Sashe 10
Rayuwar Rayhana Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
****
[12/24/2019, 21:47] Takori: Wannan shine dan mabudin da ya bude kofar soyayyar Rayhah da Khalipha. Alkunyarta, rashin son magana, saukin kai da kawaici, rikon addininta sune manyan halayen ta da suka jawo Khalipha gaba daya ya afka a rijiyar soyayya ruwan ya sha shi har wuyansa.
Duk yadda ya yi tsammanin Rayhanah ta wuce nan a qualities din da yake hasashen tana dasu, wadanda yake so a matar aurensa.
Washe garin ranar Daddy ya zo ya dauketa suka wuce Kano, ta kwana biyu ya maidota Talata saboda Monday aiki bai barshi ya samu sukuni ba, ba kuma zai sata a motar haya ba.
Yadda Rayha ta ga Mami cikin kwanaki biyun nan da ta yi abin ya tsoratata. Completely Mami ta canza kamar wahainiya, muraran take nuna ba ta son zaman Rayhanah a gidanta yanzu, duk da Baba Dacta bai fito fili ya gaya mata Khalipha son ta yake ba. Amma ya ce da ita aure zai mata ba za ta shiga B.U.K ba.
Ta tambaye shi waye mijin? Ya ce da ita, “Time will tell you!” sai tasa mishi ido tana cewa a ranta, “Kai ma lokacin zai gaya maka ko wace ce Anita Shiyana, tunda Asma’u ka sani.
Lallai gaskiyar Dr. Halima ta yi sakaci da yawa da Dr. Mansur, tana ganin cewa wai yana sonta, ba za ta taba bin malamai a kansa ba. Yanzu kam ta yarda cewa ta yi sakacin, tunda ya fara munafuntarta ya soma boye mata wasu al’amura da ya lura ba za ta yi na’am dasu ba.
Shi kuma har ga Allah zuciyarsa daya, bai ki gaya mata don munafurci ba sai don baya son bacin ranta ko nasa cikin al’amarin, ya fi son sai komi ya kankama tukunna sannan ya zauna ya yi mata bayani ya ba ta hakurin karya alkawarin da ya yi mata, a dalilin ajizanci irin na dan Adam.
Bai yi da niyya ba, bai hadasu ba su suka hada kansu. Shi dan bin umarnin Allah ne kawai da sunnar ma’aiki da ya ce idan ‘ya’yanku sun nuna suna son aure, to ku yi musu cikin umarnin Ubangiji.
Ban da haka shi bai taba hasaso Khalipha zai taba cewa yana son Rayhanah ba, yana dai da nashi burin a kan Rayhanan amma tunda Khalipha ya riga ya furta to ya kashe waccan kudirin nasa ya karbi wanda Allah ya bayyana.
Duk sati Khalipha na tafe, baya Abuja baya Kano, baya Kazaure. Wata muguwar shakuwa da fahimtar juna ta wanzu tsakaninsa da Rayhanah. Duk da cewa kullum shine mai nuna son, kalamanta tsada suke masa saboda kunyarta, in yana so ya ji furucin bakinta, to sai ya kirata da Rahane, ko ya ce matar Audu, a nan kam ba ta jurewa sai ta bayyana masa kyawawan hakoranta guda talatin da biyu.
Ba soyayya ce kadai tsakanin Khalipha da Rahane ba, akwai wani abu wai shi yarda da juna, kusancin zuciya da zuciya da amincin da ya zarta soyayya.
Ko Baba Dacta bai san Rahane yadda Khalipha ya yi mata kyakkyawan sani ba ciki da bai dinta. Ya san halinta, ya san abin da take so da wanda ba ta so. Ba ta da yawan ado, kuma ba ta cika kwalliya a jikinta, she is smart, and simple. Yana son Rayhanah har yadda ba zai iya kwatantawa ba. Yana son Rayhanah yadda shi kansa bai san adadin ba.
