Sashe 20
Rayuwar Rayhana Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Bayyanar dangin Yalwati mahaifiyarta shi ya shafe firgicin da rudanin da zuciyarta ta shiga na auren mutumin da rabonta da shi shekaru goma cif, wadanda tsayinsu da shudewar su basu mantar da ita waye shi ba; Dan Mami! Wanda ta fi so fiye da kowa da komai a rayuwarta (YA HEEMU).
“An gudu ba a tsira ba, an rabu da Bukar an haifi Habu!!!”.
In ji masu iya magana. Har gara-gara ma Khalipha a kan son da Mami ke yiwa HEEMU da burirrikan da ta ci a kanshi. Wadannan tunane-tunane basu bar zuciyar Rahane ta huta ba a wannan dare, basu bar idanuwanta sun runtsa ba. Jin al’amarin take kamar almara.
Wane irin aure ne irin haka? An taba yin aure irin nata a duniya kuwa? Babu shiri? Babu zato babu tsammani? Babu so babu kauna daga kowanne bangare? Babu shakuwa babu alaqa? HIMU? I.M? IBRAHEEM MANSUR? Wai shine mijinta? Ya ALLAH! Idan mafarki nake kayi gaggawar farkar dani kafin na zama zautacciya!!! Rayhanah ta fada a fili tana mai kaiwa da komowa kamar mai yin safah da marwah a dakin data ke ciki.
Wane irin matsayi Baba Dacta ya bata ne a zuciyarsa haka? Me take das hi day a bata wannnan matsayin? Ba ta cancance shi ba, matsayinta bai kai nan ba! Hadin bai yi matching ba sam..... Ibrahim ya fi karfin ta!! Sau dubu gara Khalipha. Shi wannan ko babu komai akwai shakuwa da fahimtar juna akwai kuma shimfidar fuska idan babu ta tabarma ba wannan zundumemen dan bokon ba.
Ta daga hannunta na dama a hankali ta kalli warawaran farin zinare da Haj. Karima ta zura mata, wadanda Hakimi ya ce Sadakinta kenan. Sai walainiya suke a hannunta cikin rangwamen hasken lantarkin dake dakin da take kwance (bedroom din Haj. Karima). Wadanda karbarsu da ta yi sun tabbatar da cewa ta zama matar IBRHEEM, ba Khalipha ba.
Mafarke-mafarken da ta rinka yi a Informatics farkon kulluwar soyayyarsu da Khalipha a kan Ibraheem suka shiga dawo mata filla-filla, wadanda a yau ta fassarasu da cewa, Allah ne yake nuna mata Ibrahim shine uban ‘ya’yanta ba Khalipha ba.
To ya za ta yi da son Yaya Khaliphan? A wannan sabon matsayin nata na matar kaninsa? Daddy na nufin ta haka rami ta binne soyayyar Khalipha wanda har zuwa yanzu zuciyarta ta ki yarda da cewa ya ki aurenta ne don yaudara, sai ko don wani muhimmin al’amari beyond his ability. Haka nan zuciyarta ta yi masa wannan uzurin duba da tsayin lokacin da Khalipha ya diba cikin soyayyarta tun tana kankanuwa, wannan ba yaudara ba ce.
Laifinsa daya ya ki su magantu balle ta san daga ina matsalar take? Sai dai kaso tamanin cikin dari na zuciyarta ce mata yake “Daga Mami ne”.
To in daga Mami ne ya ya akai ta amince ayi da wanda ta fi so ta fi ciwa buri fiye da Khalipha?
Da ta ga wadannan lissafe-lissafe da saka da warwara da tunane-tunane na neman tarwatsa mata kwakwalwa da wargaza kwanyar kanta, ba kuma zasu samar mata da amsoshin data ke son sani ba, haka bazasu zamo solution ga halin da take ciki a yanzu ba, sai ta tattarasu duka ta mikawa Allah! Wahidun Qahharun!! Mai tsarawa bawa rayuwa ta inda bai zata ba.
Minsharin Inna Juma ya dameta, wadda suke kwance tare a dakin anyi mata shimfida a kan kilishi da filo sai kwasar rabar A.C take tana kwararo minshari mai sauti.
