Sashe 6
Rayuwar Rayhana Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Gaba dayansu suka dube shi sosai har Rahanen. I.M ya mike ya fice a ranshi yana yiwa Babanshi Allah ya kara. Haka kawai don bala’i da kwashe-kwashe zai kwaso musu wasu shirgin kauye babu gaira babu dalili. Ai gara da uban nata ya gwale shi, ya yi tafiyarsa cikin gida.
Hakimi ya karbi Dacta Mansur wanda ya yi mutuwar zaune ya ce, “Yar wannan yarinyar za ka yiwa auren? Wa za ka aura mata? Wa ya ce yana sonta?”
Mal. Rashidu ya ce, “Ku yi hakuri don Allah, na gode da taimakon ku garemu ba wai ban gode ba, amma idan na yi mata aure hankalina zai fi kwanciya, kuma na riga na karbi sadakinta.
Ado dai da kuka sa aka kama ku sako shi, don na riga na ci sadakinsa, tun kan a haifi Rahane yake hidima dani, bani da abin da zan biya shi ban da in aura masa Rahane. Ku yi hakuri don Allah, na riga na ba shi aure”.
Rahane ta fashe da kuka, “Baba Dacta ku ceceni bana son sa...wallahi bana son sa…!!!”.
Ta gurfana gaban Dr. Mansur tana rera kuka mai ban tausayi, ta buya a bayansa ta kankame shi. “Baba Dacta kashe ni zai yi....kana gani fa ya yaga min riga a gaban Babana… amma shine zai aura min shi?”
Ran Dacta Mansur ya yi mugun baci, lallai ya yarda komai akai da matsiyaci sai ya ci kara. Wannan Mal. Rashidun a jahilan ma bai san a ajin da yake ba. Kai baka ce shi da bakinsa yake fadar rashin arzikin da Ado ya yi masa ba, wai ya boye Rahane har ya yi attempting keta mata mutunci a gabansa, wannan shine mijin da zai bawa aure.
Ya ce, “Kai Malam! Ina jin dai ba lafiyarka kalau ba. Aure da wannan mutumin, mun hana, ya lissafa duk abin da ya kashe maka a biya shi, bayan ya gama zaman gidan kaso na keta haddin da yaso yi. Ba zan iya cin fuskarka ba albarkacin Rayhanah”.
Ya dau waya ya ce, “Ibraheemu jeka ofishin ‘yan sandan nan ka ce su zo min da wannan mutumin da nasa aka kama yanzu-yanzun nan”.
I.M Takai tsaye ya yi rike da wayar hannunshi “What’s wrong with Daddy ne?” Ya dubi wayar hannunshi sosai cike da takaici, sannan ya dubi Nabilah diyar Hakimi da suke tsaye tare, “Mts! Daddy ya samu matsala Nabilah!”
Ta ce, “Matsalar me?”
Ya sake hura hanci ya ce, “Jirani ina zuwa”. Ya juya ya fita.
Cikin dan lokaci an kawo Ado fada. Malam Rashidu ya dube shi jikinsa yana ta rawa ya ce, “Yauwa don Allah ku sa a sake shi”.
Haushi ya kama Hakimi ya ce, “Kai Malam ka nutsu ka san a inda kake bama son shirmen banza”.
Malam Rashidu ya koma cikin nutsuwarsa. Dacta Mansur ya dubi Ado sosai ya ce, “Da gaske kana son auren diyar Malam Rashidu?”
Ado wanda ya ci kaniyarsa sosai a hannun ‘yan sanda ya ce, “Eh”.
Dacta ya ce, “Shine kuma za ka yi mata fyade a gaban ubanta?”
Ya ce, “Ba nufina kenan ba”.
Dacta ya ce, “To meye nufin ka na tsaraita ta?”
Ya yi shiru. Dacta ya ci gaba da kallonsa a ransa yana mamakin Malam Rashidu, wai wannan mutumin mai kama da ‘yan fashi zai aurawa innocent yarinya kamar Rayhanah.
Ya boye mamakinsa ya ce, “Sulhu nake nema da kai”.
