Sashe 11
Rayuwar Rayhana Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Saboda gigicewa Khalipha bai tsaya kara ko mintuna biyar cikin gidan ba, ya juya kan motarshi ya dauki hanyar Abuja.
Karfin zuciya irin ta namiji da karfin imani da tasirin addu’a su suka kawo Khalipha Abuja lafiya, amma ba nutsuwar tuki ba.
Maganar a ce ya hakura da Rayha ma ba mai dadin ji ba ce a kunnensa, gara a soka mai allurai dari ba daya da wannan furucin na Mami, wai ya ce da Baba Dacta ya fasa auren Rayhanah. Ta ya ya? Ta ina? Ta wace hanya? Da wane bakin da wace fuskar zai je ya fadi hakan?”
Sai dai fa wani bangare na zuciyarsa na gaya masa, wannan fa umarni ne na MAHAIFIYA, wanda bai isa ya musunta shi ba. Don haka Khalipha ya shiga wani irin tashin hankali da bai taba shiga irinsa ba. Har kullum Mami da Daddy abin da suke so suke musu, don haka ba duka kalubalen rayuwa suka sani ba. Basu san su so abu ko yaya su rasa ba balle soyayyar zuciyarsa ga Rayhanah! Wadda yakeda yaqinin an halicci zuciyarsa ne tare da sonta, kowanne bugunta kuma ke tafiya tareda kaunarta.
Don haka haqiqatan baima san takamaman inda son Rayhana yake ba specifically azuciyarsa, balle yasa wuka ya yanko mata shi, tunda ya mamaye zuciyar duka, sai dai Mami ta tsigeta gabadaya (zuciyar) daga shi har ita kowa ya huta.
Bayan kaduwa da tsorata, yana cikin mamakin ashe halin mutum yana canzawa haka farat daya daga mai kirki da sanin ciwon kai zuwa mara kirki da tunani?
Iyaka hangensa bai ga hujjar Mami kwakkwara guda ta haramta masa abin da yake so shekaru har takwas da doriya ba, bayan kuma ya riga ya sanar da mahaifinsa ya yi na’am, me Mami take so Daddy ya dauke shi?
Idan ya je ya ce ya fasa auren Rayhanah? Fiye da wannan ma, ya ya rayuwar za ta kasance idan babu Rahane a ciki? Mene ne hujjar Mami na cewa lallai sai ya auri ‘yar kawarta? Ita ba kwadayi ba, su ba kwadayi ba, me Mami take nufi ne? Ka taba auren wadda baka taba jin kana so ba? To ta yaya za ku rayu?
Shi fa ba wai so kawai yake yiwa Rayhanah ba, har da son ya tallafi rayuwarta ya ingantata, idan bai aure ta ba wani ne can da bai san darajarta ba bai san mutuncinta ba zai aure ta.
A yadda mazan yanzu suka mayar da aure kamar sanya riga da tube ta ga ‘ya’yan gata ma ba marayu marasa madafa irin Rayhanah ba, wane ne zai aure ta ya daraja ta? Ya rike musu ita irin yadda sukeso shida Daddy???
Bai yi aune ba sai ji ya yi wani ruwa mai dumi yana fita daga idonsa. Da ya kai hannu ya sharesu, wasu ne suka kara shimfidowa aguje. Wannan karon bai yi wata hobbasa ta hanasu zubowar ba, kyalesu ya yi suka yi ta shatata, fitarsu na rage masa suyar da kirjinsa ke yi.
A gida ko ofis, cikin kwanaki biyun nan Khalipha ya gama fita daga hayyacinsa. Ya rufe waya, ya kasa aiki a ofis, ga shi ya yiwa Mami alkawarin barin shan Marlboro balle ya sha ta wanke mai zuciya. Maimakon hakan ya yanke shawarar fara shan zam-zam ya zamo masa ruwan sha.
A hankali sai ya ji tunanin da yai yawa da katutu cikin kwakwalwarsa da zuciyarsa na raguwa, nutsuwa ta zo mishi, addu’a kawai yake da nafilfili Allah ya sauko da zuciyar Mami, don dai ya kasa aiwatar da umarninta har yau.
An debi kwanaki har hudu, Khalipha bai cika umarnin Mami ba, ya kashe waya tun dawowarsa. Itama Rahanen baya kiranta, don baya son ya zamo heart breaker a gareta. Ko da yake dai-dai da second daya bai taba tunanin wai zai iya hakurin da ita ba.
