Sashe 21
Rayuwar Rayhana Part 2 Complete Hausa Novel · about 11 min read
“Gashin ba saloon..... Mami na tsami ba wanka, kayan jikinta yau kwana uku ba ta canja su ba. Lebenta a bushe kyamas, kamar tayi sati bata sha ruwa ba! Allah ya isa........ tsakanina da duk mai canza min Asma’u na zuwa Ta-ma’ule!”.
Ya dan ture ta ta yi taga-taga ta fada kan gado ya wuce toilet ya hada ruwa mai zafi ya zuba dettol da sabulun ASDA, ya dauko Mami ya wanketa tas, ya wanke gashinta da kumfar shampoo (pert-plus) ya nado ta cikin shawul ya jona dryer yana busar da gashin kanta. Ya dauko doguwar riga ruwan madara mai kyau dinkin Dammam ya sanya mata, ya juyota ya rungumeta.
Runguma mai karfi da tsanani. Kamar zai tsaga kirjinsa ya sanyata. Mami don tausayin Dacta, sai tasa kuka.
Kyaleta ya yi ta yi kukanta mai isarta bai katse ta ba, tana rungume a kirjinsa.
“Ni kaina na rasa me ke damuna Dacta, na zama rikitacciya, abu kadan sai ya ruda ni, ya tsorata ni. Kaina na gaya min abubuwa wadanda na kasa gane musu........”
Hannu ya kai ya toshe mata baki.
“Ba komai bane, sakaci da ibada ne, da rashin tsai da salloli biyar a kan lokaci. Mami ki nutsu ki koma Asma’unki, you are not my precious Asma’u, Dacta guda da warin hammata???”
Ya fada yana dariya yana fesa mata ‘Carolina Herrera’ sai ta rungume shi kam’kam, da haka al’amarin ya sauya. Ko bayan da suka koma cikin nutsuwarsu suka yi wanka suka yi sallah bai gaya mata ya aurawa Ibrahim Rayhanah ba. Sai batun dauko amaryar Khalipha.
Gidan da Daddy ya ginawa Ibrahim da Khalipha na nan a (Farm Center). European Flat zallah, mai dakin barci uku, falo, katon kitchen da bandaki, can ya ce a kai kayan Radhiyyah, har da Mami a ‘yan jere da Dacta Haliman kanta. Naira kam ta sha kuka, aure na GIRMA da KASAITA irin wanda Mami ke so.
Washe gari aka kai amarya dakinta, sai dai babu ango babu alamarshi. Wayoyinsa duk a kulle, basu sani ba shi a lokacin kwanansa biyu a Hurghada tare da Uncle Yohan Yayan Mami suna binciken dangin Mukhlis Imran a birnin Hurghada.
Haka suka hakura suka baro amaryar ita kadai da ‘yan aiki a gidanta ta ci gaba da jiran ango, a karbe shi da soyayya marar misali, da aka tanadar masa.
****
A TAKAI
A Takai, Rayhanah ta wayi gari a gidan Hakimi matsayin daya daga cikin surukan gidan, yadda Haj. Karima da Hakimi ke kula da tarairayarta basa yiwa ‘ya’yan da suka haifa su Nabilah. Ga wani girma na musamman da barorin gidan ke bata.
Su Zinaru sun koma gidajensu. Juma kawai aka bar mata, Hakimi ya ce ta rufo gidanta kwata-kwata ta zauna da jikarta a duk inda Allah ya kaita zaman aure. Tunda bata da miji, ba Da, ba jika. Don dadi Rayhanah kuka ta saki ta rungume Inna Juma tana yiwa Hakimi godiya.
Ya ce, “Babu komai Rayhanah, yadda zamu kula da ‘ya’yan cikinmu, haka muke kula da surukanmu. A kalla kina bukatar budar ido ki ga jininki ko yaushe a kusa dake. Allah ya ji kan Malam Rashidu, na zauna da shi cikin amana don haka Rayhanah ke amanar Allah ce a hannunmu”.