Ado ya dago a fusace, sai kuma suka yi mishi kwarjini ya kasa cewa komai. Dacta ya ci gaba da cewa, “Ka lissafa duk abin da ka kashewa Mal. Rashidu da ‘yarsa zan fanshe su ba ta isa aure ba!”
Ado ya gallawa Mal. Rashidu harara wanda ya takure ya yi lakwam yana kallon Ado a tsorace. Ado ya bude wawulon bakinsa ya ce cikin zafin rai, “Hakorana da aka zubar min fa?”
“Zamu makala maka na roba yanzu”.
Ya ce, “To a rabani da ‘yan sandan nan”.
Hakimi ya ce, “An raba ku”.
Ado ya ce, “Naira dubu dari biyar zaku bani, kuma su tashi su bar min gidana”.
Hakimi ya yi murmushi, ya jawo wata bakar akwati ya bude, ya dauko daurin kudi ‘yan dubu-dunu dauri biyar ya zube su a gaban Ado.
“Gasu, gidanka kuwa ko komawa ba zasu yi ba. Duk tarkacen dake ciki ma sun bar maka. ‘Yan zaman makokin ma in kaso ka koresu ka koresu su zo nan su yi”.
Ado ya gigice don dai kawai ya shaci kudin ne da gayya bai taba zaton ba za suyi musu ba.
Ya kwashi kudi ya nade cikin rigarsa ya mike zai fita, cike da tsoron kada su kwace kafin ya kai kofa. Dariya ta kama Dacta Mansur ya ce, “Hakoran fa Ado?’
Ya ce, “Barsu kawai, zan je kudu a sa min”.
Gaba daya suka sa dariya har Mal. Rashidu dake takure a gefe sai da ya murmusa.
Karshen diramar Ado da Rahane kenan. Tunda ya hada kudin nan ya gudu ya bar Takai, ya bar ‘ya’yansa da matarsa ba a kara jin duriyarsa ba. Aka bawa Mal. Rashidu muhalli a cikin gidajen bayin Hakimi, washegari ya fara aikinsa na kula da Dawakin Hakimi.
Dr. Mansur da dansa I.M suka taho Kano da Rahane, bayan ta yi sallama da babanta.
RAHANE A GIDAN DR. MANSOOR
Gidan Dr. Mansur Balarabe Takai babban gida ne mai tsarin gaske a unguwar Lamido Crescent, wanda ke rufe cikin bakin girgijejen get. Asalinsa Turawa ne suka zauna cikinsa shekaru masu yawa da suka gabata lokacin mulkin soja sanda suka bude kamfanin PZ da za su koma kasarsu suka sayarwa gwamnati.
Lokacin da Dr. Mansur ya yi kwamishinan lafiya a Kano, lokacin Gwamna Kabiru Gaya, gwamnati ta bashi gidan ya zauna, da tenure din su ya kare ya yi kokarin da ya sayi gidan da taimakon mahaifinshi mai girma Hakimin Takai na III (Balarabe Sardauna).
Haka ya ci gaba da sabunta gidan, yadda zai yi dai-dai da zamanin da ake ciki har kawo yau.
Gidan farin fenti ne da shi, kana shigowa cikin get din gidan mikakkiyar kwalta ce wadda zata sadaka da rumfar adana motoci a kalla biyar, ba tare da kowacce ta gogi ‘yar’uwarta ba.
Idan ka yo gaba kadan grass carpet ne wanda zai kai ka bakin kofar reception din gidan. A cikin reception din matattakalar bene take wadda za ta sadaka da falon sama da yake kunshe da dakunan barcin jama’ar gidan.
Dakunan barci hudu ne a cikin falon, daya na Dr. Mansoor, daya na Mami, daya na I.M da Yayansa Khalipha, wanda a halin yanzu yake karatu a jami’ar BAZE dake Abuja, yana karantar hulda da kasashen ketare wato (International Relation). Daya dakin na Abida da Jawahir ne, sai autar su Azizah.
Abida shekarunta takwas, Jawahid goma, Mami ta dade bayan haihuwar Abida kafin ta haifi Aziza wadda ke da shekaru uku a halin yanzu.
