Sashe 8
Rayuwar Rayhana Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
RAYHANAH A KAZAURE
Rayuwar Rayhanah a Informatics, have brought new insights a kowanne fanni na ci gaban rayuwarta. Malaman duk Asians ne, mostly Indians da Singaporeans.
Ba neman kawaye ya kaita ba, don haka ba ta tsaya neman sabo da kowa ba. Tsakaninta da ‘yan hostel da ‘yan ajinsu gaisuwa ce ta Musulunci ta hanyar sallama da musabaha.
Rahane ba ta wasa da addininta, ba ta wasa da sallolinta guda biyar a kan lokaci, duk sanyi, duk zafi, duk ruwan sama basa hanata yinsu tare da liman a masallaci.
Da farko ta samu kanta cikin rikicewa da rudanin ganin kamar karatun ya fi karfinta. Amma a hankali da taimakon malamanta, ta soma gane kan karatun nasu, har ta hada da wayar da kan wadanda basu gane ba cikin ‘yan ajin nasu a lokacin da babu darasi (Tutorial).
Satinta biyu a Kazaure ba ta taba kunna wayar da Daddy ya bata ba, sai wata ranar Lahadi da yamma bayan ta gama duk abin da za ta yi. Tana ninke kayanta ne wayar ta fado daga inda ta tusa ta, domin a wurin Rahane ai sai da matsala ko lalura waya take da amfani.
Haka nan ta samu kanta da son sanyata a caji. Bayan awa daya ta cika ta kwanta a rigingine a gefen gadonta, kyan wayar ya isa, ba ta taba ganin waya mai kyan wannan ba.
Tana kunnawa sakonni hudu suka shigo, na farko daga Daddy ne, lafiyarta yake tambaya da yanayin karatun nasu, a karshe ya kare da yi mata addu’a da fatan alheri.
Sako na biyu babu suna, sai dai anyi saving lambar da ‘husband’. Wane ne husband? Ba ta sani ba. Ga abin da ke rubuce.
“Idanuwana sun makance a laluben neman uwar ‘ya’yana. Shekara da shekaru zuciya na fada min ba za ka sameta nan kusa ba. Sai dai kuma Allah ya yanke min wahalar a lokacin da ban zata ba. To amma Rayhanah wife din ba ta san ina yi ba”.
Ba ta fahimci komai ba, amma da ta ji an ambaci sunanta ta tabbata sakon nata ne. To wane ne ya turo? Lambar ba iri daya ce da ta Daddy ba.
Sai ta matsa ga sako na gaba.
“Wani lokacin idan na yi yunkurin in bayyana kaina gareta, sai kwarjininta da fargabar yadda zata karbi al’amarin ya hanani, saboda matsayin da ta bani ba matsayi ne na uban ‘ya’yanta ba.
Mai yiwuwa kuma ba zan zama irin zabin mijin da take so ba, sai ta yi amfani da karamci da halarci ta karbe ni, wanda nikuma bana son hakan. Rayhanah soyayyarta nake nema, ba halacci da karamci ba”.
Sako na gaba.
“Bude zuciyarki ki sanya mata wani hoto na wani mutum da kika yiwa farin sani. Kin bashi matsayi kala-kala a rayuwarki, amma cikin kwayar idonki bai taba ganin SO ba! Rayhanah sai girmamawa da sadaukarwa! When he decided to turn the relationship to a more complex one, more important, more valued, ya zamo ya shigo cikin rayuwarki ta kowanne bangare right, left and central........ would it be accepted?”
Ba ta san sanda ta yi murmushi ba, haka nan ta samu kanta da yin replying a gajarce.
“Who is he???”
“Someone that love u unconditionally Rayhanah!!!y”.
A dai-dai lokacin ne kuma kiran waya ya shigo daga wata lambar daban wadda babu ita cikin wadanda Baba Dacta ya yi saving. Hakan bai hanata dagawa ba, Yaya Khalipha ne.
Yadda ya ji muryarta tana rawa sanda take gaisheshi sai ya ji babu dadi, bai so ya yi hakan ba, da ya san zai sata cikin damuwa. To amma bai da mafita sai hakan, don baya son ya yi mata fin karfi. Ya sani ya kuma tabbata ba ta taba yin mu’amala da wani namiji ba a rayuwarta, balle ya yi tunanin tana son wani. A shekarunta na yanzun (goma sha takwas) a ganinsa ta isa ta tantance abin da take so da wanda ba ta so.