Tunda aka daura auren nan Nabilah ke ta kuka, ta hana uwarta sakat da jama’ar gidan baki daya. Kowa na da masaniyar cewa ta zauna ta kai shekaru talatin a gida ne cikin jiran dawowar Ya Himu, ta kori duk masoyanta amma ba a duba hakan ba, mahaifinta da mahaifiyarta sune ja-gaba wajen aurawa Ibraheem din da ta kallafawa rai wata bare ‘yar talakawa ba ita ba.
Duk mai tausayi dole ya tausayawa Nabilah a bisa yadda ta mai da kanta kamar matar mamaci, balle kuma iyayen da suka haifeta.
Haj. Karima mutum ce mai tsananin kawaici da zuciyar mai da nata ba nata bane, da kuma biyayya ga mijinta. Tabbas tana tausayin Nabilah amma ita a ganinta gara haka, gara da hakan ta faru da Nabilah ta yi auren da ba za a ga kimar ta ba, tunda ita ce mai son, wanda ake son bai san tana yi ba.
Tabbas kulluwar aure a tsakaninsu zai iya kawo babbar baraka cikin zumuncin iyayensu da suka budi ido suka gansu tare ba a taba jin kansu ba (Dr. Mansur da Hakimin Takai Abdulkadir Balarabe Sardauna).
Ta kuma yi la’akari da cewa, Dr. Mansur ya san da zaman Nabilah, amma ya kawo baren ya ce ita ya zabawa dansa. To nacin na mene ne? Dama ita ta maida kanta tsohuwa, amma manema wane iri ne Nabilah bata gani ba? ‘Yan boko, attajirai, masarauta babu irin wadanda basu nemi auren ta ba amma ta ki.
Yanzu da hakan ta faru a ganin Haj. Karima, sai ta nutsu, ta san tudun dafawa (in fa har tana da hankali). Ibrahim ba shine autan maza ba, ta yiwa kanta suttura kamar yadda Hibbah ta yi, gata can da ‘ya’yanta dugwi-dugwi dasu har uku. Soyayya daban, aure daban. Aure ana yin shi ne don Ibada, ba don son zuciya ba, soyayya ba ita ce aure ba.
Sai ayi soyayya kamar a cinye juna shekaru aru-aru, amma idan Allah ya kawo aure, sai a yi shi cikin kwana uku. Masana a ilmin halayyar dan Adam sunyi ‘analysis’ a kan soyayya sun gano cewa, majority (akasari) long-dating (doguwar soyayya) ba a yin nasarar yin aure da ita, iska take bi, kamar ba a yi ta ba.
Sai ayi aure ba a san juna ba kuma a zauna lafiya, a hankali sai so ya shiga. Shi wannan son ba irin na soyayyar iska bane, so ne na halitta wanda gamayyar jiki (physical relationship) ke haifar da shi. Yana da karfin da soyayya bata da shi, yana da tasirin da soyayya bata da shi, yana da tubalin da dan Adam bai iya hako tushensa wanda shine tsakanin Adamu da Hauwa’u, sune kuma suka haifemu, Allah ne ke sanya shi ba long-dating ba.
Don haka ita Haj. Karima addu’a take yiwa autarta Allah ya yi mata zabin miji mafi alheri, wanda zai so ta fiye da yadda take son shi, amma ba bahaguwar soyayyar da take yiwa Ibraheem ba. Gara ka auri wanda ke sonka a kan ka auri wanda kake so!!!
****
[12/24/2019, 21:48] Takori: Mukhlis Abu-Arab, shi ya musuluntar da ita a Jos, ba da sanin yayanta Yohan ba, wanda yake rike da ita a lokacin bayan mutuwar iyayensu. Mukhlis abokin cinikin Yohan ne, yana kawo kaya daga Egypt su Yohan na saye su zuba a shagunansu a babbar kasuwar Jos. Galibi gayan yara ne (Children wears and accessories) a lokacin duniya na kwance, kasuwanci yanada albarka. Sai Allah ya hada Yohan da Mukhlis duk da bambancin addini sakamakon son da yake yiwa tilon kanwarshi.