Kallonta Rahane ke yi cikin shudiyar fitilar barci dake kunne tana jin wani sanyi a zuciyarta.
Kafin wata sabuwar fargabar ta zo ta lullube mata zuciya........ yaushe za su hadu da Ibrahim? Yaushe zai zo? Da wace fuska zai karbi al’amarin? Wace irin karba zai yiwa auren nasu? Maganar so ma ta san babu ita in aka yi la’akari da irin yanayin rayuwarshi wadda ta sha bambam da ta Khalipha ta kowanne bangare.
Ita dai kam a yanzu zuciyarta neutral. Wato ba ta bayan kowanne bangare (neither tana son sa nor ba ta son sa). Lamarin zai kasance ne da fuskar da ya zo mata, da ita za ta karbe shi. Babu soyayya cikin zuciyarta kuma babu kiyayya, kai ita duk jinin Dr. Mansur ma abin so ne da girmamawa a gareta.
Ba don komi ba sai don cewa, su suka rufa mata asiri a lokacin da ta bude ido ta tsinci kanta tare dasu, babu kowa nata.
Ba ta taba kullatar Mami ba ko ta sawa ranta Mami ba ta sonta. Rikon shekara goma shag Dan da ba kai ka Haifa ba ba karamin sadaukarwa bane. Ta yarda da abin da Mami ke ikirari na cewa ba kinta take ba, asalinta ne da tsohuwar lalurar ta ya sanya bata isa ta hada zuri’a da ita ba.
Ita ma kuma ta yarda da cewa asalin nata (idan aka hada da nasu) kaskantacce ne. Sannan lalurar ta abin gudu ce ko don tsoron genetic wato gado. Sai dai kuma Mami ta mantacewa ba’a yiwa Allah wayo itama bata gada ba iftila’I ne na Ubangiji. Hakan baya nufin suma ba mutane ne da Ubangiji ya halitta don baya son su ba,kowa da kaddarar rayuwarsa in one way or the other! Dukkanmu masu nakasu ne idan bata nan ba ta can. Maganar asali kuwa Ubangiji guda ne ya halicce mu yana kuma son bayinsa bakidaya.
Ba don baya son su bane ya hana su ilimin, mulkin da arzikin, sai don cewa ko ‘yan yatsu bai yi mana su kai daya ba. There is always hierarchy...... a tsakanin bani-Adam. Abin da ta yarda da shi shine, “Inna akramakum indallahi atqakum”. Wato mafi girmanku a wajen Ubangiji shine wanda yafi tsoron sa.
Don haka zamu iya cewa, a wannan daren baki dayansa, idanuwan Rahane basu runtsa ba. A kan kunnenta aka kira Asubahi, sai ta yi amfani da damar don gusarwa da kanta damuwar da ta gallabeta ta addabeta, ba kuma za ta amfanata da komai ba.
Ta yo alwala ta fito ta tashi Inna Juma. Yayin da ta nabba’a a gaban mahaliccinta don nemawa zuciya, kwakwalwa da rayuwarta sauki a wajen Mai duka. Tana rokon sa ya cire mata firgici da faduwar gaban da take samun kanta a ciki, a duk lokacin da ta tuno ranar da zata yi arba da IBRAHEEM MANSUR TAKAI. Har yanzu tana tantama tana kuma shakkun kasancewar wai Ibraheem ne mijinta ba Khalipha ba.
A hankali ta kai duba ga warawaran hannun ta masu kara tabbatar mata da hakan, ta hanyar fidda dan sauti kas-kas da walainiyar da sukeyi a duk kankanin motsin da ta yi. Abubuwan ban mamakin rayuwa yawa garesu, wasu ma basu zo ba tukunna….. wasu ba’a fara su bama RAYHANAAAAH!!!
****
Washe gari ya kasance litinin, su Daddy tun jiya bayan daurin aure suka wuce Kano aka daura na Khalipha da Radhiyyah. Daddy shi ya biya sadaki da wara-waran zinare kamar yadda ya biya na Rayhanah. A take kuma gidan su amarya suka zarce da biki na tsere ma sa’a.