“Ya na ji muryarki kamar tana rawa?”
Ta yi ajiyar zuciya ta ce, “Wasu sakonni aka turo min Yaya Khalipha, na kasa gane musu”.
“Wa ya turo?”
“I don’t know!”
Ta fada a hankali. Domin a wurin Rahane rashin tarbiya ne a ce maka (I love you) har da unconditionally.
Khalipha sai ya yi murmushi, ya sake kwanciya sosai cikin sofa din bed room dinsa.
“Me ya ce cikin sakon?”
Ta yi ajiyar zuciya ta ce, “Something like rashin kunya Yaya Khalipha”.
Dariya ya yi mara sauti. Ya lumshe ido cikin murya kasa-kasa ya ce, “Ya ce miki I love you ne?”
Sai da ta rufe fuska sannan ta ce, “Eh mana”.
Ya ce, “To ke baki son shi?”
Ta girgiza kai ta ce, “Yaya Khalipha a bar maganar nan, ni bana son irin wannan maganar”.
“Why Rayhanah? Kin girma fa, amma ki kasa sanin abin da duk mai shekaru kamar naki ya kamata ya sani?”
Shiru ta yi, wanda ya ba shi damar ya fallasa kansa kawai komai ta fanjama-fanjam. Ya ce, “Idan kuma nine fah?”
Ta zaro ido sannan ta rufe da karfi, ta kasa cewa da shi komai.
Shiru ta ratsa na wani ‘yan dakikai, zuciyoyinsu da gangar jikinsu ke aiki iri daya. Rahane ta dade tana son Yaya Khalipha, sai dai ita kanta ba ta san cewa son nashi take yi ba. Ta dauka kawai shakuwa ce da kauna a dalilin kulawar da ya nuna cikin rayuwarta. Sai dai ba ta taba kawo wani abu da ya wuce wannan cikin zuciyarta ba. A yau da Khalipha ya yi mata wannan misalign, sai ya zamanto kamar yayi fami ne akan tsohon gyambo, sai kaunar da kwantacciyar soyayyar suka taso gaba daya.
Soyayyar da Khalipha ke yiwa Rayhanah yana jinyarta shekara da shekaru unexpressable ce. Don haka a yau daga Khalipha har Rayhanah babu wanda ya yi barcin kirki, tunda ya ji ta yi shiru ba ta da niyyar tankawa ya kashe wayar. Bai kuma kara kiranta ba sai bayan kwana biyar.
Kwanaki biyar din nan tamkar shekaru biyar ne a wurin Khalipha. Duk da haka ya daure bai kira Rayhanah ba, yana so ya ba ta sarari ne ta karbi soyayyarsa a hankali.
Ita kuma Rahane sai ta ji dadi da bai kara kiran nata ba, don in da wanda take jin nauyi yanzu a duniya, to Yaya Khalipha ne. Sai dai ita ma kwanakin sun dafa ta, har ta dafu lugub.
Sai dai wani mafarki da ta yi a kan Khalipha ya tsaya mata a rai matuka, a rana ta hudu da yin wayarsu. A al’adarta idan ta yi mafarki ta tashi ba ta kara tunawa da shi, amma ta rasa dalilin da yasa ta kasa manta wannan mafarkin.
Cikin wata gona ce mai cike da korran gangayyaki, ga kayan itatuwa nunannu irin su goba, kashu, inibi, tuffah, mangoro har da fasa-dabur da roman, yara goma kyawawa lafiyayyu na ta tsinkowa suna kawo mata inda take zaune cikin wani gado na alfarma.
“Momi ga kashu......Momi ga roman...... Mommy ga Inab.....”
Sai ta ce musu, “To ku raba su biyu, ku kai wa Daddy rabi ga shi can”. Ta nuna musu managarcin mutum da ke tsaye yana yiwa fulawoyi ban ruwa. Ya juya bayansa, wanda take da tabbacin Khalipha ne.
Da gudu yaran suka doshe shi ko wanne irke da kayan marmari nunanne na karshe.
