← Book details Yarima Abdulmaleek Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 6 OF 20

Sashe 6

Yarima Abdulmaleek Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Gari na wayewa yace ta shirya zasu wani guri saida ta gama komai ta fito ta sameshi a mota mintina kalilan suka iso inda zasu cikin mamaki Zainab ke kallon masarautar a ranta tace kodai dan sarki ne, to amma me zasuyi anan? ganin ya wuce ta yasa tabi bayansa tana kalle kalle kamar 'beran kauye yaje birni bai zame ko'ina ba sai asalin babban palon mai martaba kuma yau gabadaya ahlin suna can bai tsaya ko'ina ba sai gaban mai martaba ya durkusa ya kwashi gaisuwa cikin mmk mai martaba yake kallon Zainab yace "Muhammad daga ina ka samo wannan"? Cikin ladabi ya fara fada musu komai har kuwa zaman datai a gidansa shiru palon ya dauka kowa na kallon Zainab cikin tausayawa banda Yaha da haka kawai taji tsanarta lokaci guda ta diram mata arai.

Mai martaba ne ya kalli Zainab yana cewa "ke yarinya daga ina kika fito? mene gaskiyar labarinki,? kada kiyi mana karya ke 'yar waye? Zainab da kanta ke sunkuye tun dazu muryata na rawa ta fara basu labari kowa ji yake tsumin jikinsa na tashi dajin labarin yayin da ita kuma take kukan tuna mahifanta.

Lallai kam taga rayuwa ace bakasan dangin ka ba ko daya wanne irin hali zaka shiga.

Mai martaba daya gama tunani yace "to yanzu mene shawararku akan wannan al'amarin domin abune mai girma"? Abban Mahmud ne yace ai inaga ba abinda zamuyi daya wuce mu rike ta anan tamkar 'yar da muka haifa idan shawara ta tayi, "amma ranka ya dade me kace"? Mai martaba yace "haka shine dai dai Ibrahim nima abinda nake tunani kenan idan ma mun barta ta tafi babu inda zataje, to amma a cikin ku waye zai riketa kai ko Yusuf "? Abba yace "a'a nizan riketa sai ta zauna a gurin Yahanasu duk abinda take so zata samu".

Gyara zama Yaha tai tana cewa "gaskiya nidai bazan riketa ba tunda Hajara ta kusa zuwa taya zan rikesu har su biyu kawai bansan yarinya ba daga ta fada muku karyarta ko da sharri tazo wa yasani sai a nemi a likamin ita ni dai bazanyi rikon wannan tsintacciyar magen ba"tana fadin haka ta mike ta fice a palon.

Da mmk mai martaba yace "Ibrahim dama matarka bata da kirki a gabana take iya fadar bakaken mgn haka"? Cikin ladabi Abba yace "ayi hakuri ranka ya dade amin afuwa"dadyn Yarima mai martaba ya kalla yace "Yusuf kai na baka ita daga yau kaine mahaifinta duk wani nauyin ta akanka yake"cikin girmamawa yace "to ranka ya dade godiya nake "kallon mama yai yana mata alama dan murmushi tai tana jinjina kai kafin ta mike tana cewa "yata tashi muje"mikewa Zainab tai tana goge hawayen maganar da Yaha ta fada akanta suka fita Yarima ma sallama ya musu yana fita domin shi kasar ma zai bari.

Mama na rike da hannunta har part dinta ta rakata wani bangare daban tace ta zauna tana zuwa ba'a jima ba ta dawo tare wata budurwa zamatai tana kallon Zainab tace "ranki ya dade dama Yarima Abdul-malik nada kanwa wallahi suna kama"? Murmushi mama lokacin zata fita tace "kedai yi mata lalle kawai ina dawowa yanzu"lalle ta fara zana mata mai kyau saida aka gama sannan aka fara yimata kitso tab masha Allah sai wanda ya ganta bayan angama komai tai wanka mama ta kawo mata kaya tasa ta fita palo.

Dagowa mama tai tana murmushi tace "dota zo ki zauna ga abinci nan zama Zainab tai tana sunkuyar da kanta tace "nagode mama Allah ya saka da alkairi" har lokacin murmushi mama keyi Yarima ya shigo cikin shirinsa alamar lokacin tafiyarsa yayi mikewa mama tai tana riko hannunsa tace baby harka shirya,? yaushe kuma zaka dawo"? Zama yai yana lankwasar da kai yace "bazan wuce wata biyu ba kawai"zaro ido mama tai "baby wai watan nan jinta kake kamar sati naga alama dadi kake ji idan ka tafi ka barni amma yanzu tunda muna da wata babyn shikenan kaje kai shekara ma"cikin shagwaba yace "haba mama kar muyi haka dake am first and last"cikin zolaya mama tace "tab waya fada ma"? Gara ka sake shiri dan kaidin yanzu babban yayane"yunkurawa yai zai tashi ta rike shi tana dariya tace "baby tsaya kaci abinci" dan bata fuska yai ganin ta dauko cikin lallami tace "ci ko spoon biyar ne sai ka tafi kaji babyna" tana fada masa magana mai dadi ta samu yaci abinci kafin ya tafi Zainab kan dataga irin lallabashin da mama keyi kamar yariri yasa ta zaro ido aranta tace "tabdijan shagwababbe".

Sati uku da tafiyar Yarima Hajara ta zo murna gurin Yaha kamar ta maida ita ciki duk abinda tace yanzu za'ai mata shi.