Ita dai Mami har zuwa lokacin ta gaza nutsuwa da samun kwanciyar hankali, don har zuwa lokacin Daddy bai bude baki ya ce mata komai game da Rayhanah ba, bai tambayeta ina Rayhanah ba, bai gaya mata auren wa aka daura a Takai ba.
Ba ta kara ganin Khalipha ba har zuwa lokacin, ya wuce Abuja ya mai da kansa kamar inji saboda aiki, ya ki yarda zuciyarsa ta kadaice ko kadan balle ta samu filin saka mishi damuwa, tashin hankalin jin cewa shi ba dan Baba Dacta bane ya shafe komi, wato ya fi karfin soyayyar Rayhanah wadda ya kira da sunan bygone issue. Sawun Giwa ya take na Rakumi kuma gaba da gabanta wai aljani ya taka wuta……….
Daddy ya gama masa komai tunda bai bar Rayhanah ta wulakanta ba, wanda shine babbar damuwarsa kuma babban abinda ke kara ingizashi cikin son ya aure ta ya tallafi rayuwarta bayan Kalmar SO, ya zaba mata miji na garari na likawa a goshi in ana likawa, wanda zurfin tunaninsa bai taba bashi kasancewar hakan ba. Damuwarsa daya, wace irin tarba Ibraheem zai yiwa Rahane ‘as a wife??? Yana yi mata fatan alheri.
Shi yanzu haka ma shirin zuwa Jos yake wajen dangin Mami na can don ya fara bincike a kan al’amarin mahaifin nasa, ya dangana da Hurghada. Ya mance da wata aba can wai amarya Radhiyyah.
Lafiya sumul Daddy ya tarbi Dr. Asma’u da fara’a da komai a sanda ya shigo gidan daga ofis ranar da ya dawo daga Takai, ta yi mishi barka da zuwa. Rungumeta ma yayi, ya ce,
“Mami naaa.....”
Ita ma ta ce,
“Dacta naaah....”
Tana loosing tie din wuyan shi.
“Ya aka baro su Hakimi?”
“Kowa lafiya”.
Ya zagayeta da hannayenshi.kanshi cikin wuyanta yana sunsunar ta yake fadin;
“An gudu ba a tsira ba, an rabu da Bukar an haifi Habu!!!”.
In ji masu iya magana. Har gara-gara ma Khalipha a kan son da Mami ke yiwa HEEMU da burirrikan da ta ci a kanshi. Wadannan tunane-tunane basu bar zuciyar Rahane ta huta ba a wannan dare, basu bar idanuwanta sun runtsa ba. Jin al’amarin take kamar almara.
Wane irin aure ne irin haka? An taba yin aure irin nata a duniya kuwa? Babu shiri? Babu zato babu tsammani? Babu so babu kauna daga kowanne bangare? Babu shakuwa babu alaqa? HIMU? I.M? IBRAHEEM MANSUR? Wai shine mijinta? Ya ALLAH! Idan mafarki nake kayi gaggawar farkar dani kafin na zama zautacciya!!! Rayhanah ta fada a fili tana mai kaiwa da komowa kamar mai yin safah da marwah a dakin data ke ciki.
Wane irin matsayi Baba Dacta ya bata ne a zuciyarsa haka? Me take das hi day a bata wannnan matsayin? Ba ta cancance shi ba, matsayinta bai kai nan ba! Hadin bai yi matching ba sam..... Ibrahim ya fi karfin ta!! Sau dubu gara Khalipha. Shi wannan ko babu komai akwai shakuwa da fahimtar juna akwai kuma shimfidar fuska idan babu ta tabarma ba wannan zundumemen dan bokon ba.
Ta daga hannunta na dama a hankali ta kalli warawaran farin zinare da Haj. Karima ta zura mata, wadanda Hakimi ya ce Sadakinta kenan. Sai walainiya suke a hannunta cikin rangwamen hasken lantarkin dake dakin da take kwance (bedroom din Haj. Karima). Wadanda karbarsu da ta yi sun tabbatar da cewa ta zama matar IBRHEEM, ba Khalipha ba.
