← Book details Zaheedah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 19 OF 23

Sashe 19

Zaheedah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tace to yanzu me kk so kici, Heedah ta dan yatsine baki tace Mamy ni bana son komai.
Mamy tace ah ah tuna dai ance mutum bazai ci abinci ba.
Heedah tace to Mamy indomie n ki kawai nake so.
Mamy tace to bari inje in daura but dole ki nemo wani abunda kk so don indomie ba abincin da zaa taci bane dare da rana kinji ko? tace to Mamy.
Cikin fifteen minutes Mamy ta hada mata indomie guda hudu qanana ta soya mata kwai hudu shima sannan ta dafa wani kwan don taci wanda take so.

Bisa dining table Mamy ta jera mata abincin ga malt.

Adeel ne ya shigo Mamy tace yawwa je ka kira Heedah kace mata the food is ready.
Tare suka fito suka nufi dining din suka zauna Heedah ta jawo plate din indomie ta maida kwan gefe ta fara nadar indomie kamar ba gobe.
Shidai Adeel na gefe na kallon ikon Allah.
Sai da ta cinye indomie n kaf ko ni nayi mamakin Heedah da ta cinye indomie da wannan lafaffen cikin nata.
Malt din ma shanyewa tayi sai da ta nutsu sannan ta kalli Yah Adeel wanda ya qura mata ido yana kallo ko qyaftawa baya yi.
Yah lfy ta fada ajiyar zuciya ya sauke sannan yace babu komai baby girl.

Tashi ta yi tare da kamo hannunsa tace Yah muje ka rakani na gaishe da Goggo, yace ok let's go.

Har side din Goggo suna riqe da juna sai da zasu shigo sannan ta qwace kanta suka shiga da sallama.
Heedah ta gaishe da Goggo sannan suka cigaba da hira.

Nan Heedah ta yi sallan azahar shi kuma Adeel ya tafi masallaci.

Wuraren two sai ga Mamy ta shigo parlour n Goggo
Sai da suka gaisa tace ashe yarannan na wurin ku Goggo.
Tace ai ko dai suna nan tun dazu.
Mamy ta kalli Heedah tace me zaki ci ne, Heedah ta bata fuska tace Allah Mamy ni bana son komai fa.
Mamy tace ai fa sai kiyi amma baki isa ba sai kin fada abunda kk so don haka kiyi sauri ki fada mun.
Heedah ta dan yi shiru can tace yawwa uhmmnnn.
Mamy tace me ne ne tace uhmmm cabbage da quli!!!

Dukkansu dariya suka yi banda Heedah wadda ta turbune fuska kamar zatayi kuka.
Adeel hada su riqe ciki, sai da yabar dariyar sannan yace baby girl what's going on with you, you are craving something so repulsive and oh gosh!!! (mudai cabbage da quli yana mana dadi ba wani repulsive)

Mamy tace ke share shi kinji daughter Nah yanzu zan hada miki kinji.
Adeel ta kalla tace kai taso ka je ka sawo mana quli yace Mamy ina zan samo quli Goggo tace kaje gidan Hajiya Rabi me mai zaka samu.
Yace wannan qawar taki tace eh ita maza ka tafi sai ka siyo da yawa dan gaba.

Cikin 30 minutes Adeel ya dawo da gari yy zafi cike da quli

...................................

Written by the 💅🌟✨DIVAS🌟💅

Aysha,Nafeesah Mazoji &Amira Jibia.

(4 any comments or correction )👇
07032266308
[4/21, 9:18 PM] Aysha Mazoji: 💏💍ZAHEEDAH💏💍7⃣1⃣

Goggo tace ah wannan qulin kamar zamu ciyar da gari.
Yace ai Goggo gudun kada a nema kawai nace ta bani shi duka.

Mamy tana yanka cabbage tace bari nayi sauri na qarasa yankawa sai na daka qulin.
Mamy tace wai tsaya ma Heedah dafaffe kk so ko kuwa ba sai an dafa ba tace Mamy dafaffe nake so tace to bari nayi sauri.
Qulin Heedah ta diba tace bari na daka Mamy maza aje yanzu zan qarasa in daka.
Goggo tace ki qyale ta tayi daka mana Mamy tace to Goggo ba wata matsala kuwa.
Goggo tace ba wani matsala don kayi daka mu da har kayan nauyin da ake hana ku yan zamani dauka to mu dauka muke kuma lfy qlw zaki gammu yanzu ne da zamani ya zo.

Mamy tace to amma Heedah kiyi a hankali pls ki daka a hankali.
Adeel ya tashi yace muje na raka ki ma.

Nan kitchen din Goggo suka shiga Heedah ta dauko kujera biyu ta ba Adeel ita kuma ta zauna daya.
Ta fara daka Adeel yace wai naga su Mamy na ta habahaba dake, naga da kin ce abu har sauri ake a maki wai me ya sa.
Tabe baki tayi tace ni ma ban sani ba.
Yace to yaushe zamu koma gidan mu I'm too eager to ughhhh.
A shagwabe tace Yah stop it. We just spend one day without it fa.
Yace baby girl but kinsan fa wanda nake.
Tace Yah it's not even up-to one day.
Yace baby girl da gida muke kema kinsan da yanzu anyi fifth round ko?
Shiru ta masa ta ci gaba da dakan ta.
Bayanta ya koma ya fara shafata a hankali yana dan hura mata kunne.
A hankali wata kasala ta fara saukar ma Heedah cak ta tsaya da dakan da take don jin wani yanayi a jikinta.
Kanta ta daura bisa qirjinsa tare da lumshe ido.

