← Book details Zaheedah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 11 OF 23

Sashe 11

Zaheedah Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Wani irin shu'umin murmushi ya sakar mata tare da daga mata gira hey baby girl abunda ya fada kenan kafin ya maida kansa ga aikin da yake.
Da sauri ta kama kansa ta dago shi Don Allah Yah in kana ma darjan iyayenka ka bari wlh bana so.
Kallonta yy yace ni kuma a matsayina na mijin ki ina so.
Tuni hawaye suka wanke mata fuska yanzu Yah Don Allah fa nace Kai ya kada yace naji da Allah ni ba abunda zan miki for now amma zan ci gaba da abunda nake yanzu.dadai taji yace ba abunda zai mata sai tace Yah Dan Allah abunda Kk yi ya dace kenan Goggo na parlour kazo kana min wannan abun in ta tashi fa yace ko ta tashi nasa key ma qofar tace to wai kai baka jin Kunya yace wane Kunya kuma nida matana.
Zata qara manana yace look I'm busy right now I'm going to meet my twins so let's postpone the talking after I give them what they need (🙈🙉).
Idonta ta rufe don wata irin kunya da ta ji oh yanzu Yah baida Kunya.

Lamo tayi tana jin duk abunda yake mata ita yau taga ta kanta.
Tun tana jira ya gama har ta gaji ta fara gyangyadi dadai taji abun ba mai qarewa bane bata masan sanda tayi bacci ta qyale shi yana ta faman jagwala ta.

Shi kuwa sai da ya raba dare yana abu daya sannan ya tashi yy wanka ya dauro alwala yy sallar dare tare da roqon Allah ya basu zaman Lfy da zuriya dayyiba.

Sai wurin ukun dare sannan ya kwanta tare da jawo Heedah jikinsa yy musu addua haba sai bacci.

Da asuba koda ya tashi ya tada Heedah tayi sallah kk ta saka masa yace to sarkin Kk me kuma ya faru.
Tace yanzu Yah nan ka kwana in wani Ya ganka fa yace ai bama wanda zai ganni share hawayenki kibar Kk kinji baby girl.

Koda ya fita Goggo sai da ta tsorata tace kai kuma fa daga ina.
Cikin inda 2 yace nazo na tada Heedah ne tayi sallah tace yaushe ka wuce to yace da Kk shiga ban dakin parlour na shigo tace to yy kyau ka tafi masallaci kada ka rasa jam'i to.
Ya wuce sum 2 ita dai Goggo ta gane anan ya kwana don tashinta kenan ya fito amma hada cewa da ta shiga ban daki yazo.
Ai kuwa zata ma mamansu magana kawai a bashi matarsa su tafi gidansu. Can su qarata. Wannan rashin Kunya har ina ya tsallake ta ya wuce wurin matar sa kai yaran zamani Allah ya kyauta musu.

Bedroom din ta tashi ta shiga taga Heedah ta idar da sallah.
Tace Goggo ina kwana tace da ban kwana ba kin ganni yanzu ke Zaheedah shine dan tsabar rashin Kunya irin taku ta ya'yan zamani shine kk kira Adeelu ya kwana nan haba nidai nayi mamakin da kk zo nan zaki kwana a rashin kunya kuke son yi.

Heedah kuwa sai hawaye take tace wlh Goggo bani na kira sa ba wlh shi yasa na gudo daga side din su Mamy dan kar yazo kuma ni lokacin da yazo ma nayi bacci wlh.
Goggo tace ai na zata ke kk kira sa.
Tace wlh Goggo ba ruwana kuma ni ban ma san nan ya kwana ba Allah ko. ...................................

Written by the 💅🌟✨DIVAS🌟💅

Aysha,Nafeesah Mazoji &Amira Jibia.

(4 any comments or correction )👇
07032266308
[3/21, 7:50 AM] Aysha Mazoji: 💏💍ZAHEEDAH💏💍4⃣8⃣

Sai wurin goma Mamy ta zo gaishe da Goggo sai da suka gaisa sannan Goggo tace yawwa dama inaso in miki manana don Allah a tarkata yaran nan su tafi gidansu, Mamy tace Goggo wani abu ya faru ne? Tace ba abunda ya faru kawai dai naga haka shi yafi daidai.
Yaronnan ai yy haquri da yawa don haka ki gaya wa babansu a maida su gidansu.

