← Book details Zubar Hawaye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 13 OF 21

Sashe 13

Zubar Hawaye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Cikin kuka Aysher tace Fatima inason AHMAD bantaba son wani mutum kamar yadda nakesonshi ba akansa nafara soyayya kuma daga kansa na rufe kofa zan auri Mahmoud ne bawai dan inasonshiba.
Banason Mahmoud narasa kuma bazan iya gujema aurensa ba
Banda wanda zan iya fadawa babban tashin hankalina shina haryau nakasa sanar da Ahmad abinda akeciki ina gudun kar Ahmad yace na yaudaresa.

Kawata baffa akwanaki yana tambayata labarin Ahmad ina fadamasa muna waya sosai dashi amman tunda maganar auren nan yataso baffa yadainamin maganar ina ganin kamar ancanjamin baffa nane Fatima kamar ba baffa na danasani ba a baya.

Banason auren nan kuma bana kinsa bansan meke faruwa ba.

Addua zakiyitayi Aysher nace kidinga addua cikin dare kina tashi kuwa?

Bana iyawa fatima kasawa nakeyi koda nayi niyyar tashi sainaji kamar an daure ni ne saina kasa tashi.
Haka zaki daure shaidan ne ki dage ki maida hankali zaki samu saukin kuncin da kikeji a cikin ranki.

Nagode kawata awannan ranar Aysher sai dare ta fatima tarakata gida Innar fatima tazo tanata basu labarin yawan kayan auren Aysher tare dayi mata adduar zaman lafiya.

Kaya sunyi kyau antsayar da ranar aure sati uku masu zuwa.

Koda Aysher takoma gida daman da alwalarta datayi tun agidansu fatima dan haka dakinta sukashiga suka zauna fatima tanata bata baki tare da kara kwantar mata da hankali.
Suna cikin wannan hali kiran Ahmad yashigo wayar Aysher wanda haryanzu a vibration yake tuntana tsorata idan tajishi a jikinta harta saba yanzu.

Dasauri tadauka tare da sallama kawai saita fara yimasa kuka nan da nan Ahmad ya rikice yana tambayarta lafiya meya sameta.
Itadai takasa bashi amsa sai sheshshekar kuka takeyi
Daga karshe takatse wayar dan batasan abinda zata ce masa ba.

Sake kira yayi dan yaji ko lafiya duk hankalinsa ya dugunzuma Fatima ce wannan karon Allah yabata ikon daukar wayar dan Aysher kuka taketayi.
Sallama fatima tayi kafin tace"Ahmad kawartace fatima ina wuni"

"Lafiya meyake faruwane dan Allah kiyi gaggawar sanar dani hankalina yatashi"

Akwai matsala Ahmad Aysher takasa fada makane aure za'amata saura........

What......innalillahi wa'inna ilaihi rajiun aure kuma dawaye nan da yaushe kikace na mutu nikam Aysher tayaudareni....

Balaifinta bane Ahmad kusan auren dole za'ayimata da Mahmoud Sharrin kishiyar mamanta ne.........

Inji ubanwaye lallai yau saina goge miki wannan shegen bakin naki keda ubanwaye kike waya kikekai sunana munafuka?

Yadikko ko ce kwatsam tashigo dakin batare da tayi sallama ba yan uwantane sukace tazo ta kira Aysher taga kayan aurenta acire wanda za'akai dinki dan fitar biki toh tana zuwa dakin taji abinda fatima take cewa.

Wayar hannun fatima ta kwace ta makata da kasa atake wayar ta ragargaje alamar bazatayi sauran wani amfani ba.

Yadikko tarufe fatima da duka tare da kwalawa yan uwanta kira wai Fatima tayimata sharri kuma tanason ta lalata auren Aysher........

MAMAN HANAN
[10/19, 3:33 PM] Zeetty: [10/19, 2:34 PM] Zeetty: 🍒
🍒🍒
🍒🍒🍒
🍒🍒🍒🍒
🍒🍒🍒🍒🍒
ZUBAR HAWAYE
Page 38-39

©ZAUREN LITTATTAFAN HAUSA

*GODIYA GA DUKKAN MEMBERS NA GROUP DIN MARYAM YAHAYA SUPPOTER'S ALLAH YABAR ZUMUNCI INAJIN DADIN ADDU'ARKU ALLAHU YA AMSA*

Duka yadikko tayima fatima bana wasa ba daman tanajin haushinta batun yauba saiyau ta samu damar huce haushinta.
Dakyar Baffa Usman ya janye Fatima wanda takasa kukama tsabar azaba...

