Sashe 2
Yarima Abdulmaleek Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani gida ta bud'a ta shiga, amma iya yanayin sa zai nuna maka cewa gidan hayane, da wata tsohuwa suka hadu zata fita a gidan cikn tausayawa ta kalleta tana cewa "sannu kinji zainab, ki 'kara hakuri komai mai wucewa ne, ki daina sa tunani a ranki in Allah ya yarda wata rana zakiga ribar hakurin ki." Murmushin karfin hali zainab tai tana daga mata kai tace "ngd da kulawarki inna, sai kin dawo Allah ya tsare amin" inna tace tana ficewa. Ita kuma ta shiga gidan, bangare biyu na inna da nasu.
Da sallama ta shiga tanai wa matar dake zaune a gaban kuloli sannu da gida, ko cira kai batai ba balle ta sa ran zata bata amsa. Wuce wa tai ta shiga d'akin ta tana tunanin yaushe ne zata samu canjin rayuwa? rashin iyaye baiyi ba, gashi batasan kowa nata ba, balle ta koma wurin su. Mahaifanta sun rasu bata san danginta ba, sai hjy bilki kishiyar maman ta, wannan wacce irin rayuwa ce ta tsinci kanta a ciki? goge hawayen fuskar ta tai jin bilki na kwalla mata kira, cikin sauri ta fito tana cewa "gani umma".
Tsaki taja "wato zainab wuyanki ya fara 'kwari ko? sbd ke tinkiya ce kullum sai nayi da baki na akan fita da abinci shago saboda kin gado bakin halin uwarki, to wallahi wuya zaki sha a gurina" kuka zainab keyi dan idan akwai abin data tsana a duniya shine ka zagar mata mahaifa.
Bilki tace "inye hamshakiya danna zaki uwarki kike kuka? to ko tana raye zan zageta balle tana bayan kasa, ke dalla tashi ki fitamin da kayan sana'a ta, dan wallahi kikamin kwashe duka zaki mi'kewa tai ta f
ara diban kulolin tana fita dasu, tana shago taga Tanimu ya sauke hindu a mota dan girgiza kai tai cikin takaici, sai bayan la'asar ta koma cikin gida duk da abincin ya kare tun wuri, zaman ta a wajen yafi mata alkairi. Bata kud'in tai dai-dai Hindu ta shiga da bakar leda a hannunta, ta mi'kawa Bilki tana cewa "wanka zanyi in anjima Tanimu zai zo" kallon Zainab tai "ke jeki d'ebo mata ruwa za tai ba'ko, ba irin ki bace mai bakin jini, kuma ki dawo ki dafa mata wannan kazar"
'Kala zainab bata ce ba, ta d'au bokiti tana fita a gidan, bayan ta d'ebo tana shigo wa gidan a zaure suka hadu da Bashir, yana ganin ta cikin murna yace "masoyiya ta dama ke nazo nema, ya gida?" kallon sa tai, cikin takaici taja tsuka, zata wuce ya jawo hijab d'inta. bokitn ya fad'o ya fashe
WASH ALLAH GASKIYA KUNA KOKARI 😥
[11/25, 5:27 PM] Yusrah Musa Abubakar: 👑YARIMA ABDUL-MALIK 👑
💫 *ANNURI WRITER'S ASSOCIATION* 💫
By
YUSRAHMS ABUBAKAR
#YMA
Dedicated to Maman khaleel
Safiyya Aliyu
Ina matukar godiya da nuna kaunarki a gareni MY FEEDOH may Allah bless you and your household wannan page din naki ke daya har zuwa page 20 mallakar kine.
*If you go to the river dont swim 🏊 it can carry you away 🏃.
Page 2
Da gudu Bilki ta fito ganin abinda daya faru yasa tace kan ubancan amma Zainab anyi muguwar yarinya sbd bakin hali saida kika karasa min bokiti to wallahi baki isa ba saikin biyani mayya kawai mitsiyaciya ta karasa maganar tana janta ciki hakuri Zainab ke bata amma wani irin gigitaccen Mari ta sauke mata saida ta durkusa har kasa bisa kafafunta saboda azaba wanda hakan yai daidai da shigowar Inna da sauri ta karaso tana dago Zainab din dake kuka fuskarta tayi ja wani irin kallo taima Bilki mai nuna cewa wata rana zaki nadama tace amma wallah Bilki baki da da'a sau nawa zan fada miki ki daina dora hannunki akan yarinyar nan rashin iyaye fa ba hauka bane kinsan irin bala'in da kike kwasarma kanki kinsan hukuncin mai zaluntar maraya me yasa baki da tunani ko kadan ina tsorace miki ranar da zaki kuka da idanunki Zainab ba yarinyar da za'a wulakanta bace duk abinda ya sameki ki kuka da kanki na fada miki.
