy wallahi rana tayi hakaba

Mummy tace kedakike fama kanki zakifara magiya kuma 'yata tashi maza muwuce hospital yanzu Dan gaskiya yayi zafi sosai

Husnah bata son jayya da mummy shiyasa ta sauko duk da taso tayi tafiyarta normal amma hakan ya gagara

Abinda mummy zargi yatabbata kenan

Dama taso tazargi ba abinda yashiga tsakaninsu
Saboda yadda take muamalarta

Cikin farinciki mummy takamata tace sannu kinji 'yar albarka
Allah ya albarkaci rayuwarku yabaku zuri' masu albarka

Itadai husnah ko kallon mummy takasayi saboda gani take mummy tasan me yafaru da ita kenen

Ita rikemata hanu sukayi kasa da ita aikuwa mutan falon suka zubo masu ido cike da tuhuma

Mummy kuwa dagangan take Dada Jan husnah ajikinta
Tana mata sannu

Suna fita Laila tace nashiga uku kardai yarinnyar nan cikine da ita

Suby tace kema dai anty dawani magana
Yarinyar da kullum a dakinta take kwana yaune fa kawai suka hada gurin kwana

Laila tace nashiga uku na mutu na Lalace

Shikenan aikinmu ya ware

Wallahi duk atunanina bazai kwana da yarinyar nan ba saboda alkwarin da malam yayamana

Nan Laila tafadi kasa sumammiya

Duk sukayi kanta

Next page

Your comment is needed fans
📝📝📖📖📝📝📖📖
[05/05, 8:59 PM] UMMU AFAN 🌹: 🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗
🎗🎗
🎗
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM

Story & written
By
The special writer

UMMU AFAN

🖊🖊🖊🖊🖊🖊📚

🌹FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION🌹

🌹🌹 (F.C.T.W.A)🌹🌹

🌹HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION🌹

🎗I DEDICATE THIS PAGE TO YOU sister Sameera (masha Allah) Allah yabar zumunci ina alfahari dake wallahi keep it up🎗

🎗AKWAI LOKACI 🎗

🎗PAGE 121 to 130🎗

HUSNAH ta kalli Hakeem daya Zuma mata ido yana kallonta

Tace kayi mamakin ya akayi nasan Kaine ya muallim dina ko

Tayi murmushi kawai ta tashi taje inda ya boye akwatinshi tafito da fuskar (masks) kenan tafito da zoben data bashi

Sannan uwa uba Nokia din shi meroba

Husnah tayi murmushi tace kaga nagansu
Kuma yana son kafada min komai saboda nasan komai

Dan nakaranta a diary din ka
Ina sonka mijina wallahi inasonka kuma nasan kaima kasan haka saboda haka niba yaya Hakeem na aura ba

Ya muallim na aura ta juya baya
Tana murmushi

Hakeem yayi murmushi dan tariga tagama dashi yana daga zaune yakasa cewa komai

Ya tashi yakamota yazaunar daita kan cinyarshi
Yace nagode da kaunarki agareni Allah yamiki albarka
Cikin shagwaba husnah tace ameen

Yace kinsan wani ta girgiza kai yace nabaki rayuwata Husnah kiyi yadda kikeso dani
Nikam kingama mallakar zuciyata

Zaiyi magana Husnah ta tashi daga kan cinyarshi da sauri tawani maka mishi kallon so
Tace OK saiyanzu ma kabani rayuwarta ka
Dacan ma kenan ba dagaske kake ba ko

Hakeem yace ani tunranda nafara ganinki a school dinku kikagama dani

Husnah tayi murmushi dimple dinta suka lotsa sosai
amma dai ka rage wadan nan kyautar dan Allah wallahi sunyi yawa

Yace OK sunmiki kadan ne barin kara miki

Husnah tayi saurin kama kunnenta tace a a wallahi sunma yi yawa ne

Tace amma kai zaka rike a gurinka ko

Yace a a sai dai zanbaki shawara
Husnah tabashi hankalinta

Yace kibawa yaya shamsu ya rinka juya miki su anasa kasuwancin

Cike da mamaki. Husnah tace ya shamsu yafara business ne

Hakeem yace a a idan yagama makaranta nake nufi

Tace to nagode yayana

Hakeem yashafi kanta yace banason godiya kamata yayi idan namiki
Abu nizan gode miki dan kincancanta

Hakeem dai bai bar Husnah haka ba sai dayasake hutawa sukayi wanka

Husnah takalli Hakeem dake saka turare tana kallonshi kuwa shima yana juyowa aikuwa suka hada

Tayi saurin saukar danata

Murmushi Hakeem yayi ya ma daf da ita yana kokarin cire towel din dake jikinta
Wai zai shafa mata

Tace a a nida kaina zansha fa Hakeem ya lakace mata hanci yace waya fada miki zanbari idan ina tare dake kiyima kanki wani Abu

Zanbarki kiyi aiki ne kawai idan nizakima dan kisamu lada
Daga yau nizan miki wanka nizan shafa miki mai nizansa miki kaya

