← Book details Zazzafan Rabo Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 12 OF 18

Sashe 12

Zazzafan Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Asheshi wai rashin nuna damuwar da banyiba ashe shi yabashi haushi ,har gida yaxo agaban umma yadinga yimin fada ,wai meyasa bana damuwa da karatu bansan shine gatanaba a yanxoba,wai wasan da nakeyi yanxo yayi yawa,umma tace karabu da ita gani takeyi katakura mata,duk lkcin data samu matsala naga meshige mata gaba ,dan idan tace xata tunkareka karka saurareta ,tunda a iya gaskiyarka kagayamata,akomai Salwa bata daukan abu da muhimmanci ,yace umma abinda yake damuna da ita kenan ,Salwa tanada kokari sosai kawai dai samari ne suke hure mata kunne,nayi nayi da ita akan tabar samarin Jami,a duk " yan yaudarane Amman Salwa taki umma ,tace rabu da ita kaima kaxame hannunka akanta kaima kahuta ,nidai shiru nayi musu yagama surutun tsiyarsa yatafi ,duk fadan da umma takeyi shiru nayi mata sbd duk abinda xankare kaina dashi ba yarda xatayiba ,yawan xuwan da sultan yakeyi har mamaki nakeyi ,idan natanbayeshi sai yacemin wai mommy ce tace yaxo wajen auntynsa suyi hira nace to uncle dinka yasani ,yarike bakinsa aini uncle dina bayasan Na dinga xuwa wajenki SBD yace dukana kikeyi nace to daga yanxo kadainayin abin dukan ,a ranar dai muka dinga nushadi da yaron shi kansa yaron yaji dadin yadda na sakar masa fuska muka dinga wasa da dariya ,itadai umma kallanmu kawai takeyi ,dagyar aka lalla6ashi yatafi gida,umma tace narakashi bakin get din gidan saina dawo ,nace to naxira hijabina narike masa hannu muka fito yana cewa da umma gobema xaixo tace to Allah yakaimu ,adai dai bakin get din gidan mukayi kicibus da Abdul nace to sultan sai gobe yace to aunty da murnarshi ,ya rike ya Abdul yana murna yace uncle meyasa kagudu kabarni yace ai 'kauye Abba ya aikeni kuma nasan whl xakasha shi yasa banje dakaiba ,Amman duk randa xansake xuwa xanje dakai kaji yaron kirkina yamiko masa hannu suka tafa tamkar wasu abokai ,nidai bansan abinda ya shagaltar dani natsaya kallansuba ,sai ji nayi yanacewa nifa bancikasan munafinciba da saka idon tsiya ,nayi saurin yin baya da saurina ya biyoni ke inasan nayi miki gargadi karki sake daukar min yaro kitafi yawon gantalinki,kinsan shi yarona metarbiyane da sanin yakamata ,banasan abinda xai 6atamin tarbiyar yarona dan bakisan dadewar da nayi inayi masa tarbiyaba lkc daya Salwa baxaki lalataminba ,nabude bakina nace dan Allah kayi hkr yanxonma umma ce tace narakoshi da baxaka ganni dashi ba baxan sake shiga huruminsaba dan kawai ance narakoshine dan nima basan yawo nakeyi dashi ba ,danni wannan yaron baya gabana ,yawani juyo a fusace me kike nufi dan baki damu dashi ba kowama bedamu dashi ba, ninasan yarona mefarin jinine dan wata banxa takishi sai akace kowa xai gujeshi mgnar tayimin ciwo to Amman babu yadda xanyi masa sai kawai natafi nabarshi a wajen nashige gida ,nayi kuma alkawarin in Allah yayarda babuni babu rakoshi gida har abada kulashidai yaxama dole tunda konaki kulashi shi xai kulani ,Amman dai agabansa bani babu yaron ko kallansa baxanyiba haka nabarshi yana ta 6a6atunsa shi kuma habu direba saiya kalleni yawani saka dariya shima wlh wataran sainayi mgnin munafincinsa ,umma tafarayinmin fadan dadewar da nayi nace kiyi hkr nida ya Abdul ne wai bayasan yadinga shigowa gidannan shine nabashi hkr ,itadai umma shiru tayimin nasan abinne yabata mamaki koda yake idan aka tunada ai ba abin mamakibane abdul yana shiga gida yawuce toilet yayi wanka yadauro alwalar sallar isha,i yafito yaxura wata farar doguwar Riga sai daukan ido takeyi sai xuba 'kanshi yakeyi ,dan Abdul akwai san kanshi yafito ,duk akan table yasamu mutanan gidan yagaisheda iyayen nasa ,daddyn nasa yanayimasa yagajiyar hanya ai gaskiya yau daddy nawahala da yawa wai ahaka sultan yakeyi min rigimar tafiya dashi ,ai daba 'karamar whl xaishaba ,ya kalleni kaifa Abdul dadina dakai raki ,dan dan wannan tafiyar shiyasa kakeyin mita,meyasa bakatafi da mutumin nakaba aikafijin dadin tafiyar,aini whlar nagudar masa shi kuwa habu direba dake 'katan 'kauyene aiko ajikinsa shi ahakanma rokona yakeyi wai mukwana nikuma naki yadda ,daddy kasanme harfa budurwa yayi ,sai alokacin mommy tayi mgn tace banga laifinsaba ,nace tabdijan mommy bakigafa budurwarba abin dariya duk ta wani daddan6ara abu a fuskarta ni wlh dariyama tabani ,shi kuwa kamar karsu rabu har wani matsar hawaye sukeyi yasa dariya mommy tace yafi Wanda dashi da ita,yashare mgnar yace mommy ina sultan tace aiyayi bacci ko abinci beciga ya kwanta ,daddy ya kalleta da sauri yace kuma kika barshi ya kwanta ,tace aiyacemin yaci agidansu Salwa ,Abdul yayi saurin cewa mommy nifa banyarda da irin abincinsuba bafa wani medadi sukeuiba da ansani ni angayamin naxo nabashi da kaina .