Shi Yohan bai taba haihuwa ba da matarshi Marye, shi yasa yake son kanwarshi Anita kamar shi ya haifeta, gata da hazaka a makaranta, ita ma Marye tana son Anita saboda yarinya ce kyakkyawa mai shiga rai. Har yau Yohan bai musulunta ba, sai dai ya bar Anita (Asma’u) ta yi addinin da ta zaba shi kam banda shi.
Kuma fa Hausawa ne, Hausa rangadadau a bakinsu kamar jakan Kano, amma basu yarda da addini ba, Neither Islam nor Christianity, Budduism, Hinduism, Jainism, Sikhism Paganism, Rastafari, Taosim ko kowanne ma.
Ta wannan kasuwancin Mukhlis da Yohan suka yi kudi na ban mamaki. Mukhlis ya sayi gida a Jos, kawai don Yohan ya yarda ya aura masa Anita. Suka ci gaba da kasuwancinsu Anita na girma. Mukhlis ya sayi kadarori da yawa a Jos don a nan yake son kafa tubalin iyalinsa.
A lokacin kasar Egypt na fama da matsin durkushewar tattalin arziki kamar Sudan. Larabawan Egypt da yawa sun warwatsu a duniya don neman halalinsu. Garin Hurghada a can matsin yafi yawa. A Larabce ana kiran Hurghada da El-Ghardaqah).
Da yawa sun shigo cikin Cairo suna leburanci masu ilimi sun tsallaka kasashe irin Saudiyyah, Dubai, Bahrain, Kuwait, Taiwan, Dammam Qatar da sauransu. Wasu sunyo Africa irin su Mukhlis kenan.
Duk dimbin iliminsa a kan Geography ya fi ganewa kasuwanci, kuma Allah ya sanya mishi albarka a ciki. Har ya soma tsallakawa kasashen da suka ci gaba yana kawo kayan daga can, musamman Saudiyyah, akwai wani shago a Madina wai shi Majma’al Qimmah da ya shahara wajen kayan yara, Mukhlis na daya daga cikin manyan dilolinsu.
Sanda Anita ta shiga aji shida na sakandire shekarunta goma sha biyar, sai tsahon kafa kawai. A lokacin ne ya nemi Yohan da bukatarsa na neman iri a wajensa.
A lokacin shi Yohan yana shirye-shiryen komawa kasar Ireland shi da Marye, inda harkokinsa suka fi yawa. Shi abin ma dariya ya bashi, wai Mukhlis ya yiwa Anita tsufa duk da bai taba aure ba. Sai dai shi kansa ya san bai isa ya hana Mukhlis Anita ba, ba don su basu da addini ba su, sai don shakuwar da ke tsakaninsu ta tsayin shekaru masu yawa.
Tun Anita na ‘yar shekara biyar Mukhlis yake kula da ita da daukar nauyoyin rayuwarta. Da dora ta a kan hanyar tarbiyya kamar diyar Musulmi. Ya dora Asma’u a kan turbar yin shigar da ba ta fidda tsaraici ba, sun sha yin sallah shi da ita a boye.
Haka ya taka rawa wajen kara mata karfin gwiwa a kan ilimin zamani. Har abada Asma’u ba za ta manta da Mukhlis ba, har abada hoton wannan ranar ba zai taba gushewa daga zuciyarta ba. Wato ranar da Mukhlis ya danka sadakinta a hannun Yayanta Yohan, ‘yan’uwa da abokan arziki suka shaida.
Bai kuma taba ta a ranar ba sai da ya lakana mata LA’ILAHA ILALLAHU, MUHAMMADUR-RASULULLAHI a bisa ra’ayi da yardarta. Don zuwa lokacin Anita ta yarda su dabbobi ne kawai sakamakon cakudo da musulmi a makarantu da take yi da kuma tarayyarta da Mukhlis, tana ganin yadda yake tafiyar da ibadar addininshi yana burgeta, su haka nan suke kara zube, kamar katakwaye da duwatsu. Babu direction.