Yadda kwanaki ke gudu suna juyawa tamkar gare-gare abin wasan yara a wannan zamanin, don haka bai zamo abin mamaki ba idan aka ce har ga watanni takwas sun cika. Rahane ta fito da kwalin (International Diploma in Cyber Security) tare da admission na daukar ta degree a babban reshensu dake kasar Singapore, a matsayinta na (overall student).
Fadin irin farin cikin da Baba Dacta ya yi ba zai fadu ba, a take ya yiwa Khalipha waya yake sanar masa ita ma Mami ya sanar da ita tun kafin su iso Kano daga Kazaure.
Mami ta dade zaune a bakin gadonta tana mamaki, don dai akwai ‘ya’yan kawayenta da dama a Informatics fin shekaru uku sun kasa fita daga makarantar. A karshe sai bari suka yi aka yi asarar dubunnai. Da gaske Dr. Halima take idan har ba ta raba yarinyar nan da gidanta ba, ba ta gama shan mamaki ba.
A take ta bugawa Dr. Halima take sanar mata. Ta ce da ita kada ta damu komai ya zo karshe, amma ta shirya gobe su wuce Plateau (Jos) tushen Mami kenan, komai ya kammala karbowa kawai za suyi.
Don haka da suka iso ba ta yi wani action negatively a kan nasarar Rayhanan ba. Sai dai shi a can Khalipha ya shiga damuwa, yana tsoron kada Daddy ya yarda da batun tafiya yin digirin ba tare da anyi aurensu ba.
Don haka ranar Juma’a ya baro dukkan ayyyukansa ya taho Kano, abin haushin Daddy baya gari ya je Ireland wani taron karawa juna sani a kan cutar Otosclerosis a matsayinsa na ganau ba jiyau ba a kan fidarta, da aka yi aka kuma ci nasara a yankin Braemar.
Khalipha ya yi sallama a bedroom din Mami ba ta ji ba tana waya, kuma da yake ta bai wa kofa baya ba ta ga shigowar shi ba. Hirar da take yi a wayar bai fahimceta ba, amma kawai jikinshi ya ji ya yi sanyi da ya ji Mami na cewa, “Ko zan yi yawo tsirara haihuwar uwa da uba na Khalipha ba zai auri yarinyar nan ba”.
Ta ajiye wayar tana huci, a lokacin ne ta ankara da shigowarsa. Ta kasa saisaita fushinta ta kasa boye anger din da ta taso mata. Don haka kallon sa kawai ta yi ba ta ce masa komai ba.
A salube ya zauna a kusa da ita gwiwoyinsa babu kwari, duk da bai san wace yarinyar ake nufi ba tunda Allah bai nufe shi da jin an kama suna ba.
Khalipha ya san iya rayuwar Mami ba ta da makiyi, ba ta da mugun hali. To a kan wa take cin mugun alwashi haka? Ta dago idanunta jajir ta dube shi.
Cikin kakkausar murya ta ce, “ABDALLAH!”
A firgice ya dubeta saboda shi dai tsawon rayuwarsa bai taba ji ko da kuskure ta ambaci sunansa na ainihi ba, sai ko ranar da ta je gidansa a Abuja ta kama shi da babban laifi. Fargaba bata barshi ya amsa ba.
Ta ci gaba da cewa, “Duk abin da kuke ciki kai da ubanka na sani, tunda ban yi kama da wadda ba ta je makarantar boko ba. Amma ina so in ji sahihiyar amsa daga bakin ka, tunda Allah ya hana hukunci a kan zargi”.
Ya girgiza mata kai alamar yana sauraronta. Kafin ta jefo masa tambayar tata da ta shafe taraddadinsa.
“Wace ce yarinyar da kake so ka aura?”
Ba tare da nuku-nuku ba kai tsaye ya ce, “Rayhanah!’
Ta sake cewa, “Wane ne mijin da Dacta yake so ya aura mata?”
Ya nuna kirjinshi ba tare da ya yi magana ba wato “Shine”.