***Takaimin dakowa tace banasan hk Abdul, kasan duk tsiya idan bekoshiba xaiyi mgn,nidai nayi shiru dani dan yanxo sainajawa kaina ,nace umma yana ina tace yana can dakina a kwance ,yashige yadaukoshi a kafadarsa ,yace da iyayen nasa saidasafe sukace su Abdul bakara kokace xaka barmanashi ya kwana ,yace daddy ai baxan iya bacciba ,tace to muma bama nema nidai nayi musu saida safe ,muka nufi daki nacire masa kayansa nasaka masa Na bacci ,muka yi addu,ar bacci narufemu da bargo muka kwanta ,gaskiya a gajeye nake yau sosai nan danan bacci yayi awan gaba dani ,banfarkaba sai asuba shima kiran da daddy yakeyiminne yafarkar dani ,dasaidai namakara nayi saurin mekewa nayi alwala ,nace kodai yau nabar sultan ne dannaga shima agajiye yake ,dasafe munacikin karyawa saga Mlm Abdul nan yagaida umma ta amsamasa da sakin fuska ,yaxauna yace umma danxubamin kunun nan naki medadi wai umma damadara kikeyine ,tace a a da gyada dai yana wanisha a yangance umma tace kebaki iya gaisuwaba ne nasha kunu nace ina kwana danni banasan ganinsa kona sakan dayane yace bargaisuwarki Salwa tunda ba a San ranki kikayitaba saida akasaki bansake kallan inda yakeba naciga da abinda nakeyi ,sukagama hirarsu
Yafice daga gidan ,yanafita umma yadinga yimin fadan abinda nayimasa ,nidai nabata hkr nace baxan sakeba dan nasan umma da mita har saimukai yamma tana abu daya .

Shi kuwa yana komawa gida dan rigimar tasa yana ta nemansa harda kukansa yadaukeshi sukayi cikin gida ,yaxuba masa abinci yaron yasha kunu nifa uncle baxanciba saikagayamin indakaje bakace yawo babu kyauba to kai inakaje ,gidansu aunty naje nagaida umma ainagayamaka gaskiya ko yasa dariya ainasan can kaje kuma wajen aunty kace ba umma ba ainasan bakayin karya