Saboda tsantsenin tarbiyya irin na Dr. Mansur bai warewa I.M da Khalipha daki a wajen gidansa ba, duk da girmansu tare yake dasu yana ganin kowanne motsinsu. Idan abokai ne ga reception nan bai yarda ko baskwata su zauna ba, masu aikace-aikacen gidan ne a baskwatan.
Motar Dr. Mansur ta sako kai farfajiyar gidansa. Ibraheem ne ke tukin. Dacta na gaban motar rike da jaridar This Day da ya saya a go slow din roundabout na kofar Nassarawa. Rahane na baya a makure jikin kofar motar kamar ka ce kyat! Ta bude murfin motar ta arta a na kare.
Abida da Jawahid ne zaune a rumfar adana motoci tare da malamin Islamiyyarsu dake zuwa duk Alhamis da Juma’a yana koya musu karatun Alkur’ani da Hadisi, tajweed da Tawheeed, ga bakin allo (black board) an kafa musu cikin rumfar adana motocin. Ta bala’in raina malamin, don Abida ‘yar rainin wayau ce, sabanin Jawahir da ko magana ba sosai take yinta ba.
Jin shigowar motar Daddy Abida ta nutsu daga mintsinin Jawahir da take yi, shi kansa Malam Umar ya lura Abida ta shiga taitayinta, don haka ya juyo don ganin abin da ya nutsar da ita.
Daddy ne da Ibraheem ke fitowa daga mota, tare da wata dukun-dukun din yarinya baka wuluk! Kanta a daure cikin wani bakin tsumma da wani sidadden silifa a kafarta, ko’ina a jikinta ciwo ne, wani da plasta wani plastar ta daye.
Abida ta soma zungurin Jawahir don ita ma ta juya ta ga abin da ta gani, amma Jawahir ta yi banza da ita ta ki juyawa ta ba da hankalinta sosai ga Malam Umar.
Malam din ya aje Alkur’anin dake hannunsa ya isa ga Daddy ya tsugunna yana gaisuwa. Daddy ya amsa ta hanyar bashi hannu sukayi musabiha. Tuni Ibraheem ya shige gida. Daddy ya kama hannun Rahane suka doshi reception.
Rahane dai taku take a tsorace, don ita tunda Allah ya halicce ta bata taba ganin waje irin wannan ba, kamar Aljanna da ake kwatantawa.
Hakimi ya karbi Dacta Mansur wanda ya yi mutuwar zaune ya ce, “Yar wannan yarinyar za ka yiwa auren? Wa za ka aura mata? Wa ya ce yana sonta?”
Mal. Rashidu ya ce, “Ku yi hakuri don Allah, na gode da taimakon ku garemu ba wai ban gode ba, amma idan na yi mata aure hankalina zai fi kwanciya, kuma na riga na karbi sadakinta.
Ado dai da kuka sa aka kama ku sako shi, don na riga na ci sadakinsa, tun kan a haifi Rahane yake hidima dani, bani da abin da zan biya shi ban da in aura masa Rahane. Ku yi hakuri don Allah, na riga na ba shi aure”.
Rahane ta fashe da kuka, “Baba Dacta ku ceceni bana son sa...wallahi bana son sa…!!!”.
Ta gurfana gaban Dr. Mansur tana rera kuka mai ban tausayi, ta buya a bayansa ta kankame shi. “Baba Dacta kashe ni zai yi....kana gani fa ya yaga min riga a gaban Babana… amma shine zai aura min shi?”
Ran Dacta Mansur ya yi mugun baci, lallai ya yarda komai akai da matsiyaci sai ya ci kara. Wannan Mal. Rashidun a jahilan ma bai san a ajin da yake ba. Kai baka ce shi da bakinsa yake fadar rashin arzikin da Ado ya yi masa ba, wai ya boye Rahane har ya yi attempting keta mata mutunci a gabansa, wannan shine mijin da zai bawa aure.
Ya ce, “Kai Malam! Ina jin dai ba lafiyarka kalau ba. Aure da wannan mutumin, mun hana, ya lissafa duk abin da ya kashe maka a biya shi, bayan ya gama zaman gidan kaso na keta haddin da yaso yi. Ba zan iya cin fuskarka ba albarkacin Rayhanah”.