Mukhlis shi ya sanya mata suna Asma’u, sunan mahaifiyarsa bayan yin shahadarta. Wata da watanni Mukhlis na koyar da Asma’u hukunce-hukuncen addinin gaskiya. A karatun Alkur’ani da yake koya mata sun zo izfi ashirin ya kuma dauketa ya sanya a Islamiyya, kasancewar shi ba mazauni ba.
Sai da ya tabbatar ta ilmantu ta zama cikakkiyar Musulma sannan ya fara mu’amalar aure da ita. Rayuwar auren Asma’u da Mukhlis rayuwa ce mai dadi amma takaitacciya. A lokacin Yohan da Marye suna Ireland sun tafi sun barta da mijinta, wanda ke tattara komai nasa a Nigeria cikin nutsuwa domin ya koma gida tare da matarsa. Allah ya aiko da mummunan hatsarin jirgin ‘Egypt Air’ wanda ya taso daga Cairo zuwa Nigeria har da Mukhlis a ciki.
Asma’u dai sakamakon wannan labari sai nakuda ta tashi, ciki wata takwas sai fedeta aka yi don ta kasa haihuwa. Aka fidda yaro namiji mai kama da ita, amma kalar mahaifinsa.
Bayan takaba da zuwan dangin Mukhlis suka sai da duk wata kadara tasa suka auna suka yi gaba, sun ki sauraren kowa a kan matar da Dan. A lokacin Yohan na Ireland kuma babu hanyoyin sadarwa irin na yanzu.
Asma’u gidan Yohan ta koma ita kadai ta ci gaba da rainon yaronta wanda take yiwa wani irin masifaffen so kamar yadda take son Mukhlis Abu-Arab, tana amfani da ajiyarta ta banki da Mukhlis ke zuba mata duk wata tun aurensu da sunan asusun ajiyar ko-ta-kwana.
Yau da gobe ba ta bar komai ba, kudin banki suka kare. Ko kudin da za a saiwa yaro madara babu, saboda tana da karancin ruwan nono. Haka nan ta yi ta fadi-tashi har da wanke-wanke da shara gidan masu akwai don kawai ta samu abin da za ta sanyawa Abdullahi a baki. Ba ta damu da kanta ba, she only want to save his life..... Asma’u har kosai da fanke ta sayar, a kofar gidansu take soyawa safe da yamma da kuruciyarta da komai, duk saboda Khalipha. Khalipha na da shekara daya Allah ya jefo Yohan gida.
Kuka na duniya Yohan ya yi shi da ganin yadda tilon kanwarsa wanke-hannu ka taba ta koma rufe hannunka sannan ka taba. Amma fa yaronta bul-bul very energetic, diety.
Ita dai ce cikin tsummokara, amma danta tsaf cikin napkin mai tsafta da riga mai kyau har kamshi yake. Rasuwar Mukhlis da abin da danginsa suka yiwa Asma’u da danta ya taba zuciyar Yohan. Abin da ya kai shi ga yin alkawarin har Khalipha ya mutu ba zai kai musu shi ba, zai rike. A satin suka daga Dublin.
Abin da Yohan ya fara yi domin inganta rayuwar Asma’u da danta shine samar mata gurbi a Jami’ar Trinity, ta fara karatun medicine cikin himma. Ba ta yi nisa da karatu ba Khalipha ya soma wani rashin lafiya, sai hankalinta ya rabu biyu, don ma Marye tana taimaka mata da hidimarsa.
Zama a Turai bai sa Asma’u ta canza daga addinin da ta karba da zuciya daya ba, ba ta son barin danta hannun Marye don ta san ba ta da tsarki. Ta fi so ta kula da danta da kanta, ko ina zata tura shi take cikin keken zaman yara, sai dai dole lokutan daukar darasi take barinsa da Marye.
Likitoci sun sha bincike a kan dalilin da ya hana yaro Khalipha barci kullum cikin dare sai kuka, inda suka gano cewa ciwon hanta ne (Hypertitis B). Allah ne ya yi kawai Khalipha rayayye ne ba maganin asibiti da kwakule-kwakulen likitoci ba.