Tambayarta abinda yafaru yayi amman fatima takasa magana sai hawaye daketa fita daga idonta yajuya kan Aysher itama kukan takeyi sosai takasa cewa komai.

Yadikko yatambaya tafara magana cikin bala'i wato Zuwa nayi nasameta tana waya da wani cewar nine natakura ayima aure saboda haka yayi duk yanda zaiyi auren nan kar'ayishi, daman nadade da fada maka malam karaba yarinyar nan da Aysher kaki toyau ga irinta nan tanaso tasa asirinka yatonu abar maka abin tarihi a gari cewar ankusa auren yarinyarka magana ta lalace nikuwa tsabar takaici shine nakama bugunta.

Kai Baffa usman ya kada kafin yace"Baki kyautaba duk da haka kin aikata badai-dai ba baikamata kidauki irin wannan matakin ba yanzu ina wayar take"...

Nuna inda ta yardashi tayi da hannunta salati baffa yasaki kafin yace yanzu wannan wayar mai tsada kika fasa mata saboda Allah toh baruwana kinemi yadda zakiyi kibiyata bayan dukan da kika mata harda fasa mata waya.

Hakuri Baffa yashiga bama Fatima kafin yace muje narakaki gida nabasu hakuri.

Itadai yadikko jikinta yagama yin sanyi dan ganin irin aika-aikar datayi dakuma irin kudin wayar da Baffa yake ambata.

Chemist baffa yafara biyawa da Fatima yasiya mata magunguna kafin yawuce da ita gida
Sallama yasa tayimasa da mahaifinta.

Bayan yafito Baffa yayi masa bayanin abinda yafaru tare da bashi hakuri akan wayar Fatima da aka fasa yace zaibada wani abu.
Cikin Nutsuwa mahaifin fatima yace bakomai Baffa Usman kaima kayi hakuri yaran yanzu kahaifesu baka haifi halinsu ba maganar waya kuwa kabarta munyafe.

Godiya Baffa Usman yashiga yimasa tare da sanar masa gobe zai wuce lagos shima sai biki yarage kwana biyu zai dawo.
Da haka sukayi sallama.

Mahaifin Fatima yana shiga gida yatarar dasu Fatima da Innarta a kan tabarma a tsakar gida neman guri shima yayi yazauna kafin yafara tambayar fatima abinda yafaru dakuma inda tasamu wayar datake amfani dashi batare da saninsu ba.

Cikin Nutsuwa fatima tafara basu labarin soyayyar Ahmad da Aysher dakuma wayar daya bama Aysher taboye saboda kar yaddikko tagani suke waya a cikinta har zuwa yau da abinda yajawo mata shan duka takara da cewa dan Allah baba karka nunamusu wayar Aysher ce karyakara jawo mata wani matsalar abarshi akan nawane.

Allah ya kyauta abinda mahaifin Fatima yace kenan yakara da cewa wannan abu akwai sarkakiya nima nayi mamakin Yadda wannan auren yataso da wuri haka amman koma meye xamuci gaba da addua maganar waya kuwa daman nace masa munyafe kudinta dayace zairage mana Allah mata zabi mafi Alheri.

Ameen suka amsa gaba dayansu.
[10/19, 3:33 PM] Zeetty: 🍒🍒🍒🍒🍒

Bangaren Ahmad kuwa tashin hankalin dayashiga bazai kwatantu ba gashi suna cikin waya da fatima yaji shiru bayan yaji kamar ana musu masifa.

Wani irin sarawa kansa yafarayi daya kara kiran wayar Aysher yajita akashe
Mudansir yakira yana dauka baisaurari abinda yakecemasa ba yafara magana" Nawan yau ba ranar wasa bane pls katafi yola yau kaje aiport kozaka samu flight karna rasa Aysher wai aure zatayi kuma ankusa bansan haka Aysher zataminba Aysher tayaudareni mudan......yakarasa fada cikin raunin murya

Mudansir shima daya gama rikicewa fadi yake"Waye yafada maka haka nawa koma waye karya yake maka Aysher bazata taba yimaka hakaba dan ni shaidane akan irin son datake maka.

Aysher takasa fadamin saboda kukan datakeyi kawartace Fatima tasanar dani itama muna cikin magana da ita naji shiru yanzu nakara kiran wayar akashe dan Allah Mudansir kataimaka kaje kaga abinda yake faruwa nima gobe zanje gurin Ambasador na Nigeria a Makka yasamin baki abani Visa nataho gobe dan Allah Nawan bakaji yadda nakeji ba daman akwanakin nan asan Aysher tacanja daman Jikina yana bani akwai abinda zaifaru ya Allah karka jarabceni da rashin auren Aysher dan komai zai iya faruwa.