“Take it Daddy..... Momy ta ce mu kawo maka, she said she love you much...... and we love u either...... do you love us, Dad?”
Sai ya juyo da murmushi yana karba yana gutsira yana basu, ya janyo su duka ya rungume yana cewa, “Daddy love you too...... and he love mummy as well, a kiss plzzzz???”
Ya tura musu kumatunshi, ko juyowar da ya yi ne ta bata damar ganin fuskarsa. Ba Khalipha bane….. IBRAHEEM NE!.
Wannan mafarki ya tsaya a zuciyar Rayhana, mene ne hadinta da Ibraheem da har take mafarkinsa? Mutum na farko da ta tsana saboda girman kansa. Duk da ba ta da shekaru masu yawa sanda Ibraheem ya bar Nigeria, ta yi mishi farin sani, ba ta kuma manta halayensa ba.
Idan za ta fassara mafarkinta, yana nufin Ibraheem shine uban ‘ya’yanta? “Noooo!!!” Ta fada a fili. Mafarki ne kawai ba gaskiya bane, kuma ba duka mafarki ne yake gaske ba. Don tasa abin a ranta ne kawai.
Ko da kiran Khalipha ya shigo a rana ta biyar, Rahane kasa dagawa ta yi saboda jin nauyi da nauyin zuciya hadi da rashin abin ce masa.
Bai yi fushi ba ya ci gaba da kira a kai a kai amma ta kasa dagawa. Zuciyarta bugawa take yi a duk lokacin da sunan Yaya Khalipha ya bayyana a screen din wayar.
Da ya kira a karo na bakwai sai ta yi shahada ta daga a hankali wayar na neman subucewa saboda rawar da hannunta ke yi.
Khalipha ya yi ajiyar zuciya a galabaice ya ce,
“Rayhanah sabauta ni kike so ki yi? Laifin me na yi miki haka da kika zabi ki azabtar dani ta wannan hanyar?’
Shiru ta yi. Da ya tabbatar bata da amsar ba shi sai ya ce,
“Alright, maybe am not good enough to be your husband. Bari in barki ki huta. Good night”. Ya kashe wayar.
Rayuwar Rayhanah a Informatics, have brought new insights a kowanne fanni na ci gaban rayuwarta. Malaman duk Asians ne, mostly Indians da Singaporeans.
Ba neman kawaye ya kaita ba, don haka ba ta tsaya neman sabo da kowa ba. Tsakaninta da ‘yan hostel da ‘yan ajinsu gaisuwa ce ta Musulunci ta hanyar sallama da musabaha.
Rahane ba ta wasa da addininta, ba ta wasa da sallolinta guda biyar a kan lokaci, duk sanyi, duk zafi, duk ruwan sama basa hanata yinsu tare da liman a masallaci.
Da farko ta samu kanta cikin rikicewa da rudanin ganin kamar karatun ya fi karfinta. Amma a hankali da taimakon malamanta, ta soma gane kan karatun nasu, har ta hada da wayar da kan wadanda basu gane ba cikin ‘yan ajin nasu a lokacin da babu darasi (Tutorial).
Satinta biyu a Kazaure ba ta taba kunna wayar da Daddy ya bata ba, sai wata ranar Lahadi da yamma bayan ta gama duk abin da za ta yi. Tana ninke kayanta ne wayar ta fado daga inda ta tusa ta, domin a wurin Rahane ai sai da matsala ko lalura waya take da amfani.
Haka nan ta samu kanta da son sanyata a caji. Bayan awa daya ta cika ta kwanta a rigingine a gefen gadonta, kyan wayar ya isa, ba ta taba ganin waya mai kyan wannan ba.
Tana kunnawa sakonni hudu suka shigo, na farko daga Daddy ne, lafiyarta yake tambaya da yanayin karatun nasu, a karshe ya kare da yi mata addu’a da fatan alheri.
Sako na biyu babu suna, sai dai anyi saving lambar da ‘husband’. Wane ne husband? Ba ta sani ba. Ga abin da ke rubuce.
“Idanuwana sun makance a laluben neman uwar ‘ya’yana. Shekara da shekaru zuciya na fada min ba za ka sameta nan kusa ba. Sai dai kuma Allah ya yanke min wahalar a lokacin da ban zata ba. To amma Rayhanah wife din ba ta san ina yi ba”.
