Sashe 15
Rayuwar Rayhana Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Ibraheem Mansur, (HEEMU ko I.M) kamar yadda kannensa da abokansa ke kiransa. Bai da shiga sharo ba shanu balle abin da bai shafe shi ba.
Amma a yau, haka nan ya samu kansa da son sanin asali da tushen su Rayhanah, da rayuwarsu ta baya. Abinki da karamin gari, kowa ya san kowa.
Don haka bai sha wuyar samun tarihin su Rayhanah ba. An gaya mishi uwarta ta rasu tun lokacin haihuwarta, kakarta da suka yi hatsari tare ita ta raine ta.
Har makarantar su Rahane ya je ya binciko takardunta. Malamansu sun shaideta wajen kokari da son karatu. Sai ya ji hankalinsa ya kwanta da rayuwarta tare dasu.
Sai dai ko a fuska bai nunawa Baba Dacta komi ba. Malam Rashidu ya samu kyakkyawar shaida daga bakin makwabtansa. Amma a da sam hankalinsa bai kwanta da zaman yarinyar tare dasu ba, saboda halin rayuwa da butulci irin na dan Adam.
Sai kuma yake tambayar kansa, shin me yasa ya damu kansa kan yarinyar? Damuwa irin wadda bai taba yi a kan kowa ba??? Ya tattara zancen ya watsar ya shiga sabgoginsa.
Da yammacin ranar yana barga tare da kaninsa Sha’aban dan Hakimi, kowannensu ingarman doki ya zaba Sarkin Dawaki ya aza musu sirdi suka dane suka nufi ‘yar shakatawa bayan gari.
Suna tafe hira suke yi kan sabbin gine-ginen zamani da Hakimi ke yi a cikin garin da ginin gidan saukar baki mai dauke da bukkokin zamani, inda Turawa ke sauka idan sun kawo ziyara. Haka nan Hakimi na sauke bakin alfarma idan sun zo.
Ibraheem ya yi sha’awar wadannan gine-ginen sosai. Yake ce da Sha’aban duk lokacin da ya tashi ginin gida zai sanya ‘Hut’ wato bukka ta gargajiya mai suffar zamani.
Sanda suka dawo magariba ta gabato, suka sauka daga dawakan suka soma alwala a famfon wajen. Kamar an ce da Ibrahim ‘juya’, ya hango Rahane na yankewa Babanta akaifa da nail cut. Sai dai bai jin me suke cewa a tsakaninsu.
To haka washe gari da misalin karfe goma na safe ya shigo bargar domin an kawo sababbin (Polo Horses) daga Ireland duka na Baba Dacta ne, yake ba da hayarsu ga masu sana’ar tseren Dawaki ake masa kiwon su anan bargar hakimi. Sun bambanta sosai da sauran dawakan ko daga koshinsu da shekin da suke yi da kuzari.
Ya dan juya ido sai ya hango Rahane da jibgin kayan wankin Babanta da ta tattaro tana ta dirzarsu kamar Allah ya aikota. Shi kuma Baban yana gefe yana yiwa dawakin askin jelarsu da katon almakashi. Yana cewa,
“Wato Rahane ba kya jin magana ko? Na ce ki bar wankin nan ya fi karfinki in na gama zan yi abina”.
Ta ce, “Albarka nake nema Baba, ka barni in samu, in ban yi maka ba wa zan yiwa? Idan mun tafi ban san yaushe zamu kara dawowa ba”.
Ibraheem ya jinjina kai suka kara ba shi tausayi.
Washegari suka yi sallama da kowa za su tafi, Rahane har kuka ta yi saboda ba ta son barin Babanta. Amma ba ta bari Baba Dacta ya gani ba, sauri ta yi ta dauke hawayen da yatsunta.
Da gudu ta koma ta sake rungume Babanta, sannan ta shiga mota tana share hawaye da sauri.
Har Ibraheem ya kunna mota ya hango Mal. Rashidu tafe da sassarfarsa rike da katuwar leda, don haka ya dakata.
Baba Dacta ya sauke gilashi sai ya mika masa, “Yalo ne da kashu (cashew) babu yawa a yiwa yara tsaraba”.
Hannu biyu Baba Dacta yasa ya karba, ya ce, “Yara sun gode Baban Rayhanah. Allah ya kara nisan kwana”.
Ya sanya hannu cikin aljihu ya zaro naira dari biyu ya mikawa Aziza, “Ungo yarinya ka sha ruwa a hanya kin ji?”
Mami ce ta karba fuskarta fal fara’a ta ce, “Aziza ta gode Baba”.
Ya daga musu hannu suka ja motar suka tafi. Abida ta juyar da kai gefen taga tana tsaki mara sauti. Kamar ta rufe Mamin da duka da ta karba.
Su kuwa iyayen sun ji dadi har ransu. ALHERI komi kankantarsa dadi gare shi, amma ga wanda ya san mutuncin dan Adam.
Kafin la’asar sun iso Kano. A harabar gidan bakuwar mota ce kankanuwa mai santsi (one door, Camero) fake a harabar adana motoci.
Ai kuwa daga Jawahir, Abida har Azizah fita suka yi a guje har Azizah na faduwa, ta kuwa fashe da kuka, don har bakinta ya fashe.
Da sauri Rahane ta fito ta dauke ta tana goge mata jinin dake fita daga bakinta. Mami na ta fada za su kashe mata ‘ya sai ka ce yau suka fara ganin Khalifan. Amma ko jin ta basu yi ba balle su tsaya. Sai da suka dangane ga dan’uwansu suka rungume shi.