Mami ta girgiza kai, “Kai tsaye abin da zan iya cewa shine, ban amince ba! Watakila bai gaya maka alkawarin da muka yi da shi ba kamin in yarda da zaman yarinyar nan tare da mu. Kai kuma da fari ka munafunce ni, tunda har Abuja na taka na je saboda kai da damuwa da halin da kake ciki, amma ka ninke ni a bai-bai, saboda ka raina min hankali.
Me ka gani a jikin wannan yarinyar Khalipha ban da son zubar mana da kima da mutunci? Kaskantaccen asali, ragowar cuta, babu iyaye babu dangi, an ce ‘yar Takai ce uwarta da ubanta da kakarta sun rasu, to su daga sama suka fado kenan tunda basu da dangi?” Ta fidda manyan idanunta.
Khalipha tun daga kansa har yatsar kafarsa gumi yake, duk da sanyin split dake neman daskarar da mutanen dakin. Tunda ta fara magana bai ce mata komai ba, haka da ta dire tana sauraron jin ta bakinsa amma ya gaza ce mata komai.
Ta nuna shi da dan-alinta cikin matsanancin fushi ta ci gaba da magana, “Idan kana son zaman lafiya dani, to ka bar maganar nan, ka kai wa ubanka maganar Radhiyyah, idan fa har ni na haifeka na yi nakudarka bayan daukar ka cikin mahaifata har tsayin watanni tara cikin halin kaka-nikayi.
Ba ta yi isar da zan hada jini da ita ba. Wannan kawai ita ce magana. Idan ma ka je ka ce masa ka fasa kai masa zancen Radhiyya, idan ka ki kuma kada ka ga laifina a kan duk abin da ya biyo baya.
Kwanaki biyu kacal na baka ka je ka warware kullin naku kai da uban naka, in ba haka ba wallahi za ku sha mamaki, na shirya karbar kowanne bacin rai na Dacta, na shirya masa kana iya tafiya, wannan shine”.
****
[12/24/2019, 21:47] Takori: Wannan shine dan mabudin da ya bude kofar soyayyar Rayhah da Khalipha. Alkunyarta, rashin son magana, saukin kai da kawaici, rikon addininta sune manyan halayen ta da suka jawo Khalipha gaba daya ya afka a rijiyar soyayya ruwan ya sha shi har wuyansa.
Duk yadda ya yi tsammanin Rayhanah ta wuce nan a qualities din da yake hasashen tana dasu, wadanda yake so a matar aurensa.
Washe garin ranar Daddy ya zo ya dauketa suka wuce Kano, ta kwana biyu ya maidota Talata saboda Monday aiki bai barshi ya samu sukuni ba, ba kuma zai sata a motar haya ba.
Yadda Rayha ta ga Mami cikin kwanaki biyun nan da ta yi abin ya tsoratata. Completely Mami ta canza kamar wahainiya, muraran take nuna ba ta son zaman Rayhanah a gidanta yanzu, duk da Baba Dacta bai fito fili ya gaya mata Khalipha son ta yake ba. Amma ya ce da ita aure zai mata ba za ta shiga B.U.K ba.
Ta tambaye shi waye mijin? Ya ce da ita, “Time will tell you!” sai tasa mishi ido tana cewa a ranta, “Kai ma lokacin zai gaya maka ko wace ce Anita Shiyana, tunda Asma’u ka sani.
Lallai gaskiyar Dr. Halima ta yi sakaci da yawa da Dr. Mansur, tana ganin cewa wai yana sonta, ba za ta taba bin malamai a kansa ba. Yanzu kam ta yarda cewa ta yi sakacin, tunda ya fara munafuntarta ya soma boye mata wasu al’amura da ya lura ba za ta yi na’am dasu ba.