Abinkwai da zaki kimin kwalliyar fuskarki duk da kefa da kwalliyar ki aka haifeki

Husnah tayi murmushi tayi fari da ido tace OK aikinka yafara yanzu

Hakeem yace yes madam tace to kayan dazansa zaka debo min a bedroom dina

Hakeem yayi murmushi yace angama madam ya wuce yafita

Yana fita Husnah tayi murmushi ta tashi dasauri kafin yadawo tagama shafa manta dama wayo tamishi

aikuwa Hakeem da yadawo yaga tashafa mai tana mishi dariya yace OK wato wayo kikamin ko aikuwa

Sai nabaki punishment tunda kin kar ya min doka

Kafin Husnah tayi magana

Hakeem ya hada bakinsu waje daya
Takasa kwace kanta karshema dai cak yayi da kan bed tana bashi hakuri

Ina baijita ba yayi nisa sosai

Sai daya dawo hayyacinsa kafin yarungumota yace duk randa kika sake shiga min aiki ko to punishment dinki kenan

Husnah dai ta gurzu baki ya mutu

Tana kwance kan kirjinshi

Yace barin hada mana ruwan wanka
Husnah ta rufe ido kaman tayi bacci ya leka fuskarta yaga a rufe

Sai yayi murmushi shima yadada mannota da jikinshi kafin bacci yayi a won gaba dasu

Sai karfe goma Hakeem ya bude ido
Yaduba agogo yaga har goma

aikuwa ya tashi da sauri dan makara office

Ya je yahada musu ruwan wanka cak yazo yadauki husnah sai cikin ruwa

Ita Husnah abin nashi har mamaki yakebata kokadan baya jin kunyarta

Tare sukayi wankansu yadaukota zuwa kan bed

Saida yafara shiryata cikin wata doguwar rigar shadda Wanda yazabo mata acikin kayanta

Ya feffesa mata turarruka masu kamshi kafin yace maza yi na fuskar da daurin dan kwalin

Husnah ta turo baki tace kai kamin kwalliyar tunda kace karnayi komai
Nima ban iyaba

Hakeem yayi murmushi dan yarin tar da tanuna mishi ya burgeshi sosai

Yace OK gani kikeyi bazan iya ba bari kiga ni zanbaki surprise

Nan fa Hakeem yazage sosai waishi yana mata kwalliyar fuska

Itadai husnah tana ganin ikon Allah

Har yagama yamata dauri shima dai daurin gashi ga yanayinshi

Ya hanata kallon madubi wai sai yagama

Yana gamawa yajata zuwa gurin mirror

aikuwa husnah tana hada ido da fuskarta ta kwalla kara ta kankameshi

Tace nisai ka biyani fuskata
Dariya sosai Hakeem yake
Damshima kanshi yasan yabata mata fuska

Sosai take mishi rigima wai sai yabiyata fuskarta

Saida yagama dariyarshi sannan yadauketa zuwa bathroom ya wanke mata fuska

Kafin suka dawo
Hakeem yace insake miki mekyau ne

Husnah tace wallahi na yafe zanyi abuna

Yace OK tashi maza kiyi nabaki 5 minutes kigama
Kizo kizauna kawai inashiryawa ina kallon kyakkyawar surarki

Murmushi husnah tayi kafin tayi kawalliyarta Hakeem masha Allah kawai yake nanatawa tunyanayi azuciya yadawo afili yadawo

Husnah ta taso tazo gabanshi tahure mishi ido
Murmushi yayi husnah tace yada kallo

Hakeem yakamota yazaunar da ita bakin bed
Yace kinyi kyau mamatata I LOVE

Husnah tayi murmushi cikin salon shagwabar ta tace kardai kasa love yakare fa
Dan nasan kafada yafi a kirga

Hancinta yaja yace ai saidai yakare dan ba ranar da bazakijishi ba abakina

Ya tashi zaifara shafa mai yaga hanun Husnah tarike

Yakalleta tace niban amince inanan kama kanka komai ba wannan ai kina ne banakaba

Sai dai ranar da kake gurin anty na

Shine zan barmata kai amma fa ba wai dan naso ba sai dan yazama dole
Nan kuma tacigaba da samishi kaya
Tabbas tabashi mamaki baizata tana da wannan wayewar ba amma yanzu. Ya tabbatar wa kansa yasan yayi aure

Atare suka fito zuwa kasa bayan husnah tasaka key ta kullo saman Yakama hanunta suka gangaro

Laila ce kwance suna waya da meenat

Dan ta nunawa Husnah cewan itama fa tana da martaba agidan

Tace wa meenat ga ma daddyn naki yasauko
Ta taso jiki narawa tana iyayi itaga mai uban 'yarta

Hakeem ya kalleta yace Bata San layi na bane
Kice takira ni ta layi na

Zaiyi waje husnah taja hanunshi tace haba my one
Dan Allah kakarba bazata jidadi bafa

Kafin Hakeem yayi magana Laila to bakar munafuka
Chapter 6 · 0% Book details