Ba ta fahimci komai ba, amma da ta ji an ambaci sunanta ta tabbata sakon nata ne. To wane ne ya turo? Lambar ba iri daya ce da ta Daddy ba.
Sai ta matsa ga sako na gaba.
“Wani lokacin idan na yi yunkurin in bayyana kaina gareta, sai kwarjininta da fargabar yadda zata karbi al’amarin ya hanani, saboda matsayin da ta bani ba matsayi ne na uban ‘ya’yanta ba.
Mai yiwuwa kuma ba zan zama irin zabin mijin da take so ba, sai ta yi amfani da karamci da halarci ta karbe ni, wanda nikuma bana son hakan. Rayhanah soyayyarta nake nema, ba halacci da karamci ba”.
Sako na gaba.
“Bude zuciyarki ki sanya mata wani hoto na wani mutum da kika yiwa farin sani. Kin bashi matsayi kala-kala a rayuwarki, amma cikin kwayar idonki bai taba ganin SO ba! Rayhanah sai girmamawa da sadaukarwa! When he decided to turn the relationship to a more complex one, more important, more valued, ya zamo ya shigo cikin rayuwarki ta kowanne bangare right, left and central........ would it be accepted?”
Ba ta san sanda ta yi murmushi ba, haka nan ta samu kanta da yin replying a gajarce.
“Who is he???”
“Someone that love u unconditionally Rayhanah!!!y”.
A dai-dai lokacin ne kuma kiran waya ya shigo daga wata lambar daban wadda babu ita cikin wadanda Baba Dacta ya yi saving. Hakan bai hanata dagawa ba, Yaya Khalipha ne.
Yadda ya ji muryarta tana rawa sanda take gaisheshi sai ya ji babu dadi, bai so ya yi hakan ba, da ya san zai sata cikin damuwa. To amma bai da mafita sai hakan, don baya son ya yi mata fin karfi. Ya sani ya kuma tabbata ba ta taba yin mu’amala da wani namiji ba a rayuwarta, balle ya yi tunanin tana son wani. A shekarunta na yanzun (goma sha takwas) a ganinsa ta isa ta tantance abin da take so da wanda ba ta so.
“Ya na ji muryarki kamar tana rawa?”
Ta yi ajiyar zuciya ta ce, “Wasu sakonni aka turo min Yaya Khalipha, na kasa gane musu”.
“Wa ya turo?”
“I don’t know!”
Ta fada a hankali. Domin a wurin Rahane rashin tarbiya ne a ce maka (I love you) har da unconditionally.
Khalipha sai ya yi murmushi, ya sake kwanciya sosai cikin sofa din bed room dinsa.
“Me ya ce cikin sakon?”
Ta yi ajiyar zuciya ta ce, “Something like rashin kunya Yaya Khalipha”.
Dariya ya yi mara sauti. Ya lumshe ido cikin murya kasa-kasa ya ce, “Ya ce miki I love you ne?”
Sai da ta rufe fuska sannan ta ce, “Eh mana”.
Ya ce, “To ke baki son shi?”
Ta girgiza kai ta ce, “Yaya Khalipha a bar maganar nan, ni bana son irin wannan maganar”.
“Why Rayhanah? Kin girma fa, amma ki kasa sanin abin da duk mai shekaru kamar naki ya kamata ya sani?”
Shiru ta yi, wanda ya ba shi damar ya fallasa kansa kawai komai ta fanjama-fanjam. Ya ce, “Idan kuma nine fah?”
Ta zaro ido sannan ta rufe da karfi, ta kasa cewa da shi komai.
Shiru ta ratsa na wani ‘yan dakikai, zuciyoyinsu da gangar jikinsu ke aiki iri daya. Rahane ta dade tana son Yaya Khalipha, sai dai ita kanta ba ta san cewa son nashi take yi ba. Ta dauka kawai shakuwa ce da kauna a dalilin kulawar da ya nuna cikin rayuwarta. Sai dai ba ta taba kawo wani abu da ya wuce wannan cikin zuciyarta ba. A yau da Khalipha ya yi mata wannan misalign, sai ya zamanto kamar yayi fami ne akan tsohon gyambo, sai kaunar da kwantacciyar soyayyar suka taso gaba daya.