Mami ta neme shi a waya har ta gaji, domin tana son aiwatar da kudirinta a kan Rayha da Khalipha kamin Daddy ya dawo ne kada ya bata mata lamari. A yau saura kwanaki biyu Dr. Mansur ya dawo Najeriya.
Cikin daren Khalipha ya kasa barci ya kuma kasa kunna waya. Ya lura Mami so take ta zurma shi cikin laifin shi kadai wajen Daddy ba tare da sunanta ya fito ba.
“Ya Allah me ya samu mahaifiyata ne haka? Ya Allah me na yiwa Mami da a yau ta gwammace in sarayar da farin cikin rayuwata a banza? Saboda Rayha ta fito daga tsattson talakawa, ta yi cuta shine kawai hujjar a ki aurenta?
Mami ta manta ita ma tana da ‘ya’ya mata? Abin da ya faru da Rayha zai iya faruwa ga ‘ya’yanta, sai a ce kada a aure su?
Ita ‘yar masu kudin me za ta yi mata? Kudi za ta ba ta ko Makka za ta kaita? A iya sanin Khalipha Mami ta fi uwarta albashi mai tsoka, ubanta ne dan siyasa (arzikinku na dan wani lokaci) balle ya ce wani abu Mami ke hange a kan lamarin. Yadda take daukar al’amarin Dr. Halima da muhimmanci ba ta daukar na mijinta haka yanzu. Ta zama wata irin masifaffiya, ya tabbata muddin ya gayawa Daddy cewa ita ta ce ya yi kaza ya yi kaza Daddy zai sa mata katanga ma ba birki ba.
Ya kuma lura ita ma ta shirya daukar kowanne hukunci daga Daddyn idan ya tuno da kalamanta. Wanda ba zai so haka ba, a kan nasa auren ya raba na iyayensa. Kuma ta ce duk abin da ya biyo baya idan ya ki bin umarninta kada a ga laifinta. Wato za ta iya korar Rayhanah daga gidanta, ta fada wani hannu da basu sani ba tunda su ba mazauna bane daga shi har Daddy.
Wannan tunani da Khalipha ya yi ya razana shi ba dan kadan ba. Bai san sanda ya mika hannu ya dauko wayarsa daga kan center table ya kunnata ba. Bai tsaya karanta sakonnin dake ta tuttudowa cikin wayar ba, ya yiwa Mami text ya tura mata ya sake rufe wayar da sauri a lokacin da kiran Rayhanah ya shigo. Kuwa riris Khalipha yake yi wanda bai taba yin irinsa a rayuwarsa ba.
****
A lokacin da sakon Khalipha ya shiga wayar Dr. Asma’u tana ofis dinta tare da Dr. Halima suna ci gaba da kulle-kullensu na tsiya, a kan mutanen da basu ji ba basu gani ba, son zuciya kawai da raina talaka.
“Ya rufe wayar har yau na kasa samun shi, fargabata gobe Dr. zai dawo, so nake mu gama kafin ya dawo kada ya bata al’amarin don na rantse zai iya yin komai don ya nuna min bacin ransa, mafi kankantar ciki shine SAKI, ni kuma na shirya masa”.
Dr. Halima ta ce, “Wallahi kuwa, ko yau kasuwar ta watse dan koli ya ci riba. Wa zai dube ki ya ce kin haifi Jawahir ma balle Ibrahim da Khalipha? Wallahi za ki yi mamakin yadda consultants za su yo rubdugu a kanki. Dr. Mansur ya raina ki, ki yarda da abin da na ce, ya raina ki”.
Fuskar Dr. Asma’u ta muzanta kwarai, ba abin da ta tsana a rayuwarta irin raini. Babbar hujjarta ta kin Rahane kenan, ta fito daga tsatson raini, abin kunya cikin kawayenta da tsararrakin yin ta.
Shigowar sakon cikin wayarta yasa ta sassauta bacin fuskarta, ta dauki wayar ta bude.
“Uwata da na sani a baya farin cikina shine nata, babban tashin hankalinta shine shigata cikin damuwa, ko wani hali na kaka- nikayi. Mami would never lose her temper to such an extent....... shi yasa har yau na kasa yanke hukuncin yarda da abinda idanuwa da kunnuwa na suka jiye mini daga Mami. Ina cikin tantamar, anya Mamina ce???
A cikin kwanakin da ban yanke hukunci ba, so nake idan mafarki nake Allah ya farkar dani. Mamina ta asali za ta iya kadar da duk abin da ta mallaka saboda farin cikinmu. Sai nake tambayar manazarta halayyar dan Adam cewa, shin dama halin mutum yana canzawa a lokaci daya?
