Sashe 7
Rayuwar Rayhana Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
“Mami! Mami!!”
Daddy ke kira a falon sama.
Ta fito daga laundary inda take shanyar kayan Azizah data wanke cikin injin wanki, sanye take da riga da siket na wani bakin material mai yarfin light green flowers, gashin kanta kame da hair-bound, shima light green ya sauko har kafadunta. Duk wani likita kirki ne da shi, to haka Dr. Asma’u Takai, musamman kasancewarta likitar yara.
Amma a yau kam ga dukkan alamu za suyi fada da Dactan nata, don kirkin nata bai kai nan ba.
Za ka rantse ba ta haifi Da kamar I.M ba, balle kuma Yayansa Khalipha. Ta fi kama da matashiya ‘yar shekaru talatin ba talatin da tara ba.
Ta fito falon tana fadin “Dacta na!” Shima ya ce, “Mamina!!”.
Ya juya ga Rahane, “Rayhanah matsa ki gai da Mamanku”.
Sai a lokacin ta kai idonta ga Rahanen da ta zube a gabanta tana fadin “Barka da yamma Hajiya”. A firgice ta juya ga Ibraheem, sannan Daddyn ta kasa tambayar komai.
Dariya ce ta kama Ibraheem ganin idanun Mami sunyi mitsi-mitsi, ya lallaba ya shige dakinsa kada dariyar da yake yi ta fito.
Daddy ya yi murmushi ya isa ga Rahane yasa hannu ya cira ta daga zubewar da ta yi kamar bawa a gaban Ubangijinsa. Ya zaunar da ita a kujera yana ce da Mami
“Karin ‘ya na kawo miki, sauran bayani sai anjima, yanzu ba ta abinci da ruwa tukunna mun sha tafiya”.
Ta dan saki fuska ta koma kicin ta zubo abinci a plate da robar ruwan Eva mai sanyi da lemun La-casera ta kawo mata kan tebir. Amma da ta kira yarinyar ta ce ta zauna a kujera ta ci, sai ta ga ta sauke plate din kan marbles ta bararraje abinta tana ci kamar Allah ya aikota saboda yunwa.
Ta bi bayan mijinta cike da mamaki. Ta same shi yana cire safar kafarshi a gefen gado, ta zauna a kasan kafafun nashi ta karbe shi. Sai da ya yi wanka ya kwanta yana hutawa, Mami ta matsa jikinsa tana cewa,
“Ina ka samo yarinya bakauya haka?”
Ya ce, “Garinmu Takai”. Ta ce, “Yar waye?”
Ya ce, “Yar AMANA!”
Ya tashi daga kishingidar da ya yi ya kama hannayenta masu taushi ya ce, “Mami batun yau ba ni da ke muke da bambancin ra’ayi a kan al’amura da dama, amma kowa ya kasa rinjayar dan’uwanshi ya bi nashi ra’ayin.
Amma a yau ina neman alfarma Mami, wadda na san mai girma ce a gare ki, ita ce ki rike min Rayhanah kwatankwacin rikon da kike yiwa ‘ya’yan da kika haifa.
Ko da komai bai zamo hundred parcently equal ba, ki kwatanta kara da karamci. Rayhanah da ubanta ba shegiya ba ce. Sai dai marainiya ce ba ta da uwa, ta rasu tun lokacin haihuwarta. Ta girma a hannun kakarta, ita ma yanzu babu.
Na tserar da ita ne daga kaskantacciyar rayuwa da ubanta ke so ta yi, wato early and abusing marriage, sakamakon wasu extraordinary characteristics dana gani a tare da ita.
Ban taba haduwa da pateint din da ya shiga raina irin ta ba. Sannan ta gamu da ‘lalura’ wadda dole a tausaya mata, a bata kwarin gwiwar da zata fuskanci rayuwa a, duk yadda ta zo mata.
Ta samu hearing impairment wanda bazamu ce a sakamakon hadarin da suka yi bane, har yanzu source din, bai bayyana garemu ba, har sai anyi CT Scan and MRI Scan, wadanda bamu da injinan yin su anan Nigeria, in kin lura akwai hearing-aid a kunnenta. Mami ban taba neman alfarma kin kasa yi min ba, a yau wadda nake nema ma ba za ta gagareki ba, tunda kin saba haihuwa kin san ciwon DA. Yadda naki yake a ranki haka na kowa yake a zuciyar nashi iyayen.