Asma’u ta ji jiki ta sha wahala da danta Khalipha, Yohan da Marye sun taimaka. Ta yi ta yi su Musulunta sun ki. Rashin lafiyar Khalipha ne yasa ta dauki bangaren likitancin yara paedatric don kawai ta kula da lafiyar Khaliphanta.
Ya dan ture ta ta yi taga-taga ta fada kan gado ya wuce toilet ya hada ruwa mai zafi ya zuba dettol da sabulun ASDA, ya dauko Mami ya wanketa tas, ya wanke gashinta da kumfar shampoo (pert-plus) ya nado ta cikin shawul ya jona dryer yana busar da gashin kanta. Ya dauko doguwar riga ruwan madara mai kyau dinkin Dammam ya sanya mata, ya juyota ya rungumeta.
Runguma mai karfi da tsanani. Kamar zai tsaga kirjinsa ya sanyata. Mami don tausayin Dacta, sai tasa kuka.
Kyaleta ya yi ta yi kukanta mai isarta bai katse ta ba, tana rungume a kirjinsa.
“Ni kaina na rasa me ke damuna Dacta, na zama rikitacciya, abu kadan sai ya ruda ni, ya tsorata ni. Kaina na gaya min abubuwa wadanda na kasa gane musu........”
Hannu ya kai ya toshe mata baki.
“Ba komai bane, sakaci da ibada ne, da rashin tsai da salloli biyar a kan lokaci. Mami ki nutsu ki koma Asma’unki, you are not my precious Asma’u, Dacta guda da warin hammata???”
Ya fada yana dariya yana fesa mata ‘Carolina Herrera’ sai ta rungume shi kam’kam, da haka al’amarin ya sauya. Ko bayan da suka koma cikin nutsuwarsu suka yi wanka suka yi sallah bai gaya mata ya aurawa Ibrahim Rayhanah ba. Sai batun dauko amaryar Khalipha.
Gidan da Daddy ya ginawa Ibrahim da Khalipha na nan a (Farm Center). European Flat zallah, mai dakin barci uku, falo, katon kitchen da bandaki, can ya ce a kai kayan Radhiyyah, har da Mami a ‘yan jere da Dacta Haliman kanta. Naira kam ta sha kuka, aure na GIRMA da KASAITA irin wanda Mami ke so.
Washe gari aka kai amarya dakinta, sai dai babu ango babu alamarshi. Wayoyinsa duk a kulle, basu sani ba shi a lokacin kwanansa biyu a Hurghada tare da Uncle Yohan Yayan Mami suna binciken dangin Mukhlis Imran a birnin Hurghada.
Haka suka hakura suka baro amaryar ita kadai da ‘yan aiki a gidanta ta ci gaba da jiran ango, a karbe shi da soyayya marar misali, da aka tanadar masa.
****
A TAKAI
A Takai, Rayhanah ta wayi gari a gidan Hakimi matsayin daya daga cikin surukan gidan, yadda Haj. Karima da Hakimi ke kula da tarairayarta basa yiwa ‘ya’yan da suka haifa su Nabilah. Ga wani girma na musamman da barorin gidan ke bata.
Su Zinaru sun koma gidajensu. Juma kawai aka bar mata, Hakimi ya ce ta rufo gidanta kwata-kwata ta zauna da jikarta a duk inda Allah ya kaita zaman aure. Tunda bata da miji, ba Da, ba jika. Don dadi Rayhanah kuka ta saki ta rungume Inna Juma tana yiwa Hakimi godiya.
Ya ce, “Babu komai Rayhanah, yadda zamu kula da ‘ya’yan cikinmu, haka muke kula da surukanmu. A kalla kina bukatar budar ido ki ga jininki ko yaushe a kusa dake. Allah ya ji kan Malam Rashidu, na zauna da shi cikin amana don haka Rayhanah ke amanar Allah ce a hannunmu”.
Tunda aka daura auren nan Nabilah ke ta kuka, ta hana uwarta sakat da jama’ar gidan baki daya. Kowa na da masaniyar cewa ta zauna ta kai shekaru talatin a gida ne cikin jiran dawowar Ya Himu, ta kori duk masoyanta amma ba a duba hakan ba, mahaifinta da mahaifiyarta sune ja-gaba wajen aurawa Ibraheem din da ta kallafawa rai wata bare ‘yar talakawa ba ita ba.