Soyayyar da Khalipha ke yiwa Rayhanah yana jinyarta shekara da shekaru unexpressable ce. Don haka a yau daga Khalipha har Rayhanah babu wanda ya yi barcin kirki, tunda ya ji ta yi shiru ba ta da niyyar tankawa ya kashe wayar. Bai kuma kara kiranta ba sai bayan kwana biyar.
Kwanaki biyar din nan tamkar shekaru biyar ne a wurin Khalipha. Duk da haka ya daure bai kira Rayhanah ba, yana so ya ba ta sarari ne ta karbi soyayyarsa a hankali.
Ita kuma Rahane sai ta ji dadi da bai kara kiran nata ba, don in da wanda take jin nauyi yanzu a duniya, to Yaya Khalipha ne. Sai dai ita ma kwanakin sun dafa ta, har ta dafu lugub.
Sai dai wani mafarki da ta yi a kan Khalipha ya tsaya mata a rai matuka, a rana ta hudu da yin wayarsu. A al’adarta idan ta yi mafarki ta tashi ba ta kara tunawa da shi, amma ta rasa dalilin da yasa ta kasa manta wannan mafarkin.
Cikin wata gona ce mai cike da korran gangayyaki, ga kayan itatuwa nunannu irin su goba, kashu, inibi, tuffah, mangoro har da fasa-dabur da roman, yara goma kyawawa lafiyayyu na ta tsinkowa suna kawo mata inda take zaune cikin wani gado na alfarma.
“Momi ga kashu......Momi ga roman...... Mommy ga Inab.....”
Sai ta ce musu, “To ku raba su biyu, ku kai wa Daddy rabi ga shi can”. Ta nuna musu managarcin mutum da ke tsaye yana yiwa fulawoyi ban ruwa. Ya juya bayansa, wanda take da tabbacin Khalipha ne.
Da gudu yaran suka doshe shi ko wanne irke da kayan marmari nunanne na karshe.
“Take it Daddy..... Momy ta ce mu kawo maka, she said she love you much...... and we love u either...... do you love us, Dad?”
Sai ya juyo da murmushi yana karba yana gutsira yana basu, ya janyo su duka ya rungume yana cewa, “Daddy love you too...... and he love mummy as well, a kiss plzzzz???”
Ya tura musu kumatunshi, ko juyowar da ya yi ne ta bata damar ganin fuskarsa. Ba Khalipha bane….. IBRAHEEM NE!.
Wannan mafarki ya tsaya a zuciyar Rayhana, mene ne hadinta da Ibraheem da har take mafarkinsa? Mutum na farko da ta tsana saboda girman kansa. Duk da ba ta da shekaru masu yawa sanda Ibraheem ya bar Nigeria, ta yi mishi farin sani, ba ta kuma manta halayensa ba.
Idan za ta fassara mafarkinta, yana nufin Ibraheem shine uban ‘ya’yanta? “Noooo!!!” Ta fada a fili. Mafarki ne kawai ba gaskiya bane, kuma ba duka mafarki ne yake gaske ba. Don tasa abin a ranta ne kawai.
Ko da kiran Khalipha ya shigo a rana ta biyar, Rahane kasa dagawa ta yi saboda jin nauyi da nauyin zuciya hadi da rashin abin ce masa.
Bai yi fushi ba ya ci gaba da kira a kai a kai amma ta kasa dagawa. Zuciyarta bugawa take yi a duk lokacin da sunan Yaya Khalipha ya bayyana a screen din wayar.
Da ya kira a karo na bakwai sai ta yi shahada ta daga a hankali wayar na neman subucewa saboda rawar da hannunta ke yi.
Khalipha ya yi ajiyar zuciya a galabaice ya ce,
“Rayhanah sabauta ni kike so ki yi? Laifin me na yi miki haka da kika zabi ki azabtar dani ta wannan hanyar?’
Shiru ta yi. Da ya tabbatar bata da amsar ba shi sai ya ce,
“Alright, maybe am not good enough to be your husband. Bari in barki ki huta. Good night”. Ya kashe wayar.