Sashe 4
Rayuwar Rayhana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
****
Cikin wadanda aka kwasa zuwa asibitin koyarwa na Kano, cikin masu hatsarin da suka tsira da numfashinsu har da Rahane. Cikin gawarwakin da aka kai mutuware kuma har da Iya Bilki.
A hankali Rahane ke bude idanunta tana kallon likitan da ke tsira mata allura cikin jijiyoyin hannunta.
Abubuwan suka soma dawowa Rahane tar-tar a idanunta. Da sauri ta juya gefenta inda Iya Bilki ke zaune, babu kowa. Kai dakin ma da take ciki ba ta taba ganin irinshi ba. Haka mutanen da take gani suna gilmawa ba ta saba ganin irinsu ba.
Wadannan fes-fes suke cikin fararen kaya masu tsabta, ba irin kalar jama’ar da ta saba gani bane.
Dr. Mansur, ya manyanta sosai, shine babban likita yau a emergency, yana daga zaune yake bai wa dalibansa dake tsaitsaye lacca na taimakon da za su yiwa Rahane, wadda goshinta ya fashe ko’ina kaca-kaca da jini a jikinta, ba za ka iya tantance iyakacin raunin da ta ji ba.
Dinke nan, like nan haka suka yi ta yi, yayin da kuka ya gagari Rahane saboda azabar da take ji a cikin gangar jikinta tayi azaba. Ta suma ya fi sau uku suna kakaba mata oxygen tare da bata taimakon duk da ya dace.
Washegari da ta farka karfe takwas na safe da dan sauki jikin nata. Don haka ta fara kuka a hankali. Dai-dai da shigowar Dr. Mansur da tawagar kananan likitoci dake binsa a baya.
Cikinsu har da photocopy na Dr. Mansur wato matashin likitan da ke (housemanship) mai amsa sunan I.M Takai, wato IBRAHIM MANSUR TAKAI.
Da gani babu tambaya ka ga uba da dansa. Duk da yanayin halayyarsu a fuska ya nuna ba daya bane, domin shi Dr. Mansur mutum ne mai sakin fuska sosai, sabanin Ibraheem da yake mutum mara walwala sam-sam. Duk abin da Dr. Mansur ke yiwa Rahane suna jotting ne.
Dr. Mansur ya matsa dai-dai kan Rahane ya dora hannunshi a kanta ya ce, “Daina kuka kin ji? Insha Allah za ki samu lafiya”.
Ta cira idanunta da suka kada suka yi jawur a hankali ta dube shi, bakinta na motsi amma ta kasa magana.
Ya dubi Ibraheem ya ce, “Dagata ta zauna”. Ya cirata ta zauna ya tusa mata filo a bayanta ta zauna sosai.
Dr. Mansur ya ce, “Me sunanki?” Bin shi ta yi da ido kawai ba ta yi magana ba. Ya ce, “Ku rabu da ita ta warware a hankali”.
Nurse din da suke tare ta mika mata kofin tea. Dr. Mansur ya ce, “Bata shayin ta sha Ibrahimu”.
Ya yi kamar bai ji ba, ya yi baya kadan ya dan tura Eric Ipatobe abokin karatunsa dake gabansa yayi baya. Shima Dr. Mansur sai ya yi kamar bai ga abin da ya yi din ba. Cikin girgiza kai ya karbi kofin ya matsa sosai ya soma bata da kansa. Yana fadi cikin ransa, dani kake zancen, wallahi sai na kwashe maka maki (marks).
Mamaki ya kama su dukkansu, Doctor Mansur da kansa! Da sauri Nurse din ta karba tana bata. Ya dan ja baya ya sarke hannun shi a kirjinsa bai kara kallon Ibrahim ba. Ya ci gaba da feso musu lacca kamar Obama ya diro Nijeriya.
Kwana uku Dr. Mansur na kula da Rahane, ta ji sauki sosai amma ta ki magana. Don haka ya soma tunanin akwai wani abu. “There must be something wrong beneath!” Ya fadawa su Ibraheem.
Ya girgiza kai ya juya gare su, “Tana bukatar ganin likitan kunne da makogaro yayi examining dinsu, wanda wannan ba shine darasin da muke a kanshi ba tukunna, muna neman lafiyar gangar jikinta ne gaba daya”.