Abinda aka samai rana me karewa ne yau gida kacame yake da murna yarima zai dawo dan Hajara ma gabadaya ta kasa nutsuwa sai kaiwa da komowa take abinci kala Kala tasa aka mata na saukarsa a palon Yaha ta ajiye tana cewa bari taje tai wanka Yaha batai mata magana ba domin abinda ke damunta daban Abba da Dady sun tafi masarautar Bauchi mai martaba ya aikesu kawai ji take hankalinta bai kwanta da hakan ba da tafiyar da sukai.

Da yamma Yarima iso gida murna abin ba mgn kamar yadda aka saba tararsa koda yaushe yauma haka saida ya gaisa da mai martaba sannan ya shiga part dinsa don hutawa yana palo Hajara ta shigo da wadanda suke dauke da abincin suna ajiyewa sukai waje sai daya gama daura agogon hannunshi ya nufi hanyar fita shan gabansa tai tace "haba Abdul-malik mene haka"? Da mamaki yake kallon ta ita kuma wannan lfy uban me tazoyi nan cikin danjin haushi yace "ban guri idan kika kara shigowa part din nan saikin gane kurenki"cikin nuna isa Hajara tace "malam bafa zaiyuwu ka wulakanta niba dan kawai ina sonka bashi yake nufin kana da ikon da zakai min kowanne cin fuska ba"kallon ta yake cike da tsana danshi wannan me kama da tabaryar ba abinda zaiyi da ita zagaye mata yai zai fice ta jawo hannunsa tana cewa "wallahi fa baka isa ka fita a palon nan ba sai ka saurare ni ko anfada maka nidin sa'ar____bata karasa ba tai shiru jin wani lafiyayyen mari ya sauka a kumatunta ba arziki ta sake shi ko karasa kallonta baiyi ba ya fice yana jan tsuka kuka Hajara ta fice dashi tana komawa guri Yaha harda birgima a kasa wai marinta yai hankali tashe Yaha tace "ya mareki"? Amma wannan yaro anyi mara tarbiyya kinga daina kukan aure ke dashi kamar an daura ne"share hawaye tai "wallahi umma ko baya sona dole ya aureni "Yaha tace af kwantar da hankalinki nace miki nasan abinda zanyi.

Part din mama ya nufa dai dai zai shiga yaji Zainab na waya dan dakatawa yai jin tace "ina jinka nufin ka wai kazo gidanmu, tab a'a gaskiya zan dai fada maka amma ba yanzu ba saina tambayi mamana da dadyna
idan sun amince zan sanar dakai sai kaz______jitai an zare wayar afirgice ta dago ganin wanda batai zato ba yasata rudewa ga wani abu da take hangowa cikin idanunsa da batasan me zata kira shi ba tsawa ya daka mata cewa da ubanwa take mgn shiru tai mama dake bedroom batasan meyake faruwa ba jin karar Zainab yasa ta fito da gudu da mmk take kallon Zainab datai kneel down a gaban Yarima tana kuka shi kuma yana tsaye ya zuba mata ido karasowa mama tai tana daga zainab din cikin mamaki tace "baby lafiya? meya faru? Idansa nakan Zainab din yace "yaushe wannan yarinyar ta fara hira da samari cikin wayarki a ina ta sansu?"? Da sabon mmk mama tace "Zainab din"? Bai sake magana ba ya juya ya fita a part lallashinta mama tai sannan ta kama hannunta suka shiga ciki.

Washe gari suna zaune ana firar yaushe gamo su Abba sun dawo mai martaba ya kalli Yarima yana cewa "Muhammad ya kamata ace yanzun kayi aure kana da iyali kaima ko ba haka ba, kaga aure shine darajar kowanne mutum ya kamata kayi"sunkuyar dakai Yarima yai baiyi mgn ba alamar bai shirya ba mmk ne ya kama mai martaba amma sai yace "to shikenan Muhammad tashi kaje"mikewa yai yana fita Yaha tai gyaran murya tace "ranka ya dade ai wannan mai sauki ne Hajara ta dade tana sonshi saboda shi ta dawo nan da zama ta jona karatunta ta dade tana cemin na fada nace mata a'a".

Shiru palon ya dauka zuwa can mai martaba yace "kai Yusuf ya kake gani domin danka ne kaine mahaifinsa"? Cikin ladabi dady yace "a'a duk hukuncin dakayanke dai dai ne kai da kaya ai duk mallakar wuya ne"zuciyar mama tafasa take tun lokacin da Yaha ta fara mgn tasan akwai wani abu data kulla a cikin wannan abin Abba kam cewa yai "a'a a bari tukuna aji ta bakinsa idan ya amince shikenan "karaf Yaha tace "to shiyai kansa duk umarnin da aka bashi dole zaibi"mama so take tayi magana ta kasa mai martaba yace "shikenan zamuje medigurin in sha Allahu" Abba kan bai amince ba ya kuma cewa "gaskiya ya kamata a fara tambayar_____ tarar numfashinsa Yaha tai "ya kake jada maganar mai martaba ai ya gama yanke hukunci" tana fadin haka ta tashi ta fice a palon tana shiga part dinta ta sheke da dariya tana cewa "lokacin ki ya fara Yaha wallahi Abdul-malik sai na mayar dakai gawa.

Mama na shiga palon ta taga Yarima a zaune alamar yayi nisa cikin tunani dafa shi tai ya dago ganin mama ce yashi rungumeta jin zuciyarsa kamar zata fito waje cikin kwantar masa da hankali mama tace "baby kayi hakuri in Allah ya yarda abu mara kyau bazai taba samun ka ba kaga yanzu fitowa ta daga palon Mai martaba yace zasuje maidiguri a nema maka auren Hajara ni kuma wallahi harga Allah yarinyar nan batai min ba ko kadan".
Chapter 6 · 0% Book details