Tunda dai na yarda cewa ba mafarkin nake yi ba, cikin biyayyarki da umarninki na hakura da Rayhanah..... Allah ya ba ta wanda ya fini......ki ce Amin Mami ba don ni ba sai don kasancewarta Musulma ‘yar musulmai ‘yan’uwanmu.
Ni kuma ki aura min duk wadda ta yi miki Mami........ na yi miki alkawarin zama da ita har karshen rayuwata! Amma kada ki yi yunkurin raba gidan nan da Rahane Mami, ko don ki ceto mana aurenki da kwanciyar hankalin Daddy. Idan akwai biyayyar da ta fi wannan Mami ina rokon Allah ya bani ikon yi miki. A yau zan gayawa Daddy na hakura da RAYHANAH......na karbi zabin ki Mami. Ina neman albarkarki. Dan ki.
-Khalipha.
Ta dade tana maimaita karanta sakon dake neman karya mata zuciya, Dr. Halima na ta magana amma ba ta jinta. Sai ta kwace wayar ta soma karantawa. Farin cikinta ya kasa boyuwa a fuskarta.
Ta ce, “Ki ji yaro da lauya magana, wallahi sai ta tafi in ba haka ba ba’a rabu da Bukar ba an haifi Habu muddin tana cikin gidan yana ganinta. Ta ruwan sanyi za ta tafi babu duka babu zagi balle bakar magana”.
A nan ne Mamin ta yi magana, “Ina ganin mu kyale yarinyar nan Halima tunda dai an samu ya yi kokarin da ba’a zata haka cikin sauri ba. Baki san Khalipha ba a kan abin da yake so, kamar kuma yadda ya ce din ne AURENA zai yi tangal-tangal idan ya dawo ba ta gidan, babu kuma wata kwakkwarar magana kan inda ta shiga”.
Dr. Halima a fusace ta ce, “To shi kenan, na rantse kuwa za ta zama kishiyarki idan Khalipha bai aura ba. Kuma ai ba korarta za ayi ba, kiranye za ayi mata ta koma mahaifarta ko za a kasheta ba za ta yarda ta dawo ba. Ai muma Musulmai ne, ba cutarta zamu yi ba”.
Ta yadda da maganar Dr. Halima dari bisa dari har cikin ranta.
Karfin zuciya irin ta namiji da karfin imani da tasirin addu’a su suka kawo Khalipha Abuja lafiya, amma ba nutsuwar tuki ba.
Maganar a ce ya hakura da Rayha ma ba mai dadin ji ba ce a kunnensa, gara a soka mai allurai dari ba daya da wannan furucin na Mami, wai ya ce da Baba Dacta ya fasa auren Rayhanah. Ta ya ya? Ta ina? Ta wace hanya? Da wane bakin da wace fuskar zai je ya fadi hakan?”
Sai dai fa wani bangare na zuciyarsa na gaya masa, wannan fa umarni ne na MAHAIFIYA, wanda bai isa ya musunta shi ba. Don haka Khalipha ya shiga wani irin tashin hankali da bai taba shiga irinsa ba. Har kullum Mami da Daddy abin da suke so suke musu, don haka ba duka kalubalen rayuwa suka sani ba. Basu san su so abu ko yaya su rasa ba balle soyayyar zuciyarsa ga Rayhanah! Wadda yakeda yaqinin an halicci zuciyarsa ne tare da sonta, kowanne bugunta kuma ke tafiya tareda kaunarta.
Don haka haqiqatan baima san takamaman inda son Rayhana yake ba specifically azuciyarsa, balle yasa wuka ya yanko mata shi, tunda ya mamaye zuciyar duka, sai dai Mami ta tsigeta gabadaya (zuciyar) daga shi har ita kowa ya huta.
Bayan kaduwa da tsorata, yana cikin mamakin ashe halin mutum yana canzawa haka farat daya daga mai kirki da sanin ciwon kai zuwa mara kirki da tunani?
Iyaka hangensa bai ga hujjar Mami kwakkwara guda ta haramta masa abin da yake so shekaru har takwas da doriya ba, bayan kuma ya riga ya sanar da mahaifinsa ya yi na’am, me Mami take so Daddy ya dauke shi?
Idan ya je ya ce ya fasa auren Rayhanah? Fiye da wannan ma, ya ya rayuwar za ta kasance idan babu Rahane a ciki? Mene ne hujjar Mami na cewa lallai sai ya auri ‘yar kawarta? Ita ba kwadayi ba, su ba kwadayi ba, me Mami take nufi ne? Ka taba auren wadda baka taba jin kana so ba? To ta yaya za ku rayu?