Ya dau waya ya ce, “Ibraheemu jeka ofishin ‘yan sandan nan ka ce su zo min da wannan mutumin da nasa aka kama yanzu-yanzun nan”.
I.M Takai tsaye ya yi rike da wayar hannunshi “What’s wrong with Daddy ne?” Ya dubi wayar hannunshi sosai cike da takaici, sannan ya dubi Nabilah diyar Hakimi da suke tsaye tare, “Mts! Daddy ya samu matsala Nabilah!”
Ta ce, “Matsalar me?”
Ya sake hura hanci ya ce, “Jirani ina zuwa”. Ya juya ya fita.
Cikin dan lokaci an kawo Ado fada. Malam Rashidu ya dube shi jikinsa yana ta rawa ya ce, “Yauwa don Allah ku sa a sake shi”.
Haushi ya kama Hakimi ya ce, “Kai Malam ka nutsu ka san a inda kake bama son shirmen banza”.
Malam Rashidu ya koma cikin nutsuwarsa. Dacta Mansur ya dubi Ado sosai ya ce, “Da gaske kana son auren diyar Malam Rashidu?”
Ado wanda ya ci kaniyarsa sosai a hannun ‘yan sanda ya ce, “Eh”.
Dacta ya ce, “Shine kuma za ka yi mata fyade a gaban ubanta?”
Ya ce, “Ba nufina kenan ba”.
Dacta ya ce, “To meye nufin ka na tsaraita ta?”
Ya yi shiru. Dacta ya ci gaba da kallonsa a ransa yana mamakin Malam Rashidu, wai wannan mutumin mai kama da ‘yan fashi zai aurawa innocent yarinya kamar Rayhanah.
Ya boye mamakinsa ya ce, “Sulhu nake nema da kai”.
Ado ya dago a fusace, sai kuma suka yi mishi kwarjini ya kasa cewa komai. Dacta ya ci gaba da cewa, “Ka lissafa duk abin da ka kashewa Mal. Rashidu da ‘yarsa zan fanshe su ba ta isa aure ba!”
Ado ya gallawa Mal. Rashidu harara wanda ya takure ya yi lakwam yana kallon Ado a tsorace. Ado ya bude wawulon bakinsa ya ce cikin zafin rai, “Hakorana da aka zubar min fa?”
“Zamu makala maka na roba yanzu”.
Ya ce, “To a rabani da ‘yan sandan nan”.
Hakimi ya ce, “An raba ku”.
Ado ya ce, “Naira dubu dari biyar zaku bani, kuma su tashi su bar min gidana”.
Hakimi ya yi murmushi, ya jawo wata bakar akwati ya bude, ya dauko daurin kudi ‘yan dubu-dunu dauri biyar ya zube su a gaban Ado.
“Gasu, gidanka kuwa ko komawa ba zasu yi ba. Duk tarkacen dake ciki ma sun bar maka. ‘Yan zaman makokin ma in kaso ka koresu ka koresu su zo nan su yi”.
Ado ya gigice don dai kawai ya shaci kudin ne da gayya bai taba zaton ba za suyi musu ba.
Ya kwashi kudi ya nade cikin rigarsa ya mike zai fita, cike da tsoron kada su kwace kafin ya kai kofa. Dariya ta kama Dacta Mansur ya ce, “Hakoran fa Ado?’
Ya ce, “Barsu kawai, zan je kudu a sa min”.
Gaba daya suka sa dariya har Mal. Rashidu dake takure a gefe sai da ya murmusa.
Karshen diramar Ado da Rahane kenan. Tunda ya hada kudin nan ya gudu ya bar Takai, ya bar ‘ya’yansa da matarsa ba a kara jin duriyarsa ba. Aka bawa Mal. Rashidu muhalli a cikin gidajen bayin Hakimi, washegari ya fara aikinsa na kula da Dawakin Hakimi.
Dr. Mansur da dansa I.M suka taho Kano da Rahane, bayan ta yi sallama da babanta.