Ki yi min alfarma cikin dimbin alfarmominki gareni, ki rike min RAYHANAH da zuciya daya, ni kuma duk abin da kike so zan miki Mami. Wallahi-wallahi ko da bani da shi zan nemo. Kawai ina so Rayhanah ta yi rayuwa mai kyau kamar ‘ya’yanki. Ta yi ilimi, ba tare da nakasunta ya nakasta rayuwarta ba. Zan samu Mami?”
Ta sauke idonta a hankali kan mijin nata, ta rasa shi wane irin mutum ne, mai maida damuwar wani tasa. Ba ta da muguwar zuciya ko kankani, sai dai ba ta son kowa ya rabi rayuwarta da mijinta da ‘ya’yanta.
Ba ma wannan ne abin tsoron ba, za ta hada ‘ya’yanta ne da yarinyar da ko asalinta ba ta sani ba? Kai rigimar Daddy da yawa take.
Ta ce, “Daddy zan yi maka alfarmar da kake so, amma a bisa sharadi biyu”.
Kallonta ya yi, kallon ke nake sauraro. Ta ce, “Ka yi min alkawarin WATARANA ba zaka ce za ka hada aure tsakanin ‘ya’yana da wannan yarinyar ba. Sharadi na biyu shine, zan raba musu daki da su Abida, don hankalina ba zai kwanta ba idan tana tare dasu”.
Dariya ta bai wa Daddy sosai. Ya ce, “Mamee!”
Ta ce, “Dacta naa!!”
“ki kwantar da hankalinki da Rayhanah, ba zan kawo abin da zai cuci su Abida ba. Am their Dad, remember? Baki fini son su ba!!!.
Maganar aure da ‘ya’yanki kuwa kisa ranki a inuwa sassanya, Allah zai baiwa Rayhanah miji na ban mamaki wanda zai kaunaceta domin Allah ya rungumeta da lalurar ta, ba ‘ya’yanki ba, masu hali da akida irin taki, ‘ya’yanki ba sune kadai MAZA a duniya ba! MAZA ma tukunna, baki gansu ba Mami.
In kin so ki aura musu ‘ya’yan Queen Elizabeth, karshenta dai kenan ko? Ki rubuta ki ajiye, babu aure tsakanin ‘ya’yanki da Rayhanah! Tunda ita baki dauketa cikakkiyar mutum ba”.
“Ba haka nake nufi ba Dacta na?”
“To ya ya ne?”
“(A bit.......depressed). Ta ce, “Ni dai in hakan za a yi bani da matsala da yarinyar”.
Dacta ya ce, “Mami, hoo!”
Rahane tuni barci ya kwasheta a kan marbles din dining, inda ta ci abinci. A haka su Abida suka shigo suka sameta, Abida, Jawahir da Azizah suka sunkuya suna kallonta.
Abida ta leka tafin kafarta ta ga faso da kaushi! Ta ce, “Ehoo! Yau faso zai yaga bedsheet din Jawahid, don kuwa ba dai gadona ba”.
Aziza kuwa dukanta take tana cewa, “Tashi-tashi, cinnaka zai cijeki, ki hau gado”.
Jawahir kuwa hannunta ta kama tana cewa, “Tashi muje daki za ki dauki sanyi a nan”.
Ta bude idonta a hankali tana kallon su. Ba ta taba ganin kyawawan mutane irin wadannan yaran ba.
Dacta ne da Mami suka fito tare jin hayaniyarsu, suka gansu zagaye da ita kamar sun ga wata sabuwar halitta. Mami ta ce, “Mene ne haka? Ku kaita daki mana ta yi wanka sai ta kwanta ta yi barcin”.
Abida ta ce, “Ar! Mami kafarta faso! She is smelling bad!! Da soson wa za ta yi wanka?”
Dacta ya dunkule hannu ya danna mata, “Da na Uwaki. Ja’ira mara hankali”.
Ya matsa gabansu ya ce, “Kamata Jawahir kuje daki ki taimaka mata ta yi wanka, kin gani ba ta da lafiya”.
Jawahir ta bi umarnin mahaifinta. Suka shiga daki da Rahane. Ta cika mata ruwan dumi a kwami, ta zuba dettol, ta bare sabon sabulun zest da sabon soso ta bata.
Ta ce, “Ki yi wankan sosai kin ji, amma ki yi a hankali kada ki fama ciwukan ki”.
Ta nuna mata hanger, “Ga towell nan, ki dauki wanda kike so. Wannan kwandon ki zuba kayan da kika cire kayan wanki ne a ciki”.
Rahane ta ce, “Ai ban zo da wasu kayan da zan canza ba in na ajiye wadannan”.
Ta ce, “Zan baki nawa in ji Daddy”. Ta juya ta fita tana cewa, “Ki yi wanka sosai”.