Shi fa ba wai so kawai yake yiwa Rayhanah ba, har da son ya tallafi rayuwarta ya ingantata, idan bai aure ta ba wani ne can da bai san darajarta ba bai san mutuncinta ba zai aure ta.
A yadda mazan yanzu suka mayar da aure kamar sanya riga da tube ta ga ‘ya’yan gata ma ba marayu marasa madafa irin Rayhanah ba, wane ne zai aure ta ya daraja ta? Ya rike musu ita irin yadda sukeso shida Daddy???
Bai yi aune ba sai ji ya yi wani ruwa mai dumi yana fita daga idonsa. Da ya kai hannu ya sharesu, wasu ne suka kara shimfidowa aguje. Wannan karon bai yi wata hobbasa ta hanasu zubowar ba, kyalesu ya yi suka yi ta shatata, fitarsu na rage masa suyar da kirjinsa ke yi.
A gida ko ofis, cikin kwanaki biyun nan Khalipha ya gama fita daga hayyacinsa. Ya rufe waya, ya kasa aiki a ofis, ga shi ya yiwa Mami alkawarin barin shan Marlboro balle ya sha ta wanke mai zuciya. Maimakon hakan ya yanke shawarar fara shan zam-zam ya zamo masa ruwan sha.
A hankali sai ya ji tunanin da yai yawa da katutu cikin kwakwalwarsa da zuciyarsa na raguwa, nutsuwa ta zo mishi, addu’a kawai yake da nafilfili Allah ya sauko da zuciyar Mami, don dai ya kasa aiwatar da umarninta har yau.
An debi kwanaki har hudu, Khalipha bai cika umarnin Mami ba, ya kashe waya tun dawowarsa. Itama Rahanen baya kiranta, don baya son ya zamo heart breaker a gareta. Ko da yake dai-dai da second daya bai taba tunanin wai zai iya hakurin da ita ba.
Mami ta neme shi a waya har ta gaji, domin tana son aiwatar da kudirinta a kan Rayha da Khalipha kamin Daddy ya dawo ne kada ya bata mata lamari. A yau saura kwanaki biyu Dr. Mansur ya dawo Najeriya.
Cikin daren Khalipha ya kasa barci ya kuma kasa kunna waya. Ya lura Mami so take ta zurma shi cikin laifin shi kadai wajen Daddy ba tare da sunanta ya fito ba.
“Ya Allah me ya samu mahaifiyata ne haka? Ya Allah me na yiwa Mami da a yau ta gwammace in sarayar da farin cikin rayuwata a banza? Saboda Rayha ta fito daga tsattson talakawa, ta yi cuta shine kawai hujjar a ki aurenta?
Mami ta manta ita ma tana da ‘ya’ya mata? Abin da ya faru da Rayha zai iya faruwa ga ‘ya’yanta, sai a ce kada a aure su?
Ita ‘yar masu kudin me za ta yi mata? Kudi za ta ba ta ko Makka za ta kaita? A iya sanin Khalipha Mami ta fi uwarta albashi mai tsoka, ubanta ne dan siyasa (arzikinku na dan wani lokaci) balle ya ce wani abu Mami ke hange a kan lamarin. Yadda take daukar al’amarin Dr. Halima da muhimmanci ba ta daukar na mijinta haka yanzu. Ta zama wata irin masifaffiya, ya tabbata muddin ya gayawa Daddy cewa ita ta ce ya yi kaza ya yi kaza Daddy zai sa mata katanga ma ba birki ba.
Ya kuma lura ita ma ta shirya daukar kowanne hukunci daga Daddyn idan ya tuno da kalamanta. Wanda ba zai so haka ba, a kan nasa auren ya raba na iyayensa. Kuma ta ce duk abin da ya biyo baya idan ya ki bin umarninta kada a ga laifinta. Wato za ta iya korar Rayhanah daga gidanta, ta fada wani hannu da basu sani ba tunda su ba mazauna bane daga shi har Daddy.
Wannan tunani da Khalipha ya yi ya razana shi ba dan kadan ba. Bai san sanda ya mika hannu ya dauko wayarsa daga kan center table ya kunnata ba. Bai tsaya karanta sakonnin dake ta tuttudowa cikin wayar ba, ya yiwa Mami text ya tura mata ya sake rufe wayar da sauri a lokacin da kiran Rayhanah ya shigo. Kuwa riris Khalipha yake yi wanda bai taba yin irinsa a rayuwarsa ba.