Shi kuma har ga Allah zuciyarsa daya, bai ki gaya mata don munafurci ba sai don baya son bacin ranta ko nasa cikin al’amarin, ya fi son sai komi ya kankama tukunna sannan ya zauna ya yi mata bayani ya ba ta hakurin karya alkawarin da ya yi mata, a dalilin ajizanci irin na dan Adam.
Bai yi da niyya ba, bai hadasu ba su suka hada kansu. Shi dan bin umarnin Allah ne kawai da sunnar ma’aiki da ya ce idan ‘ya’yanku sun nuna suna son aure, to ku yi musu cikin umarnin Ubangiji.
Ban da haka shi bai taba hasaso Khalipha zai taba cewa yana son Rayhanah ba, yana dai da nashi burin a kan Rayhanan amma tunda Khalipha ya riga ya furta to ya kashe waccan kudirin nasa ya karbi wanda Allah ya bayyana.
Duk sati Khalipha na tafe, baya Abuja baya Kano, baya Kazaure. Wata muguwar shakuwa da fahimtar juna ta wanzu tsakaninsa da Rayhanah. Duk da cewa kullum shine mai nuna son, kalamanta tsada suke masa saboda kunyarta, in yana so ya ji furucin bakinta, to sai ya kirata da Rahane, ko ya ce matar Audu, a nan kam ba ta jurewa sai ta bayyana masa kyawawan hakoranta guda talatin da biyu.
Ba soyayya ce kadai tsakanin Khalipha da Rahane ba, akwai wani abu wai shi yarda da juna, kusancin zuciya da zuciya da amincin da ya zarta soyayya.
Ko Baba Dacta bai san Rahane yadda Khalipha ya yi mata kyakkyawan sani ba ciki da bai dinta. Ya san halinta, ya san abin da take so da wanda ba ta so. Ba ta da yawan ado, kuma ba ta cika kwalliya a jikinta, she is smart, and simple. Yana son Rayhanah har yadda ba zai iya kwatantawa ba. Yana son Rayhanah yadda shi kansa bai san adadin ba.
Yadda kwanaki ke gudu suna juyawa tamkar gare-gare abin wasan yara a wannan zamanin, don haka bai zamo abin mamaki ba idan aka ce har ga watanni takwas sun cika. Rahane ta fito da kwalin (International Diploma in Cyber Security) tare da admission na daukar ta degree a babban reshensu dake kasar Singapore, a matsayinta na (overall student).
Fadin irin farin cikin da Baba Dacta ya yi ba zai fadu ba, a take ya yiwa Khalipha waya yake sanar masa ita ma Mami ya sanar da ita tun kafin su iso Kano daga Kazaure.
Mami ta dade zaune a bakin gadonta tana mamaki, don dai akwai ‘ya’yan kawayenta da dama a Informatics fin shekaru uku sun kasa fita daga makarantar. A karshe sai bari suka yi aka yi asarar dubunnai. Da gaske Dr. Halima take idan har ba ta raba yarinyar nan da gidanta ba, ba ta gama shan mamaki ba.
A take ta bugawa Dr. Halima take sanar mata. Ta ce da ita kada ta damu komai ya zo karshe, amma ta shirya gobe su wuce Plateau (Jos) tushen Mami kenan, komai ya kammala karbowa kawai za suyi.
Don haka da suka iso ba ta yi wani action negatively a kan nasarar Rayhanan ba. Sai dai shi a can Khalipha ya shiga damuwa, yana tsoron kada Daddy ya yarda da batun tafiya yin digirin ba tare da anyi aurensu ba.
Don haka ranar Juma’a ya baro dukkan ayyyukansa ya taho Kano, abin haushin Daddy baya gari ya je Ireland wani taron karawa juna sani a kan cutar Otosclerosis a matsayinsa na ganau ba jiyau ba a kan fidarta, da aka yi aka kuma ci nasara a yankin Braemar.