Daddy ke kira a falon sama.
Ta fito daga laundary inda take shanyar kayan Azizah data wanke cikin injin wanki, sanye take da riga da siket na wani bakin material mai yarfin light green flowers, gashin kanta kame da hair-bound, shima light green ya sauko har kafadunta. Duk wani likita kirki ne da shi, to haka Dr. Asma’u Takai, musamman kasancewarta likitar yara.
Amma a yau kam ga dukkan alamu za suyi fada da Dactan nata, don kirkin nata bai kai nan ba.
Za ka rantse ba ta haifi Da kamar I.M ba, balle kuma Yayansa Khalipha. Ta fi kama da matashiya ‘yar shekaru talatin ba talatin da tara ba.
Ta fito falon tana fadin “Dacta na!” Shima ya ce, “Mamina!!”.
Ya juya ga Rahane, “Rayhanah matsa ki gai da Mamanku”.
Sai a lokacin ta kai idonta ga Rahanen da ta zube a gabanta tana fadin “Barka da yamma Hajiya”. A firgice ta juya ga Ibraheem, sannan Daddyn ta kasa tambayar komai.
Dariya ce ta kama Ibraheem ganin idanun Mami sunyi mitsi-mitsi, ya lallaba ya shige dakinsa kada dariyar da yake yi ta fito.
Daddy ya yi murmushi ya isa ga Rahane yasa hannu ya cira ta daga zubewar da ta yi kamar bawa a gaban Ubangijinsa. Ya zaunar da ita a kujera yana ce da Mami
“Karin ‘ya na kawo miki, sauran bayani sai anjima, yanzu ba ta abinci da ruwa tukunna mun sha tafiya”.
Ta dan saki fuska ta koma kicin ta zubo abinci a plate da robar ruwan Eva mai sanyi da lemun La-casera ta kawo mata kan tebir. Amma da ta kira yarinyar ta ce ta zauna a kujera ta ci, sai ta ga ta sauke plate din kan marbles ta bararraje abinta tana ci kamar Allah ya aikota saboda yunwa.
Ta bi bayan mijinta cike da mamaki. Ta same shi yana cire safar kafarshi a gefen gado, ta zauna a kasan kafafun nashi ta karbe shi. Sai da ya yi wanka ya kwanta yana hutawa, Mami ta matsa jikinsa tana cewa,
“Ina ka samo yarinya bakauya haka?”
Ya ce, “Garinmu Takai”. Ta ce, “Yar waye?”
Ya ce, “Yar AMANA!”
Ya tashi daga kishingidar da ya yi ya kama hannayenta masu taushi ya ce, “Mami batun yau ba ni da ke muke da bambancin ra’ayi a kan al’amura da dama, amma kowa ya kasa rinjayar dan’uwanshi ya bi nashi ra’ayin.
Amma a yau ina neman alfarma Mami, wadda na san mai girma ce a gare ki, ita ce ki rike min Rayhanah kwatankwacin rikon da kike yiwa ‘ya’yan da kika haifa.
Ko da komai bai zamo hundred parcently equal ba, ki kwatanta kara da karamci. Rayhanah da ubanta ba shegiya ba ce. Sai dai marainiya ce ba ta da uwa, ta rasu tun lokacin haihuwarta. Ta girma a hannun kakarta, ita ma yanzu babu.
Na tserar da ita ne daga kaskantacciyar rayuwa da ubanta ke so ta yi, wato early and abusing marriage, sakamakon wasu extraordinary characteristics dana gani a tare da ita.
Ban taba haduwa da pateint din da ya shiga raina irin ta ba. Sannan ta gamu da ‘lalura’ wadda dole a tausaya mata, a bata kwarin gwiwar da zata fuskanci rayuwa a, duk yadda ta zo mata.
Ta samu hearing impairment wanda bazamu ce a sakamakon hadarin da suka yi bane, har yanzu source din, bai bayyana garemu ba, har sai anyi CT Scan and MRI Scan, wadanda bamu da injinan yin su anan Nigeria, in kin lura akwai hearing-aid a kunnenta. Mami ban taba neman alfarma kin kasa yi min ba, a yau wadda nake nema ma ba za ta gagareki ba, tunda kin saba haihuwa kin san ciwon DA. Yadda naki yake a ranki haka na kowa yake a zuciyar nashi iyayen.