****
A lokacin da sakon Khalipha ya shiga wayar Dr. Asma’u tana ofis dinta tare da Dr. Halima suna ci gaba da kulle-kullensu na tsiya, a kan mutanen da basu ji ba basu gani ba, son zuciya kawai da raina talaka.
“Ya rufe wayar har yau na kasa samun shi, fargabata gobe Dr. zai dawo, so nake mu gama kafin ya dawo kada ya bata al’amarin don na rantse zai iya yin komai don ya nuna min bacin ransa, mafi kankantar ciki shine SAKI, ni kuma na shirya masa”.
Dr. Halima ta ce, “Wallahi kuwa, ko yau kasuwar ta watse dan koli ya ci riba. Wa zai dube ki ya ce kin haifi Jawahir ma balle Ibrahim da Khalipha? Wallahi za ki yi mamakin yadda consultants za su yo rubdugu a kanki. Dr. Mansur ya raina ki, ki yarda da abin da na ce, ya raina ki”.
Fuskar Dr. Asma’u ta muzanta kwarai, ba abin da ta tsana a rayuwarta irin raini. Babbar hujjarta ta kin Rahane kenan, ta fito daga tsatson raini, abin kunya cikin kawayenta da tsararrakin yin ta.
Shigowar sakon cikin wayarta yasa ta sassauta bacin fuskarta, ta dauki wayar ta bude.
“Uwata da na sani a baya farin cikina shine nata, babban tashin hankalinta shine shigata cikin damuwa, ko wani hali na kaka- nikayi. Mami would never lose her temper to such an extent....... shi yasa har yau na kasa yanke hukuncin yarda da abinda idanuwa da kunnuwa na suka jiye mini daga Mami. Ina cikin tantamar, anya Mamina ce???
A cikin kwanakin da ban yanke hukunci ba, so nake idan mafarki nake Allah ya farkar dani. Mamina ta asali za ta iya kadar da duk abin da ta mallaka saboda farin cikinmu. Sai nake tambayar manazarta halayyar dan Adam cewa, shin dama halin mutum yana canzawa a lokaci daya?
Tunda dai na yarda cewa ba mafarkin nake yi ba, cikin biyayyarki da umarninki na hakura da Rayhanah..... Allah ya ba ta wanda ya fini......ki ce Amin Mami ba don ni ba sai don kasancewarta Musulma ‘yar musulmai ‘yan’uwanmu.
Ni kuma ki aura min duk wadda ta yi miki Mami........ na yi miki alkawarin zama da ita har karshen rayuwata! Amma kada ki yi yunkurin raba gidan nan da Rahane Mami, ko don ki ceto mana aurenki da kwanciyar hankalin Daddy. Idan akwai biyayyar da ta fi wannan Mami ina rokon Allah ya bani ikon yi miki. A yau zan gayawa Daddy na hakura da RAYHANAH......na karbi zabin ki Mami. Ina neman albarkarki. Dan ki.
-Khalipha.
Ta dade tana maimaita karanta sakon dake neman karya mata zuciya, Dr. Halima na ta magana amma ba ta jinta. Sai ta kwace wayar ta soma karantawa. Farin cikinta ya kasa boyuwa a fuskarta.
Ta ce, “Ki ji yaro da lauya magana, wallahi sai ta tafi in ba haka ba ba’a rabu da Bukar ba an haifi Habu muddin tana cikin gidan yana ganinta. Ta ruwan sanyi za ta tafi babu duka babu zagi balle bakar magana”.
A nan ne Mamin ta yi magana, “Ina ganin mu kyale yarinyar nan Halima tunda dai an samu ya yi kokarin da ba’a zata haka cikin sauri ba. Baki san Khalipha ba a kan abin da yake so, kamar kuma yadda ya ce din ne AURENA zai yi tangal-tangal idan ya dawo ba ta gidan, babu kuma wata kwakkwarar magana kan inda ta shiga”.
Dr. Halima a fusace ta ce, “To shi kenan, na rantse kuwa za ta zama kishiyarki idan Khalipha bai aura ba. Kuma ai ba korarta za ayi ba, kiranye za ayi mata ta koma mahaifarta ko za a kasheta ba za ta yarda ta dawo ba. Ai muma Musulmai ne, ba cutarta zamu yi ba”.
Ta yadda da maganar Dr. Halima dari bisa dari har cikin ranta.