Mafarke-mafarken da ta rinka yi a Informatics farkon kulluwar soyayyarsu da Khalipha a kan Ibraheem suka shiga dawo mata filla-filla, wadanda a yau ta fassarasu da cewa, Allah ne yake nuna mata Ibrahim shine uban ‘ya’yanta ba Khalipha ba.
To ya za ta yi da son Yaya Khaliphan? A wannan sabon matsayin nata na matar kaninsa? Daddy na nufin ta haka rami ta binne soyayyar Khalipha wanda har zuwa yanzu zuciyarta ta ki yarda da cewa ya ki aurenta ne don yaudara, sai ko don wani muhimmin al’amari beyond his ability. Haka nan zuciyarta ta yi masa wannan uzurin duba da tsayin lokacin da Khalipha ya diba cikin soyayyarta tun tana kankanuwa, wannan ba yaudara ba ce.
Laifinsa daya ya ki su magantu balle ta san daga ina matsalar take? Sai dai kaso tamanin cikin dari na zuciyarta ce mata yake “Daga Mami ne”.
To in daga Mami ne ya ya akai ta amince ayi da wanda ta fi so ta fi ciwa buri fiye da Khalipha?
Da ta ga wadannan lissafe-lissafe da saka da warwara da tunane-tunane na neman tarwatsa mata kwakwalwa da wargaza kwanyar kanta, ba kuma zasu samar mata da amsoshin data ke son sani ba, haka bazasu zamo solution ga halin da take ciki a yanzu ba, sai ta tattarasu duka ta mikawa Allah! Wahidun Qahharun!! Mai tsarawa bawa rayuwa ta inda bai zata ba.
Minsharin Inna Juma ya dameta, wadda suke kwance tare a dakin anyi mata shimfida a kan kilishi da filo sai kwasar rabar A.C take tana kwararo minshari mai sauti.
Kallonta Rahane ke yi cikin shudiyar fitilar barci dake kunne tana jin wani sanyi a zuciyarta.
Kafin wata sabuwar fargabar ta zo ta lullube mata zuciya........ yaushe za su hadu da Ibrahim? Yaushe zai zo? Da wace fuska zai karbi al’amarin? Wace irin karba zai yiwa auren nasu? Maganar so ma ta san babu ita in aka yi la’akari da irin yanayin rayuwarshi wadda ta sha bambam da ta Khalipha ta kowanne bangare.
Ita dai kam a yanzu zuciyarta neutral. Wato ba ta bayan kowanne bangare (neither tana son sa nor ba ta son sa). Lamarin zai kasance ne da fuskar da ya zo mata, da ita za ta karbe shi. Babu soyayya cikin zuciyarta kuma babu kiyayya, kai ita duk jinin Dr. Mansur ma abin so ne da girmamawa a gareta.
Ba don komi ba sai don cewa, su suka rufa mata asiri a lokacin da ta bude ido ta tsinci kanta tare dasu, babu kowa nata.
Ba ta taba kullatar Mami ba ko ta sawa ranta Mami ba ta sonta. Rikon shekara goma shag Dan da ba kai ka Haifa ba ba karamin sadaukarwa bane. Ta yarda da abin da Mami ke ikirari na cewa ba kinta take ba, asalinta ne da tsohuwar lalurar ta ya sanya bata isa ta hada zuri’a da ita ba.
Ita ma kuma ta yarda da cewa asalin nata (idan aka hada da nasu) kaskantacce ne. Sannan lalurar ta abin gudu ce ko don tsoron genetic wato gado. Sai dai kuma Mami ta mantacewa ba’a yiwa Allah wayo itama bata gada ba iftila’I ne na Ubangiji. Hakan baya nufin suma ba mutane ne da Ubangiji ya halitta don baya son su ba,kowa da kaddarar rayuwarsa in one way or the other! Dukkanmu masu nakasu ne idan bata nan ba ta can. Maganar asali kuwa Ubangiji guda ne ya halicce mu yana kuma son bayinsa bakidaya.