Duk mai tausayi dole ya tausayawa Nabilah a bisa yadda ta mai da kanta kamar matar mamaci, balle kuma iyayen da suka haifeta.
Haj. Karima mutum ce mai tsananin kawaici da zuciyar mai da nata ba nata bane, da kuma biyayya ga mijinta. Tabbas tana tausayin Nabilah amma ita a ganinta gara haka, gara da hakan ta faru da Nabilah ta yi auren da ba za a ga kimar ta ba, tunda ita ce mai son, wanda ake son bai san tana yi ba.
Tabbas kulluwar aure a tsakaninsu zai iya kawo babbar baraka cikin zumuncin iyayensu da suka budi ido suka gansu tare ba a taba jin kansu ba (Dr. Mansur da Hakimin Takai Abdulkadir Balarabe Sardauna).
Ta kuma yi la’akari da cewa, Dr. Mansur ya san da zaman Nabilah, amma ya kawo baren ya ce ita ya zabawa dansa. To nacin na mene ne? Dama ita ta maida kanta tsohuwa, amma manema wane iri ne Nabilah bata gani ba? ‘Yan boko, attajirai, masarauta babu irin wadanda basu nemi auren ta ba amma ta ki.
Yanzu da hakan ta faru a ganin Haj. Karima, sai ta nutsu, ta san tudun dafawa (in fa har tana da hankali). Ibrahim ba shine autan maza ba, ta yiwa kanta suttura kamar yadda Hibbah ta yi, gata can da ‘ya’yanta dugwi-dugwi dasu har uku. Soyayya daban, aure daban. Aure ana yin shi ne don Ibada, ba don son zuciya ba, soyayya ba ita ce aure ba.
Sai ayi soyayya kamar a cinye juna shekaru aru-aru, amma idan Allah ya kawo aure, sai a yi shi cikin kwana uku. Masana a ilmin halayyar dan Adam sunyi ‘analysis’ a kan soyayya sun gano cewa, majority (akasari) long-dating (doguwar soyayya) ba a yin nasarar yin aure da ita, iska take bi, kamar ba a yi ta ba.
Sai ayi aure ba a san juna ba kuma a zauna lafiya, a hankali sai so ya shiga. Shi wannan son ba irin na soyayyar iska bane, so ne na halitta wanda gamayyar jiki (physical relationship) ke haifar da shi. Yana da karfin da soyayya bata da shi, yana da tasirin da soyayya bata da shi, yana da tubalin da dan Adam bai iya hako tushensa wanda shine tsakanin Adamu da Hauwa’u, sune kuma suka haifemu, Allah ne ke sanya shi ba long-dating ba.
Don haka ita Haj. Karima addu’a take yiwa autarta Allah ya yi mata zabin miji mafi alheri, wanda zai so ta fiye da yadda take son shi, amma ba bahaguwar soyayyar da take yiwa Ibraheem ba. Gara ka auri wanda ke sonka a kan ka auri wanda kake so!!!
****
[12/24/2019, 21:48] Takori: Mukhlis Abu-Arab, shi ya musuluntar da ita a Jos, ba da sanin yayanta Yohan ba, wanda yake rike da ita a lokacin bayan mutuwar iyayensu. Mukhlis abokin cinikin Yohan ne, yana kawo kaya daga Egypt su Yohan na saye su zuba a shagunansu a babbar kasuwar Jos. Galibi gayan yara ne (Children wears and accessories) a lokacin duniya na kwance, kasuwanci yanada albarka. Sai Allah ya hada Yohan da Mukhlis duk da bambancin addini sakamakon son da yake yiwa tilon kanwarshi.
Shi Yohan bai taba haihuwa ba da matarshi Marye, shi yasa yake son kanwarshi Anita kamar shi ya haifeta, gata da hazaka a makaranta, ita ma Marye tana son Anita saboda yarinya ce kyakkyawa mai shiga rai. Har yau Yohan bai musulunta ba, sai dai ya bar Anita (Asma’u) ta yi addinin da ta zaba shi kam banda shi.