Shi kuwa Adeel ya samu abunda yake so don haka ya fara saka hannunsa cikin rigarta......
Kamar daga sama suka ji muryar Mamy na wai ya naji shiru har yanzu.
Da sauri Adeel ya miqe yana sosa kai da gani bai da gaskiya, Allah ya sa bata gansu ba.

Heedah tace na gama Mamy dauko wani container tayi ta kwashe qulin.
Mamy ta daura tukunya tace ai steaming dinshi kawai zaayi.

Cikin 10minutes aka gama hada mata cabbage ya sha tomatoes, onion da cucumber. Abin gwanin ban shaawa.

Ai kuwa Heedah taci cabbage dinnan kamar ba gobe sai da taji cikinta yy dam har ba wuri.
Ita kanta Heedah tana mamakin cin da take Kwana biyu kamar bata qoshi.

xxxxxxxxxxxxxxxxxxxxxxxxxxxx

Sai ran Sunday da dare Mamy tace su koma gida tunda gobe aiki amma da sharadin komi Heedah ke so wanda bazata iya girkawa ba to a kira Mamy.

Haka suka koma gida suka ci gaba da soyewa.
Don kwana biyu Heedah wani qarfi take ji.
Ga kuma saurin fushi da take yi hakanan ko ita daya ce sai tayi ta fushi haka har Adeel ya gane da yaga tana kumbure2 zai ta lallabata har ta gaji ta sauko.
Wani lokacin kuwa sai dai ta sa masa kuka kuma komin lallashin da zaiyi bazata yi shiru ba har sai ta gaji tayi bacci don kanta kuma da ta tashi shikenan ta gama fushin sai kuma wani karon.

...................................

Written by the 💅🌟✨DIVAS🌟💅

Aysha,Nafeesah Mazoji &Amira Jibia.

(4 any comments or correction )👇
07032266308
[5/6, 7:36 PM] Aysha Mazoji: [4/24, 8:11 PM] Aysha Mazoji: 💏💍ZAHEEDAH💏💍7⃣2⃣

Haka suka ci gaba da rayuwa har tsawan wata biyu wata ranar kwata 2 Heedah bata girki wai bata son qamshin girkin sai dai su tafi gida su ci don yanzu ba abunda Heedah ke so irin cabbage da quli ko kuma zogale.

Heedah ta qara wani fresh tayi luwai2 da ita hips dinta sun qara expanding, bossom dinta kuwa wai abun baa cewa komi.

Zaune suke ya biye mata suna kallon cartoon, tana bisa cinyar sa daga ita sai crop top and faded jeans.
Shi kuma t shirt and shorts ne jikinsa.

Can ta dan dago tana kallon face dinsa, kallonta shima yy tare da kissing soft lips dinta yace baby girl wannan kallon fa tace haka nan nake kallonka.
Yace na miki kyau kenan daga Kai tayi.
Yace should we...... Oh definitely not now ta fada, I'm famished right now.
Yace what but you just ate.
Bata fuska tayi tace eh kuma wata yunwar nake ji yanzu.
Oh Allah ya fada yace wai baby girl me ke damun ki kwanannan ne.
Kamar jira take ya kai aya ta saka masa masa kuka mai sauti.

A hargitse yace baby girl me ya faru me na miki, cikin kuka tace ba kai bane kace na cika ci ba.
Yace baby girl ni Wlh ban ce haka ba amma sorry bazan qara ba kinji baby girl.
Bata bar kukan ba kuwa sai da tayi bacci.
A jikinsa tayi bacci don haka gyara mata kwanciyar sannan ya ci gaba da kallonta.

Kallonta yake yadda ta changa cikin two months tayi wani fresh tayi wasai da ita.
Ga wata yar qiba data qara bossom dinta ya ciko sosai.
Kuma cikinta shima ya ciko ya taso madadin da dayake a shafe a lafe.
Shi yasa kwanannan bai daga mata qafa Allah ya so shi bata hana sa kamar ma ta fi da juriyar lalurar sa.

Bayan sati biyu Yah Adeel ya tashi don ranar zaije wurin aiki, ya tashe da Heedah yace zai shirya zai je wurin aiki.
Cikin magagin bacci tace ya qyale ta ta qara baccin five minutes.
Yasan rigimarta kuma dama da asuba sai da yy aiki kawai sai ya qyale ta don ta samu hutu.

Kitchen ya nufa don ya sama ma kansa breakfast.
Heedah ce ke bude idonta a hankali don yanzu baccin ya fita daga idonta.
A hankali ta yaye blanket din dake jikinta ta zura qafafun ta qasa don tana son ta shiga bathroom kafin ta je ta taimaka ma Yah Adeel ta masa breakfast.
Rigarta taga ta taso, ta shafa wani abu taji mai dan tauri, da sauri ta bude rigarta dan ganin menene.

Wani razanannen ihu ta saka sanadiyar abunda ta gani ..........................................

Written by the 💅🌟✨DIVAS🌟💅

Aysha,Nafeesah Mazoji &Amira Jibia.

(4 any comments or correction )👇
07032266308
[4/24, 11:59 PM] Aysha Mazoji: 💏💍ZAHEEDAH💏💍7⃣3⃣

Adeel na kitchen yaji Heedah ta saki wani wawan ihu.
Da gudu Adeel ya nufi dakin don yasan wannan ihun bana lafiya bane.
Chapter 19 · 0% Book details