Ba don baya son su bane ya hana su ilimin, mulkin da arzikin, sai don cewa ko ‘yan yatsu bai yi mana su kai daya ba. There is always hierarchy...... a tsakanin bani-Adam. Abin da ta yarda da shi shine, “Inna akramakum indallahi atqakum”. Wato mafi girmanku a wajen Ubangiji shine wanda yafi tsoron sa.
Don haka zamu iya cewa, a wannan daren baki dayansa, idanuwan Rahane basu runtsa ba. A kan kunnenta aka kira Asubahi, sai ta yi amfani da damar don gusarwa da kanta damuwar da ta gallabeta ta addabeta, ba kuma za ta amfanata da komai ba.
Ta yo alwala ta fito ta tashi Inna Juma. Yayin da ta nabba’a a gaban mahaliccinta don nemawa zuciya, kwakwalwa da rayuwarta sauki a wajen Mai duka. Tana rokon sa ya cire mata firgici da faduwar gaban da take samun kanta a ciki, a duk lokacin da ta tuno ranar da zata yi arba da IBRAHEEM MANSUR TAKAI. Har yanzu tana tantama tana kuma shakkun kasancewar wai Ibraheem ne mijinta ba Khalipha ba.
A hankali ta kai duba ga warawaran hannun ta masu kara tabbatar mata da hakan, ta hanyar fidda dan sauti kas-kas da walainiyar da sukeyi a duk kankanin motsin da ta yi. Abubuwan ban mamakin rayuwa yawa garesu, wasu ma basu zo ba tukunna….. wasu ba’a fara su bama RAYHANAAAAH!!!
****
Washe gari ya kasance litinin, su Daddy tun jiya bayan daurin aure suka wuce Kano aka daura na Khalipha da Radhiyyah. Daddy shi ya biya sadaki da wara-waran zinare kamar yadda ya biya na Rayhanah. A take kuma gidan su amarya suka zarce da biki na tsere ma sa’a.
Ita dai Mami har zuwa lokacin ta gaza nutsuwa da samun kwanciyar hankali, don har zuwa lokacin Daddy bai bude baki ya ce mata komai game da Rayhanah ba, bai tambayeta ina Rayhanah ba, bai gaya mata auren wa aka daura a Takai ba.
Ba ta kara ganin Khalipha ba har zuwa lokacin, ya wuce Abuja ya mai da kansa kamar inji saboda aiki, ya ki yarda zuciyarsa ta kadaice ko kadan balle ta samu filin saka mishi damuwa, tashin hankalin jin cewa shi ba dan Baba Dacta bane ya shafe komi, wato ya fi karfin soyayyar Rayhanah wadda ya kira da sunan bygone issue. Sawun Giwa ya take na Rakumi kuma gaba da gabanta wai aljani ya taka wuta……….
Daddy ya gama masa komai tunda bai bar Rayhanah ta wulakanta ba, wanda shine babbar damuwarsa kuma babban abinda ke kara ingizashi cikin son ya aure ta ya tallafi rayuwarta bayan Kalmar SO, ya zaba mata miji na garari na likawa a goshi in ana likawa, wanda zurfin tunaninsa bai taba bashi kasancewar hakan ba. Damuwarsa daya, wace irin tarba Ibraheem zai yiwa Rahane ‘as a wife??? Yana yi mata fatan alheri.
Shi yanzu haka ma shirin zuwa Jos yake wajen dangin Mami na can don ya fara bincike a kan al’amarin mahaifin nasa, ya dangana da Hurghada. Ya mance da wata aba can wai amarya Radhiyyah.
Lafiya sumul Daddy ya tarbi Dr. Asma’u da fara’a da komai a sanda ya shigo gidan daga ofis ranar da ya dawo daga Takai, ta yi mishi barka da zuwa. Rungumeta ma yayi, ya ce,
“Mami naaa.....”
Ita ma ta ce,
“Dacta naaah....”
Tana loosing tie din wuyan shi.
“Ya aka baro su Hakimi?”
“Kowa lafiya”.
Ya zagayeta da hannayenshi.kanshi cikin wuyanta yana sunsunar ta yake fadin;