RAHANE A GIDAN DR. MANSOOR
Gidan Dr. Mansur Balarabe Takai babban gida ne mai tsarin gaske a unguwar Lamido Crescent, wanda ke rufe cikin bakin girgijejen get. Asalinsa Turawa ne suka zauna cikinsa shekaru masu yawa da suka gabata lokacin mulkin soja sanda suka bude kamfanin PZ da za su koma kasarsu suka sayarwa gwamnati.
Lokacin da Dr. Mansur ya yi kwamishinan lafiya a Kano, lokacin Gwamna Kabiru Gaya, gwamnati ta bashi gidan ya zauna, da tenure din su ya kare ya yi kokarin da ya sayi gidan da taimakon mahaifinshi mai girma Hakimin Takai na III (Balarabe Sardauna).
Haka ya ci gaba da sabunta gidan, yadda zai yi dai-dai da zamanin da ake ciki har kawo yau.
Gidan farin fenti ne da shi, kana shigowa cikin get din gidan mikakkiyar kwalta ce wadda zata sadaka da rumfar adana motoci a kalla biyar, ba tare da kowacce ta gogi ‘yar’uwarta ba.
Idan ka yo gaba kadan grass carpet ne wanda zai kai ka bakin kofar reception din gidan. A cikin reception din matattakalar bene take wadda za ta sadaka da falon sama da yake kunshe da dakunan barcin jama’ar gidan.
Dakunan barci hudu ne a cikin falon, daya na Dr. Mansoor, daya na Mami, daya na I.M da Yayansa Khalipha, wanda a halin yanzu yake karatu a jami’ar BAZE dake Abuja, yana karantar hulda da kasashen ketare wato (International Relation). Daya dakin na Abida da Jawahir ne, sai autar su Azizah.
Abida shekarunta takwas, Jawahid goma, Mami ta dade bayan haihuwar Abida kafin ta haifi Aziza wadda ke da shekaru uku a halin yanzu.
Saboda tsantsenin tarbiyya irin na Dr. Mansur bai warewa I.M da Khalipha daki a wajen gidansa ba, duk da girmansu tare yake dasu yana ganin kowanne motsinsu. Idan abokai ne ga reception nan bai yarda ko baskwata su zauna ba, masu aikace-aikacen gidan ne a baskwatan.
Motar Dr. Mansur ta sako kai farfajiyar gidansa. Ibraheem ne ke tukin. Dacta na gaban motar rike da jaridar This Day da ya saya a go slow din roundabout na kofar Nassarawa. Rahane na baya a makure jikin kofar motar kamar ka ce kyat! Ta bude murfin motar ta arta a na kare.
Abida da Jawahid ne zaune a rumfar adana motoci tare da malamin Islamiyyarsu dake zuwa duk Alhamis da Juma’a yana koya musu karatun Alkur’ani da Hadisi, tajweed da Tawheeed, ga bakin allo (black board) an kafa musu cikin rumfar adana motocin. Ta bala’in raina malamin, don Abida ‘yar rainin wayau ce, sabanin Jawahir da ko magana ba sosai take yinta ba.
Jin shigowar motar Daddy Abida ta nutsu daga mintsinin Jawahir da take yi, shi kansa Malam Umar ya lura Abida ta shiga taitayinta, don haka ya juyo don ganin abin da ya nutsar da ita.
Daddy ne da Ibraheem ke fitowa daga mota, tare da wata dukun-dukun din yarinya baka wuluk! Kanta a daure cikin wani bakin tsumma da wani sidadden silifa a kafarta, ko’ina a jikinta ciwo ne, wani da plasta wani plastar ta daye.
Abida ta soma zungurin Jawahir don ita ma ta juya ta ga abin da ta gani, amma Jawahir ta yi banza da ita ta ki juyawa ta ba da hankalinta sosai ga Malam Umar.
Malam din ya aje Alkur’anin dake hannunsa ya isa ga Daddy ya tsugunna yana gaisuwa. Daddy ya amsa ta hanyar bashi hannu sukayi musabiha. Tuni Ibraheem ya shige gida. Daddy ya kama hannun Rahane suka doshi reception.
Rahane dai taku take a tsorace, don ita tunda Allah ya halicce ta bata taba ganin waje irin wannan ba, kamar Aljanna da ake kwatantawa.