Kallon sama da kasa Bilki ke mata tunda ta fara magana sannan tace ahayye nanaye kaji mace da kwarton munafirci meye ruwanki a ciki amma ba laifinki bane da alama yunwa kike ji ga dusa can idan kin gama ci kije ki sha ruwa munafikar tsohuwa kawai tana kaiwa nan ta wuce ta koma ciki.
Da kallon suka bita inda sabo kuma Inna ta saba da wulakancin Bilki ba tun yauba hannun Zainab ta rike tace muje dakina Zainaba ki huta kinji ki ta hakuri komai mai wucewa ne Allah ya jikan Umar da Khadija ameen Zainab ta furta cikin damuwa amma ko babu komai tana samun sauki idan Inna ta wuni a gida.
Yau Yarima ke shirin zuwa kano gurin kakarsa zaune suke a palor mama ta kalleshi tace gaskiya babyna kana da kyau kamar balarabe "harka shirya kenan"? Da kai ya bata amsa taci gaba da cewa Allah ya kare min kai baby inaji a jikina kamar zuwanka gurin ammi alkairi ne tamkar zaka hadu da wani abu dazai saka farin ciki kuma ya zamo maka garkuwa a rayuwarka.
Ido ya zuba mata bayan ya gama jin jawabinta yai murmushi har dimple dinsa na lotsawa amma baiyi magana ba mikewa mama
tai tana kire hannunsa suka fita har mota tai masa rakiya kafin ta koma.
Lokacin daya dayai perking da mota a harabar gidan da mamaki Mustapha dake tsaye kafar shiga palor yake kallon motar da tunanin waye a ciki bai kare mamaki ba Yarima ya fito yana gyara agogon hannunshi domin shi kadai ya bata shi mutum ne wanda baya bukatar takurar wasu fadawa ko bayi duk inda zaije shi kadai yake zuwa ko driver baya bukata.
Dagowa yai sukai ido biyu da Mustapha wani ihu yai yana rungumeshi cikin nuna tsantsar murna yace abokina kaine dama zan ganka kwana kusa gaskiya nayi kewarka yaushe raban da mu hadu kusan shekara biyu fa murmushi Yarima yai yana kallon shi yace sorry ba gani yau nazo muje ciki na gaji inason na huta shiga sukai wata farar mace ta dago tana kallonsu tace dama saida tunani na ya bani tunda naji Mustapha na ihu yana cewa abokina nace nasan kaine ba wanda zaizo yayi wannan haukan sai kai ta karasa maganar da murmushi.
Rungumeta Yarima yai a rayuwarsa yana matukar son ammi Mustapha ne ya fara dariya yana cewa wato Abdul-malik har yanzu baka janye wannan dabi'ar taka ba yanzu runguma ce gaisuwa dagowa yarima yai yana kallon ammi alamar ta tanka Musty yace malam bafa zakazo ka sanya tsohuwata magana ba ka baro taka acan tana hutawa zaka wani takura min tawa harararsa Yarima yai kafin ya mike yana cewa muje na gaji inason na huta bani da lokacin ka wucewa sukai yana cewa ammi bari ya dan huta.
Zainab ce zaune a tsakar gida tana hada kunun aya Bilki ta fito a daki tana cewa Zainab me kikeyi anan? dagowa ta tana kallonta tace kunun aya nake hadawa
[11/25, 5:27 PM] Yusrah Musa Abubakar: Innalillahi dan Allah amin afuwa ban gama typing ba nayi sanding.
*👑Yarima Abdul-malik 👑*
#Yusrah m Abubakar
[email protected]
*💫ANNURI WRITES ASSOCIATION💫*
*Page 3
Tana kallota tace "kunun aya nake hadawa".
Kudi ta mika mata jeki sayo min kayan miya bari na rika dura miki to Zainab tace tana amsar kudin tasa hijab ta fita a gidan Aliya ce ta shigo tana cewa, a'a Bilki harda kunun aya kika koma yine? Um lallai liyafa taci gaba ta karasa maganar tana zama a kujerar da Zainab ta tashi sai a sannan Bilki tai magana "a'a ba nawa bane na Zainab ne makaranta zata tafi dashi jin haka yasa Aliya tabe baki tace wallahi shiyasa duk yarinyar nan tabi ta rainaki ashe guri ta samu kina mata bauta Bilki zatai mgn Zainab ta dawo dan haka tai shiru aje kayan miyan tai tana dauka jakanta ta fita a gidan haduwa sukai da hindu a karshen layin anguwar suna tsaye da wani bata ko kalli gurinsu ba ta tsaida napep ta shiga.