Kuma fa Hausawa ne, Hausa rangadadau a bakinsu kamar jakan Kano, amma basu yarda da addini ba, Neither Islam nor Christianity, Budduism, Hinduism, Jainism, Sikhism Paganism, Rastafari, Taosim ko kowanne ma.
Ta wannan kasuwancin Mukhlis da Yohan suka yi kudi na ban mamaki. Mukhlis ya sayi gida a Jos, kawai don Yohan ya yarda ya aura masa Anita. Suka ci gaba da kasuwancinsu Anita na girma. Mukhlis ya sayi kadarori da yawa a Jos don a nan yake son kafa tubalin iyalinsa.
A lokacin kasar Egypt na fama da matsin durkushewar tattalin arziki kamar Sudan. Larabawan Egypt da yawa sun warwatsu a duniya don neman halalinsu. Garin Hurghada a can matsin yafi yawa. A Larabce ana kiran Hurghada da El-Ghardaqah).
Da yawa sun shigo cikin Cairo suna leburanci masu ilimi sun tsallaka kasashe irin Saudiyyah, Dubai, Bahrain, Kuwait, Taiwan, Dammam Qatar da sauransu. Wasu sunyo Africa irin su Mukhlis kenan.
Duk dimbin iliminsa a kan Geography ya fi ganewa kasuwanci, kuma Allah ya sanya mishi albarka a ciki. Har ya soma tsallakawa kasashen da suka ci gaba yana kawo kayan daga can, musamman Saudiyyah, akwai wani shago a Madina wai shi Majma’al Qimmah da ya shahara wajen kayan yara, Mukhlis na daya daga cikin manyan dilolinsu.
Sanda Anita ta shiga aji shida na sakandire shekarunta goma sha biyar, sai tsahon kafa kawai. A lokacin ne ya nemi Yohan da bukatarsa na neman iri a wajensa.
A lokacin shi Yohan yana shirye-shiryen komawa kasar Ireland shi da Marye, inda harkokinsa suka fi yawa. Shi abin ma dariya ya bashi, wai Mukhlis ya yiwa Anita tsufa duk da bai taba aure ba. Sai dai shi kansa ya san bai isa ya hana Mukhlis Anita ba, ba don su basu da addini ba su, sai don shakuwar da ke tsakaninsu ta tsayin shekaru masu yawa.
Tun Anita na ‘yar shekara biyar Mukhlis yake kula da ita da daukar nauyoyin rayuwarta. Da dora ta a kan hanyar tarbiyya kamar diyar Musulmi. Ya dora Asma’u a kan turbar yin shigar da ba ta fidda tsaraici ba, sun sha yin sallah shi da ita a boye.
Haka ya taka rawa wajen kara mata karfin gwiwa a kan ilimin zamani. Har abada Asma’u ba za ta manta da Mukhlis ba, har abada hoton wannan ranar ba zai taba gushewa daga zuciyarta ba. Wato ranar da Mukhlis ya danka sadakinta a hannun Yayanta Yohan, ‘yan’uwa da abokan arziki suka shaida.
Bai kuma taba ta a ranar ba sai da ya lakana mata LA’ILAHA ILALLAHU, MUHAMMADUR-RASULULLAHI a bisa ra’ayi da yardarta. Don zuwa lokacin Anita ta yarda su dabbobi ne kawai sakamakon cakudo da musulmi a makarantu da take yi da kuma tarayyarta da Mukhlis, tana ganin yadda yake tafiyar da ibadar addininshi yana burgeta, su haka nan suke kara zube, kamar katakwaye da duwatsu. Babu direction.
Mukhlis shi ya sanya mata suna Asma’u, sunan mahaifiyarsa bayan yin shahadarta. Wata da watanni Mukhlis na koyar da Asma’u hukunce-hukuncen addinin gaskiya. A karatun Alkur’ani da yake koya mata sun zo izfi ashirin ya kuma dauketa ya sanya a Islamiyya, kasancewar shi ba mazauni ba.