Kuyi hkr da wannan
💓💖💖💖ZAZZAFAN RABO💖💖💖

💫💫💫Aisha Umar Indabawa 💫💫💫

🌟🌟🌟marubuciyar littafin Meka Maidani 🌟🌟🌟

📱Typing 📱

🦚page 1️⃣3️⃣🦚

Kuyi hkr masuya kunsan typing dacin rai,sai kundinga hkr dani 🌹🌹🌹

****To yimaza kacinye mufita unguwa ,yace to yadingaci a tsanake harya gama ,daman anshiryashi yayi kyau sosai cikin wata lafiyayyar shadda tayi masa kyau kuwa sosai yawancin anfiyi masa kananun kaya ,to tunda yaron yanuna da kansa yanaso shikenan akeyi masa ,yace har sai yagaji dan kansa ,gidan wani abokinsa suka nufa da kansa yakejan motar ,babu yadda habu direba beyi dashi akan yakaishiba yace a a dagashi sai sultan zasutafi ,haka yahakura babu yadda ya iya da uban gidan nasa ,suna zuwa sukayi rashin sa,ar me gidan baya nan ,Abdul yayi kiransa a waya idan bakayi nisaba gani a kofar gidanka ,yace yanzon haka muna hanyar katsina ,dan ko matarsama begayamataba ,sbd batasan doguwar tafiya ,yace to shikenan Allah yakiyaye sai kundawo,Amman adinga gayawa iyali gaskiya sukasa dariya yakashe wayar ,suka fito daga gidan ,to sai ina kuma tunda wannan baya nan kai kuma yawo kakeso ,ko kuma mukoma gida yayi saurin girgixa kansa ,a a uncle kawai muje gidansu wannan aunty me kirki ai daman bakada watako daga ita sai dayar auntyn ko,yace baradai nakaika wajen aunty ,yajuwa kan motar suka nufi gidansu Islam danko jiya dasukayi waya da ita cewa yayi sai jibi zuwansa to Amman wannan zuwan Na sultan ne ,dame gadin gidan suka fara gaisawa har yana yimasa tunin kyautar da yace xaiyi masa ,shi tunda suka rabuma yamanta da wannan batun ,yace to kayi hkr zanbaka number dinta bafa wata me muhimmanci bace saika kirata kugaisa kagayama santa kakeyi ko tanaso ko bataso dole ayi ,shi kuma sai gdy yakeyi sai kace ance an bashi salwan gaba daya ,yakirata tafito dataga sultan tadagashi sama tana dariya ,tace tabdijan yau nayi babban kamu ,to ya gida Abdul yace lfy lau kinganmu da tsakar rana ko ,tace to meye tace to muje falo haka suka jera suna hira ,yace wlh wannan zuwan na sultan ne kinsan shine yadameni saina kawoshi wajenki wai kina da kirki ,tasake rikeshi ,tace ngd sultan toya karatu yayi dariya ,to ina fatan kanayi ,ya gyada mata kai ,sannan ya gaisheta ta amsa tana dariya.

Tajashi cikin gidanwajensu hjy ya gaishesu ,tashiga hada masu beta iri-iri ta cika musu kan table da kayan dadi kamar ansan da zuwansu ,suka dinga hira cikin nishadi ,yace waini Islam a wane babin kika ajiyeni ne tace kamar yaya ,to yanxo danayi miki mgnar fitowa sai kikawo wata mgnar ,kodai ba a sonane ni kadai nake haukana kodai nadaina whlar da kainane ,tace haba my love kasan banida kowa saikai kasan matsalar Abba ne ,dadan tanine da tuni anyi angama ,tokasan kudirinsa nasan mugama karatunmu ,kayi hkr kasan munkusa ,shida da yake nufin nubar zariya yamaidamu Cairo ,nice nace a a gara mugama anan ,yaja wata ajiyar zuciya metsayi ,to nahakura a gidane mommy tadamu danayi aure har tasa daddy yafara yimin fadan ko nayi ko kuma ya bani duk wadda yaga dama ,kinsan ni kadai suke ganin zankawo musu jika itadai tayi shiru ,tahadawa sultan kaya masu yawa ,dangin kayan zaki harda kudi ,Abdul yadire mata kudinta yace banda kudi yarona besan kudiba dan bana bashi kema kinsan tsarina tayi dariya nasani oga sukasa dariya ,tarakosu har bakin motarsu ,ananma aka tsaya wata hurar kamar baza a rabuba .
Chapter 12 · 0% Book details