A shirye suka fito shida Musty zai rakashi makaranta dan lecturer ne ammi ce ta kalli Yarima cikin wasa tace me soja zaije yi makaranta karfa ka firgita dalibai dan murmushi yai yana kallonta yace, dama ana gane soja ne ko baisa kaya ba? Dariya Musty yai ana ganewa mana musamman rashin fara'arka.
Mikewa yai yace to naji muje tunda ban sako dakai ba fita sukai suna shiga mota basu zame ko'ina ba sai makaranta babu yadda Musty baiyi ba akan ya karasa office dinsa amma yaki yace ya barshi anan idan yana bukata zai biyoshi hade rai Musty yai zaiyi magana Yarima yace masa "sorry"cikin haushi yace a'a uban sorry dan iska kawai wucesa yai shi kuma ya tsaya jikin motar yana waya da mama kamar saida akazo saitin kunnensa aka kwalla kiran Zainab wallahi ki tsaya kibani abuna idan na kama ki zaki sani haka kawai xuciyarsa ta tunzura shi ya kalli inda ake maganar idonsa ne ya sauka akan Zainab dake tsaye tana dariya rike da fefa a hannunta tana kalla alamar karantawa take wani irin kallo ya bita dashi cikin mamakin da baisan yayi hakan ba.
Karasowa waccen din tayi zata kama ta sukayi wani lungu da gudu dan dafe kirjinshi yai tare da runtse ido Musty ne ya dafa shi bai dago ba cikin mamaki yace abokina yadai meke faruwa? Shiru yarima yai ba tare daya bashi amsa ba saima shiga mota dayai abin ne ya daurewa Musty kai dan haka shima shiga yai daidai zaiyiwa motar key ya kuma cewa Abdul-malik wai dan Allah meke damunka naga gabadaya ka canja ba haka muka taho ba kodai kayi gamo ne? Wata uwar harara Yarima ya sakar masa batare da yace kala ba rabuwa dashi Musty yai dan ba amsa zai samu ba.
Koda suka koma gida ma kasa samun nutsuwa yai daya rufe ido ita yake gani lokacin da take dariya gabadaya ko abinci bai samu yaci ba har dare.
Da sallama ta shiga tanai wa matar dake zaune a gaban kuloli sannu da gida, ko cira kai batai ba balle ta sa ran zata bata amsa. Wuce wa tai ta shiga d'akin ta tana tunanin yaushe ne zata samu canjin rayuwa? rashin iyaye baiyi ba, gashi batasan kowa nata ba, balle ta koma wurin su. Mahaifanta sun rasu bata san danginta ba, sai hjy bilki kishiyar maman ta, wannan wacce irin rayuwa ce ta tsinci kanta a ciki? goge hawayen fuskar ta tai jin bilki na kwalla mata kira, cikin sauri ta fito tana cewa "gani umma".
Tsaki taja "wato zainab wuyanki ya fara 'kwari ko? sbd ke tinkiya ce kullum sai nayi da baki na akan fita da abinci shago saboda kin gado bakin halin uwarki, to wallahi wuya zaki sha a gurina" kuka zainab keyi dan idan akwai abin data tsana a duniya shine ka zagar mata mahaifa.