Sai da ya tabbatar ta ilmantu ta zama cikakkiyar Musulma sannan ya fara mu’amalar aure da ita. Rayuwar auren Asma’u da Mukhlis rayuwa ce mai dadi amma takaitacciya. A lokacin Yohan da Marye suna Ireland sun tafi sun barta da mijinta, wanda ke tattara komai nasa a Nigeria cikin nutsuwa domin ya koma gida tare da matarsa. Allah ya aiko da mummunan hatsarin jirgin ‘Egypt Air’ wanda ya taso daga Cairo zuwa Nigeria har da Mukhlis a ciki.
Asma’u dai sakamakon wannan labari sai nakuda ta tashi, ciki wata takwas sai fedeta aka yi don ta kasa haihuwa. Aka fidda yaro namiji mai kama da ita, amma kalar mahaifinsa.
Bayan takaba da zuwan dangin Mukhlis suka sai da duk wata kadara tasa suka auna suka yi gaba, sun ki sauraren kowa a kan matar da Dan. A lokacin Yohan na Ireland kuma babu hanyoyin sadarwa irin na yanzu.
Asma’u gidan Yohan ta koma ita kadai ta ci gaba da rainon yaronta wanda take yiwa wani irin masifaffen so kamar yadda take son Mukhlis Abu-Arab, tana amfani da ajiyarta ta banki da Mukhlis ke zuba mata duk wata tun aurensu da sunan asusun ajiyar ko-ta-kwana.
Yau da gobe ba ta bar komai ba, kudin banki suka kare. Ko kudin da za a saiwa yaro madara babu, saboda tana da karancin ruwan nono. Haka nan ta yi ta fadi-tashi har da wanke-wanke da shara gidan masu akwai don kawai ta samu abin da za ta sanyawa Abdullahi a baki. Ba ta damu da kanta ba, she only want to save his life..... Asma’u har kosai da fanke ta sayar, a kofar gidansu take soyawa safe da yamma da kuruciyarta da komai, duk saboda Khalipha. Khalipha na da shekara daya Allah ya jefo Yohan gida.
Kuka na duniya Yohan ya yi shi da ganin yadda tilon kanwarsa wanke-hannu ka taba ta koma rufe hannunka sannan ka taba. Amma fa yaronta bul-bul very energetic, diety.
Ita dai ce cikin tsummokara, amma danta tsaf cikin napkin mai tsafta da riga mai kyau har kamshi yake. Rasuwar Mukhlis da abin da danginsa suka yiwa Asma’u da danta ya taba zuciyar Yohan. Abin da ya kai shi ga yin alkawarin har Khalipha ya mutu ba zai kai musu shi ba, zai rike. A satin suka daga Dublin.
Abin da Yohan ya fara yi domin inganta rayuwar Asma’u da danta shine samar mata gurbi a Jami’ar Trinity, ta fara karatun medicine cikin himma. Ba ta yi nisa da karatu ba Khalipha ya soma wani rashin lafiya, sai hankalinta ya rabu biyu, don ma Marye tana taimaka mata da hidimarsa.
Zama a Turai bai sa Asma’u ta canza daga addinin da ta karba da zuciya daya ba, ba ta son barin danta hannun Marye don ta san ba ta da tsarki. Ta fi so ta kula da danta da kanta, ko ina zata tura shi take cikin keken zaman yara, sai dai dole lokutan daukar darasi take barinsa da Marye.
Likitoci sun sha bincike a kan dalilin da ya hana yaro Khalipha barci kullum cikin dare sai kuka, inda suka gano cewa ciwon hanta ne (Hypertitis B). Allah ne ya yi kawai Khalipha rayayye ne ba maganin asibiti da kwakule-kwakulen likitoci ba.
Asma’u ta ji jiki ta sha wahala da danta Khalipha, Yohan da Marye sun taimaka. Ta yi ta yi su Musulunta sun ki. Rashin lafiyar Khalipha ne yasa ta dauki bangaren likitancin yara paedatric don kawai ta kula da lafiyar Khaliphanta.