Mamy tace to in Alla ya yarda yanzu zan gaya mishi.
Tace yawwa don dazu na shafaa da yazo gaishe ni na fada masa.
Mamy tace to zan gaya masa Yanzu inshaa Allah.

Ai kuwa Mamy na shiga gida ta gaya ma Daddy saqon Goggo yace dama ni ina da niyar tarkatasu su tafi gidansu yau dinnan inshaa Allah.
Zuwa bayan isha'i sai ku rakata gidan ta kowa ya huta.
Kin san dannan naki baya da kunya tace danka dai yace tun fa da asuba na gansa ya fito daga side din Goggo da na tambayesa me yaje yi sai cemin yy wai zuwa yy tashin Heedah tayi sallah jifa.
Mamy tace dan yanzu kenan Allah dai ya qara shirya mana su ameen.

Yinin ranar kayan mata Mamy ta yini bata tana sha.
Sai bayan isha 'I su duka gidan har da Daddy aka tafi rakasu sabon gidan su mai matuqar kyawu. Mota biyu sukayi.

Nasiha suka yi musu sosai mai shiga jiki daga bisani suka tashi suna sa masu albarka.
Heedah kuwa sai kk take yi ji take kamar wannan ce ranar da aka fara kaita gidan Yah Adeel dan dai wannan karon akwai bambanci sosai. Wannan karon a matsayin yana sonta aka kayo ta madadin wancan karon da ya tsane ta.

Bayan sun tafi tashi ta yi tace Yah ina dakina yake yace duk inda kk shiga dakin ki ne. Kallonsa take tana tuna wancan karon da ya koro ta daga bedroom wai nasa ne.
Jin an hura mata iska a ido yasa tayi firgigit ta dawo daga duniyar tunanin da ta tafi.
Yace kallon fa ko na miki kyau ne.
Murmushi tayi tare da sadda kanta qasa.
Tace Yah zanje nayi wanka yace OK nima bari naje nayi nawa.
Sai da ta gama wanka sannan ta shirya cikin kayan baccinta masu kyau sosai sannan ta saka ma dakin ta key tayi kwanciyar ta saboda taga taketaken Yah Adeel.

Shi kuwa yana gama wanka bathrobe kawai yasa ya nufi dakinta.
Qofan yaji a rufe da key. Yadan yi murmushi yace baby girl bashi kk dauka ne.
Ita kuwa Heedah har ta fara bacci sama2 ta tuna ko baici abinci ba da sauri ta sakko daga bisa bed din ta dauko hijab dinta ta saka ta fita zuwa parlour.
Zaune yake yana kallon aljazeera dago kai yy ya sakar mata wani qayataccen murmushi yace baby girl dama bakiyi bacci ba tace na fara dai. Yace to ya akayi ne ko you just want to be with me ya fada tare da yin wani crook smile.

Bubbuga qafanta ta Fara alamun shagwaba nidai Yah ka bari. Cikin ransa yace Yah ilahi dama Heedah ta iya shagwaba haka.
Kasa haqura yy sai da ya jawo ta zuwa jikin sa.
Zata miqe daga jikinsa ya qara qanqameta tace Yah Adeel wani abu zan sama maka kaci bana so ka kwana da yunwa.

Iyyeh yace ashe dai ana so na tunda baa so na kwana da yunwa.
Rufe idonta tayi tana qoqarin tashi.
Yace barshi Heedah bana so kibar jikina a qoshe nake.
To Yah ka sake ni na tafi na kwanta bacci nake ji, yace to baby girl nima baccin nake ji zo muje mu kwanta a dakina.
Tace Yah ni fa wlh kunyar ka nake ji Don Allah kabar ni na kwanta daki na.
Haba baby girl ke fa kinsan hukuncin matarda ta guji mijinta kuma ma bakya jin tsoro wani abu ya kama ki ke kadai a dakin ..........................................

Kuyi hqr pls kwana biyu bana jin dd ne.
I'm so so grateful for all who called and text me to hear how I was doing. I love you all 😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘

Written by the 💅🌟✨DIVAS🌟💅

Aysha,Nafeesah Mazoji &Amira Jibia.

(4 any comments or correction )👇
07032266308
[4/6, 8:39 PM] Aysha Mazoji: [3/22, 2:36 PM] Aysha Mazoji: 💏💍ZAHEEDAH💏💍4⃣9⃣
Chapter 11 · 0% Book details