Khalipha ya yi sallama a bedroom din Mami ba ta ji ba tana waya, kuma da yake ta bai wa kofa baya ba ta ga shigowar shi ba. Hirar da take yi a wayar bai fahimceta ba, amma kawai jikinshi ya ji ya yi sanyi da ya ji Mami na cewa, “Ko zan yi yawo tsirara haihuwar uwa da uba na Khalipha ba zai auri yarinyar nan ba”.
Ta ajiye wayar tana huci, a lokacin ne ta ankara da shigowarsa. Ta kasa saisaita fushinta ta kasa boye anger din da ta taso mata. Don haka kallon sa kawai ta yi ba ta ce masa komai ba.
A salube ya zauna a kusa da ita gwiwoyinsa babu kwari, duk da bai san wace yarinyar ake nufi ba tunda Allah bai nufe shi da jin an kama suna ba.
Khalipha ya san iya rayuwar Mami ba ta da makiyi, ba ta da mugun hali. To a kan wa take cin mugun alwashi haka? Ta dago idanunta jajir ta dube shi.
Cikin kakkausar murya ta ce, “ABDALLAH!”
A firgice ya dubeta saboda shi dai tsawon rayuwarsa bai taba ji ko da kuskure ta ambaci sunansa na ainihi ba, sai ko ranar da ta je gidansa a Abuja ta kama shi da babban laifi. Fargaba bata barshi ya amsa ba.
Ta ci gaba da cewa, “Duk abin da kuke ciki kai da ubanka na sani, tunda ban yi kama da wadda ba ta je makarantar boko ba. Amma ina so in ji sahihiyar amsa daga bakin ka, tunda Allah ya hana hukunci a kan zargi”.
Ya girgiza mata kai alamar yana sauraronta. Kafin ta jefo masa tambayar tata da ta shafe taraddadinsa.
“Wace ce yarinyar da kake so ka aura?”
Ba tare da nuku-nuku ba kai tsaye ya ce, “Rayhanah!’
Ta sake cewa, “Wane ne mijin da Dacta yake so ya aura mata?”
Ya nuna kirjinshi ba tare da ya yi magana ba wato “Shine”.
Mami ta girgiza kai, “Kai tsaye abin da zan iya cewa shine, ban amince ba! Watakila bai gaya maka alkawarin da muka yi da shi ba kamin in yarda da zaman yarinyar nan tare da mu. Kai kuma da fari ka munafunce ni, tunda har Abuja na taka na je saboda kai da damuwa da halin da kake ciki, amma ka ninke ni a bai-bai, saboda ka raina min hankali.
Me ka gani a jikin wannan yarinyar Khalipha ban da son zubar mana da kima da mutunci? Kaskantaccen asali, ragowar cuta, babu iyaye babu dangi, an ce ‘yar Takai ce uwarta da ubanta da kakarta sun rasu, to su daga sama suka fado kenan tunda basu da dangi?” Ta fidda manyan idanunta.
Khalipha tun daga kansa har yatsar kafarsa gumi yake, duk da sanyin split dake neman daskarar da mutanen dakin. Tunda ta fara magana bai ce mata komai ba, haka da ta dire tana sauraron jin ta bakinsa amma ya gaza ce mata komai.
Ta nuna shi da dan-alinta cikin matsanancin fushi ta ci gaba da magana, “Idan kana son zaman lafiya dani, to ka bar maganar nan, ka kai wa ubanka maganar Radhiyyah, idan fa har ni na haifeka na yi nakudarka bayan daukar ka cikin mahaifata har tsayin watanni tara cikin halin kaka-nikayi.
Ba ta yi isar da zan hada jini da ita ba. Wannan kawai ita ce magana. Idan ma ka je ka ce masa ka fasa kai masa zancen Radhiyya, idan ka ki kuma kada ka ga laifina a kan duk abin da ya biyo baya.
Kwanaki biyu kacal na baka ka je ka warware kullin naku kai da uban naka, in ba haka ba wallahi za ku sha mamaki, na shirya karbar kowanne bacin rai na Dacta, na shirya masa kana iya tafiya, wannan shine”.
****