Cikin tausayawa mudansir yace"Kayi hakuri abokin ayanzu karfe 9pm bazan samu flight ba kuma ina Abj nida Dad
But nayi maka Alkawari gobe zanbi jirgin safe natafi yola duk abinda ake ciki zansanar maka ka kwantar da Hankalinka Aysher takace babu wanda zairabaka da ita
Mudansir kwantarma da Ahmad hankali yadinga yi saida yaga hankalin Ahmad yadan kwanta kafin suyi sallama tare da cema Ahmad yasha maganinsa na ciwon kai dan yaji yadda Ahmad yake bashi amsa dakyar wanda hakan yanunama mudansir ciwon kan abokinsa yatashi.

Mudansir yana katse wayar yakalli abokinsa da sukayi waya suka hadu a Abj anan mudansir yake fadama abokin nasa cewar gobe zai tafi Yola dan duba wani abu mai muhimmanci.

Shima abokin cewa yayi nima kuwa gobe zantafi yola amman ni mota zanbi da asuba na wuce dan akwai masu farautar rayuwata.

Zaro Ido Mudansir yayi kafin yace"Like seriously Nura waye wannan haka nidaman tunda kacemin kana tare da 'yan siyasa hankalina baikwanta ba"

Anan Nura yalabartawa Mudansir labarin Hon.Mahmoud da Aysher da yadda akayi suka hadu a hoto tare da fadama Nura zuwansa Uku Yola yana neman Ahmad baisamu ganinsa ba amman daga gobe idan yaje yaduba baisamu ganinsa ba yahakura zainemo wata mafita akan auren Aysher da Mahmoud amman Nura yaboyema Mudansir matsalar dake tattare da Hon.Mahmoud.

Rikicewa Nura yayi dajin wannan labari na Nura dan haka yace" saurayin yarinyar abokina ne Nura closer friend dinama kuwa baya kasar yana saudi'a shisa bazaka ganshiba yanzu dan Allah yaza'ayi Alhamdulillahi dagaske ne aurenta za'ayi?

Kwarai makuwa Nan da sati Uku masu zuwa saboda har anbugo katin biki ma.

Nura meye shawararka Hakika idan Ahmad baisamu yarinyar nan ba komai zai iya faruwa ina tausayama Ahmad yasaka yarinyar aransa dayawa gashi jarabawa yakeyi wannan matsalar tasawo kai Nura mutafi dakai mana goben yola.

Girgizakai Nura yayi tare da cewar zuwa yola yanzu bashida amfani tunda abinda zaikaini kenan neman Ahmad ni wallahi banmasan shibane dan na taba ganinsa a gidansu Aysher da daddare amman bangane A.A Hameed bane shege kace ya mato.

Mudansir yace Nura yanzu ba lokacin wasa bane pls meye shawara banason wani abu yasamu Ahmad wallahi.

Anan dai sukayi shawarar yadda zasubi lamarin cikin sauki.

_Masu karatu menene wannan shawarar tasu lokacine kadai zai iya nuna haka_

MAMAN HANAN
[10/19, 5:30 PM] Zeetty: [10/19, 5:21 PM] Zeetty: 🍒
🍒🍒
🍒🍒🍒
🍒🍒🍒🍒
🍒🍒🍒🍒🍒
ZUBAR HAWAYE
Page 40-41

©ZAUREN LITTATTAFAN HAUSA

Bisa ga shawarar dasu mudansir sukayi shida Nura.

Ahmad suka kira mudansir yabawa Nura wayar sukayi magana da Ahmad Nura yace Ahmad yayi kokarin shigowa Nigeria nan da sati daya.

Cikin Alamar karaya Ahmad yace"Nura anhanani zuwa Ambasador dakansa yaki sakamin hannu nataho saboda jarabawar danake zanawa na karshe a makaranta yazanyi dan Allah Nura kataimakamin.

Shiru Nura yayi kafin yace toh zamuyi iya kokarinmu dan ganawa da Mahaifin Aysher kafin Ranar daurin auren amman maganar gaskiya itace kayi kokarin tahowa Dan kafin ranar auren.

Ahmad ya amsa masane kawai batare da hankalinsa ya kwanta da shawararba.

**************

Biki saikara matsowa yakeyi saura kwana goma.
Chapter 13 · 0% Book details