Bilki tace "inye hamshakiya danna zaki uwarki kike kuka? to ko tana raye zan zageta balle tana bayan kasa, ke dalla tashi ki fitamin da kayan sana'a ta, dan wallahi kikamin kwashe duka zaki mi'kewa tai ta f
ara diban kulolin tana fita dasu, tana shago taga Tanimu ya sauke hindu a mota dan girgiza kai tai cikin takaici, sai bayan la'asar ta koma cikin gida duk da abincin ya kare tun wuri, zaman ta a wajen yafi mata alkairi. Bata kud'in tai dai-dai Hindu ta shiga da bakar leda a hannunta, ta mi'kawa Bilki tana cewa "wanka zanyi in anjima Tanimu zai zo" kallon Zainab tai "ke jeki d'ebo mata ruwa za tai ba'ko, ba irin ki bace mai bakin jini, kuma ki dawo ki dafa mata wannan kazar"
'Kala zainab bata ce ba, ta d'au bokiti tana fita a gidan, bayan ta d'ebo tana shigo wa gidan a zaure suka hadu da Bashir, yana ganin ta cikin murna yace "masoyiya ta dama ke nazo nema, ya gida?" kallon sa tai, cikin takaici taja tsuka, zata wuce ya jawo hijab d'inta. bokitn ya fad'o ya fashe
WASH ALLAH GASKIYA KUNA KOKARI 😥
[11/25, 5:27 PM] Yusrah Musa Abubakar: 👑YARIMA ABDUL-MALIK 👑
💫 *ANNURI WRITER'S ASSOCIATION* 💫
By
YUSRAHMS ABUBAKAR
#YMA
Dedicated to Maman khaleel
Safiyya Aliyu
Ina matukar godiya da nuna kaunarki a gareni MY FEEDOH may Allah bless you and your household wannan page din naki ke daya har zuwa page 20 mallakar kine.
*If you go to the river dont swim 🏊 it can carry you away 🏃.
Page 2
Da gudu Bilki ta fito ganin abinda daya faru yasa tace kan ubancan amma Zainab anyi muguwar yarinya sbd bakin hali saida kika karasa min bokiti to wallahi baki isa ba saikin biyani mayya kawai mitsiyaciya ta karasa maganar tana janta ciki hakuri Zainab ke bata amma wani irin gigitaccen Mari ta sauke mata saida ta durkusa har kasa bisa kafafunta saboda azaba wanda hakan yai daidai da shigowar Inna da sauri ta karaso tana dago Zainab din dake kuka fuskarta tayi ja wani irin kallo taima Bilki mai nuna cewa wata rana zaki nadama tace amma wallah Bilki baki da da'a sau nawa zan fada miki ki daina dora hannunki akan yarinyar nan rashin iyaye fa ba hauka bane kinsan irin bala'in da kike kwasarma kanki kinsan hukuncin mai zaluntar maraya me yasa baki da tunani ko kadan ina tsorace miki ranar da zaki kuka da idanunki Zainab ba yarinyar da za'a wulakanta bace duk abinda ya sameki ki kuka da kanki na fada miki.
Kallon sama da kasa Bilki ke mata tunda ta fara magana sannan tace ahayye nanaye kaji mace da kwarton munafirci meye ruwanki a ciki amma ba laifinki bane da alama yunwa kike ji ga dusa can idan kin gama ci kije ki sha ruwa munafikar tsohuwa kawai tana kaiwa nan ta wuce ta koma ciki.
Da kallon suka bita inda sabo kuma Inna ta saba da wulakancin Bilki ba tun yauba hannun Zainab ta rike tace muje dakina Zainaba ki huta kinji ki ta hakuri komai mai wucewa ne Allah ya jikan Umar da Khadija ameen Zainab ta furta cikin damuwa amma ko babu komai tana samun sauki idan Inna ta wuni a gida.
Yau Yarima ke shirin zuwa kano gurin kakarsa zaune suke a palor mama ta kalleshi tace gaskiya babyna kana da kyau kamar balarabe "harka shirya kenan"? Da kai ya bata amsa taci gaba da cewa Allah ya kare min kai baby inaji a jikina kamar zuwanka gurin ammi alkairi ne tamkar zaka hadu da wani abu dazai saka farin ciki kuma ya zamo maka garkuwa a rayuwarka.
Ido ya zuba mata bayan ya gama jin jawabinta yai murmushi har dimple dinsa na lotsawa amma baiyi magana ba mikewa mama
tai tana kire hannunsa suka fita har mota tai masa rakiya kafin ta koma.
Lokacin daya dayai perking da mota a harabar gidan da mamaki Mustapha dake tsaye kafar shiga palor yake kallon motar da tunanin waye a ciki bai kare mamaki ba Yarima ya fito yana gyara agogon hannunshi domin shi kadai ya bata shi mutum ne wanda baya bukatar takurar wasu fadawa ko bayi duk inda zaije shi kadai yake zuwa ko driver baya bukata.
Dagowa yai sukai ido biyu da Mustapha wani ihu yai yana rungumeshi cikin nuna tsantsar murna yace abokina kaine dama zan ganka kwana kusa gaskiya nayi kewarka yaushe raban da mu hadu kusan shekara biyu fa murmushi Yarima yai yana kallon shi yace sorry ba gani yau nazo muje ciki na gaji inason na huta shiga sukai wata farar mace ta dago tana kallonsu tace dama saida tunani na ya bani tunda naji Mustapha na ihu yana cewa abokina nace nasan kaine ba wanda zaizo yayi wannan haukan sai kai ta karasa maganar da murmushi.