Amma a yau, haka nan ya samu kansa da son sanin asali da tushen su Rayhanah, da rayuwarsu ta baya. Abinki da karamin gari, kowa ya san kowa.
Don haka bai sha wuyar samun tarihin su Rayhanah ba. An gaya mishi uwarta ta rasu tun lokacin haihuwarta, kakarta da suka yi hatsari tare ita ta raine ta.
Har makarantar su Rahane ya je ya binciko takardunta. Malamansu sun shaideta wajen kokari da son karatu. Sai ya ji hankalinsa ya kwanta da rayuwarta tare dasu.
Sai dai ko a fuska bai nunawa Baba Dacta komi ba. Malam Rashidu ya samu kyakkyawar shaida daga bakin makwabtansa. Amma a da sam hankalinsa bai kwanta da zaman yarinyar tare dasu ba, saboda halin rayuwa da butulci irin na dan Adam.
Sai kuma yake tambayar kansa, shin me yasa ya damu kansa kan yarinyar? Damuwa irin wadda bai taba yi a kan kowa ba??? Ya tattara zancen ya watsar ya shiga sabgoginsa.
Da yammacin ranar yana barga tare da kaninsa Sha’aban dan Hakimi, kowannensu ingarman doki ya zaba Sarkin Dawaki ya aza musu sirdi suka dane suka nufi ‘yar shakatawa bayan gari.
Suna tafe hira suke yi kan sabbin gine-ginen zamani da Hakimi ke yi a cikin garin da ginin gidan saukar baki mai dauke da bukkokin zamani, inda Turawa ke sauka idan sun kawo ziyara. Haka nan Hakimi na sauke bakin alfarma idan sun zo.
Ibraheem ya yi sha’awar wadannan gine-ginen sosai. Yake ce da Sha’aban duk lokacin da ya tashi ginin gida zai sanya ‘Hut’ wato bukka ta gargajiya mai suffar zamani.
Sanda suka dawo magariba ta gabato, suka sauka daga dawakan suka soma alwala a famfon wajen. Kamar an ce da Ibrahim ‘juya’, ya hango Rahane na yankewa Babanta akaifa da nail cut. Sai dai bai jin me suke cewa a tsakaninsu.
To haka washe gari da misalin karfe goma na safe ya shigo bargar domin an kawo sababbin (Polo Horses) daga Ireland duka na Baba Dacta ne, yake ba da hayarsu ga masu sana’ar tseren Dawaki ake masa kiwon su anan bargar hakimi. Sun bambanta sosai da sauran dawakan ko daga koshinsu da shekin da suke yi da kuzari.
Ya dan juya ido sai ya hango Rahane da jibgin kayan wankin Babanta da ta tattaro tana ta dirzarsu kamar Allah ya aikota. Shi kuma Baban yana gefe yana yiwa dawakin askin jelarsu da katon almakashi. Yana cewa,
“Wato Rahane ba kya jin magana ko? Na ce ki bar wankin nan ya fi karfinki in na gama zan yi abina”.
Ta ce, “Albarka nake nema Baba, ka barni in samu, in ban yi maka ba wa zan yiwa? Idan mun tafi ban san yaushe zamu kara dawowa ba”.
Ibraheem ya jinjina kai suka kara ba shi tausayi.
Washegari suka yi sallama da kowa za su tafi, Rahane har kuka ta yi saboda ba ta son barin Babanta. Amma ba ta bari Baba Dacta ya gani ba, sauri ta yi ta dauke hawayen da yatsunta.
Da gudu ta koma ta sake rungume Babanta, sannan ta shiga mota tana share hawaye da sauri.
Har Ibraheem ya kunna mota ya hango Mal. Rashidu tafe da sassarfarsa rike da katuwar leda, don haka ya dakata.
Baba Dacta ya sauke gilashi sai ya mika masa, “Yalo ne da kashu (cashew) babu yawa a yiwa yara tsaraba”.
Hannu biyu Baba Dacta yasa ya karba, ya ce, “Yara sun gode Baban Rayhanah. Allah ya kara nisan kwana”.
Ya sanya hannu cikin aljihu ya zaro naira dari biyu ya mikawa Aziza, “Ungo yarinya ka sha ruwa a hanya kin ji?”
Mami ce ta karba fuskarta fal fara’a ta ce, “Aziza ta gode Baba”.
Ya daga musu hannu suka ja motar suka tafi. Abida ta juyar da kai gefen taga tana tsaki mara sauti. Kamar ta rufe Mamin da duka da ta karba.
Su kuwa iyayen sun ji dadi har ransu. ALHERI komi kankantarsa dadi gare shi, amma ga wanda ya san mutuncin dan Adam.
Kafin la’asar sun iso Kano. A harabar gidan bakuwar mota ce kankanuwa mai santsi (one door, Camero) fake a harabar adana motoci.
Ai kuwa daga Jawahir, Abida har Azizah fita suka yi a guje har Azizah na faduwa, ta kuwa fashe da kuka, don har bakinta ya fashe.
Da sauri Rahane ta fito ta dauke ta tana goge mata jinin dake fita daga bakinta. Mami na ta fada za su kashe mata ‘ya sai ka ce yau suka fara ganin Khalifan. Amma ko jin ta basu yi ba balle su tsaya. Sai da suka dangane ga dan’uwansu suka rungume shi.