Ki yi min alfarma cikin dimbin alfarmominki gareni, ki rike min RAYHANAH da zuciya daya, ni kuma duk abin da kike so zan miki Mami. Wallahi-wallahi ko da bani da shi zan nemo. Kawai ina so Rayhanah ta yi rayuwa mai kyau kamar ‘ya’yanki. Ta yi ilimi, ba tare da nakasunta ya nakasta rayuwarta ba. Zan samu Mami?”
Ta sauke idonta a hankali kan mijin nata, ta rasa shi wane irin mutum ne, mai maida damuwar wani tasa. Ba ta da muguwar zuciya ko kankani, sai dai ba ta son kowa ya rabi rayuwarta da mijinta da ‘ya’yanta.
Ba ma wannan ne abin tsoron ba, za ta hada ‘ya’yanta ne da yarinyar da ko asalinta ba ta sani ba? Kai rigimar Daddy da yawa take.
Ta ce, “Daddy zan yi maka alfarmar da kake so, amma a bisa sharadi biyu”.
Kallonta ya yi, kallon ke nake sauraro. Ta ce, “Ka yi min alkawarin WATARANA ba zaka ce za ka hada aure tsakanin ‘ya’yana da wannan yarinyar ba. Sharadi na biyu shine, zan raba musu daki da su Abida, don hankalina ba zai kwanta ba idan tana tare dasu”.
Dariya ta bai wa Daddy sosai. Ya ce, “Mamee!”
Ta ce, “Dacta naa!!”
“ki kwantar da hankalinki da Rayhanah, ba zan kawo abin da zai cuci su Abida ba. Am their Dad, remember? Baki fini son su ba!!!.
Maganar aure da ‘ya’yanki kuwa kisa ranki a inuwa sassanya, Allah zai baiwa Rayhanah miji na ban mamaki wanda zai kaunaceta domin Allah ya rungumeta da lalurar ta, ba ‘ya’yanki ba, masu hali da akida irin taki, ‘ya’yanki ba sune kadai MAZA a duniya ba! MAZA ma tukunna, baki gansu ba Mami.
In kin so ki aura musu ‘ya’yan Queen Elizabeth, karshenta dai kenan ko? Ki rubuta ki ajiye, babu aure tsakanin ‘ya’yanki da Rayhanah! Tunda ita baki dauketa cikakkiyar mutum ba”.
“Ba haka nake nufi ba Dacta na?”
“To ya ya ne?”
“(A bit.......depressed). Ta ce, “Ni dai in hakan za a yi bani da matsala da yarinyar”.
Dacta ya ce, “Mami, hoo!”
Rahane tuni barci ya kwasheta a kan marbles din dining, inda ta ci abinci. A haka su Abida suka shigo suka sameta, Abida, Jawahir da Azizah suka sunkuya suna kallonta.
Abida ta leka tafin kafarta ta ga faso da kaushi! Ta ce, “Ehoo! Yau faso zai yaga bedsheet din Jawahid, don kuwa ba dai gadona ba”.
Aziza kuwa dukanta take tana cewa, “Tashi-tashi, cinnaka zai cijeki, ki hau gado”.
Jawahir kuwa hannunta ta kama tana cewa, “Tashi muje daki za ki dauki sanyi a nan”.
Ta bude idonta a hankali tana kallon su. Ba ta taba ganin kyawawan mutane irin wadannan yaran ba.
Dacta ne da Mami suka fito tare jin hayaniyarsu, suka gansu zagaye da ita kamar sun ga wata sabuwar halitta. Mami ta ce, “Mene ne haka? Ku kaita daki mana ta yi wanka sai ta kwanta ta yi barcin”.
Abida ta ce, “Ar! Mami kafarta faso! She is smelling bad!! Da soson wa za ta yi wanka?”
Dacta ya dunkule hannu ya danna mata, “Da na Uwaki. Ja’ira mara hankali”.
Ya matsa gabansu ya ce, “Kamata Jawahir kuje daki ki taimaka mata ta yi wanka, kin gani ba ta da lafiya”.
Jawahir ta bi umarnin mahaifinta. Suka shiga daki da Rahane. Ta cika mata ruwan dumi a kwami, ta zuba dettol, ta bare sabon sabulun zest da sabon soso ta bata.
Ta ce, “Ki yi wankan sosai kin ji, amma ki yi a hankali kada ki fama ciwukan ki”.
Ta nuna mata hanger, “Ga towell nan, ki dauki wanda kike so. Wannan kwandon ki zuba kayan da kika cire kayan wanki ne a ciki”.
Rahane ta ce, “Ai ban zo da wasu kayan da zan canza ba in na ajiye wadannan”.
Ta ce, “Zan baki nawa in ji Daddy”. Ta juya ta fita tana cewa, “Ki yi wanka sosai”.