Rungumeta Yarima yai a rayuwarsa yana matukar son ammi Mustapha ne ya fara dariya yana cewa wato Abdul-malik har yanzu baka janye wannan dabi'ar taka ba yanzu runguma ce gaisuwa dagowa yarima yai yana kallon ammi alamar ta tanka Musty yace malam bafa zakazo ka sanya tsohuwata magana ba ka baro taka acan tana hutawa zaka wani takura min tawa harararsa Yarima yai kafin ya mike yana cewa muje na gaji inason na huta bani da lokacin ka wucewa sukai yana cewa ammi bari ya dan huta.
Zainab ce zaune a tsakar gida tana hada kunun aya Bilki ta fito a daki tana cewa Zainab me kikeyi anan? dagowa ta tana kallonta tace kunun aya nake hadawa
[11/25, 5:27 PM] Yusrah Musa Abubakar: Innalillahi dan Allah amin afuwa ban gama typing ba nayi sanding.
*👑Yarima Abdul-malik 👑*
#Yusrah m Abubakar
[email protected]
*💫ANNURI WRITES ASSOCIATION💫*
*Page 3
Tana kallota tace "kunun aya nake hadawa".
Kudi ta mika mata jeki sayo min kayan miya bari na rika dura miki to Zainab tace tana amsar kudin tasa hijab ta fita a gidan Aliya ce ta shigo tana cewa, a'a Bilki harda kunun aya kika koma yine? Um lallai liyafa taci gaba ta karasa maganar tana zama a kujerar da Zainab ta tashi sai a sannan Bilki tai magana "a'a ba nawa bane na Zainab ne makaranta zata tafi dashi jin haka yasa Aliya tabe baki tace wallahi shiyasa duk yarinyar nan tabi ta rainaki ashe guri ta samu kina mata bauta Bilki zatai mgn Zainab ta dawo dan haka tai shiru aje kayan miyan tai tana dauka jakanta ta fita a gidan haduwa sukai da hindu a karshen layin anguwar suna tsaye da wani bata ko kalli gurinsu ba ta tsaida napep ta shiga.
A shirye suka fito shida Musty zai rakashi makaranta dan lecturer ne ammi ce ta kalli Yarima cikin wasa tace me soja zaije yi makaranta karfa ka firgita dalibai dan murmushi yai yana kallonta yace, dama ana gane soja ne ko baisa kaya ba? Dariya Musty yai ana ganewa mana musamman rashin fara'arka.
Mikewa yai yace to naji muje tunda ban sako dakai ba fita sukai suna shiga mota basu zame ko'ina ba sai makaranta babu yadda Musty baiyi ba akan ya karasa office dinsa amma yaki yace ya barshi anan idan yana bukata zai biyoshi hade rai Musty yai zaiyi magana Yarima yace masa "sorry"cikin haushi yace a'a uban sorry dan iska kawai wucesa yai shi kuma ya tsaya jikin motar yana waya da mama kamar saida akazo saitin kunnensa aka kwalla kiran Zainab wallahi ki tsaya kibani abuna idan na kama ki zaki sani haka kawai xuciyarsa ta tunzura shi ya kalli inda ake maganar idonsa ne ya sauka akan Zainab dake tsaye tana dariya rike da fefa a hannunta tana kalla alamar karantawa take wani irin kallo ya bita dashi cikin mamakin da baisan yayi hakan ba.
Karasowa waccen din tayi zata kama ta sukayi wani lungu da gudu dan dafe kirjinshi yai tare da runtse ido Musty ne ya dafa shi bai dago ba cikin mamaki yace abokina yadai meke faruwa? Shiru yarima yai ba tare daya bashi amsa ba saima shiga mota dayai abin ne ya daurewa Musty kai dan haka shima shiga yai daidai zaiyiwa motar key ya kuma cewa Abdul-malik wai dan Allah meke damunka naga gabadaya ka canja ba haka muka taho ba kodai kayi gamo ne? Wata uwar harara Yarima ya sakar masa batare da yace kala ba rabuwa dashi Musty yai dan ba amsa zai samu ba.
Koda suka koma gida ma kasa samun nutsuwa yai daya rufe ido ita yake gani lokacin da take dariya gabadaya ko abinci bai samu yaci ba har dare.