Cikin sati biyu Dr. Mansur ya ba da hankalin shi da kwarewar shi gaba daya a kan Rahane da shi da Dr. Imam, kwararren likitan kunnen da ake ji da shi a AKTH. Duk wani taimako da ya kamata ya bata sun bata, amma Rahane sai da aka dangana da hearing test wanda ya nuna ta gamu da very unusual hearing issue, wanda ke bukatar ayi CT Scan da MRI Scan, dake bukatar kudi na fitar hankali wanda zai nuna hakikanin menene matsalarta daga inner and outer zones na kunne da kwakwalwarta, a dalilin rashin sanin daga inda ta bullo da kuma rashin sanin kowa nata, suka samar da occasional hearing Aid gareta, sannan ta ji abin da suke cewa. Amma idan aka cire bazata ji ba. Duka daga aljihun Dr. Mansur Takai, wanda Allah ya sakawa kaunar Rahane da tausayin ta,
Yau Asabar ba shine on call ba, Dr. Hashim ne, amma sai da ya shigo asibitin musamman don yaga jikin Rahane. ‘Yar shi karama AZiza na rike da hannun shi, caftan na shadda milk colour ne a jikinshi da hular da ta dace dasu ba suit da lab-coat ba.
Rahane na hangoshi ta soma murmushi, shima murmushin yake mata. Ganin ta zauna ras alamun lafiya na samuwa, ya ja kujerar dake gabanta ya zauna.
“Yar Doctor, lallai lafiya ta samu”.
A sanyaye ta ce, “Alhamdulillah!”
Lokaci na farko da ya ji furucin bakinta, tun ranar da su kai hatsarin.
Shima ya ce, “Alhamdulillah ‘yata ya ya sunanki?”
Ta ce, “Rahane”.
Ya bushe da dariya, “RAYHANAH kenan ko?’
“A’a, RAHANE!” Ta sake gyara masa.
“To na yarda Rayhanatu, ni ba zan iya fadar wancan din ba, saboda ba shi da ma’ana kwata-kwata”.
Dr. Hashim na jinsu yana dariya yana auna patient din gadon kusa da ita. Lokaci guda Rahane ta soma kuka. Duka likitocin suka tsaida dariyar suka yi kanta.
“Kuka Rayhanah? Daina kuka har gida zamu kai ki. Fatanmu shine Allah ya baki lafiya mu tambayeki ke da waye kuka taho? Kuma ina ne garinku?”
“Ni da Iya ne, kuma ban ganta ba tun ranar”.
“Za ki iya gane ta cikin kowanne hali?”
Ta ce, “Eh”.
“Daga ina kuke?”
“Takai, zamu Tsangaya”.
“Takai? Ikon Allah”.
Ya yi dan shiru yana kallon ta. “Sunana Dr. Mansur Balarabe Takai....”
Ta dube shi da sauri. Ya gyada mata kai yana dariya. Dr. Hashim ya juyokadan ya ce, “Dr. Takai, ashe ‘yar taka ‘yar garinku ce, dole a bata extra kulawa, kyakkyawa da ita, ina kamu Doctor”.
Murmushi ya yi, ya ce da Nurse dake gefe a kawo Rahane ‘matuary”.
A kujerar daukar marassa lafiya nurses biyu suka turata zuwa mutuware.
Aka soma zarowa Rahane akwatunan gawarwaki abin babu kyawun gani. Rahane ba ta taba ganin gawa ba sai yau a idanunta. Iyakacin firgita ta firgita, amma da aka zaro Iya Bilki, ba ta san sanda ta fada kanta ta rungumeta ba. Kuka take na fitar hankali, domin Iya sumul take babu ko kwarzane a jikinta. Idanunta ne kurum a rufe kamar mai barci, kamar ta ce “Iya”. Ta bude ido ta amsa mata.
Da kyar Dr. Mansur ya janyeta, aka hada Iya cikin motar daukar gawarwaki na asibitin. Motar Dr. Mansur na biye dauke da Rahane da I.M a gidan gaba, suka dauki hanyar Takai.
Rahane na baya ta kankame jikinta tana kuka mai cin rai, sai dai daga Doctor har dansa Ibraheem babu mai jin ta sakamakon kira’ar Ahmad Sulaiman da Dr. Mansur ya saki a motar har suka isa garin Takai.
Rahane ke nuna musu hanya da aka shigo Takai har kofar gidansu. Tana hango Akori-Kurar Ado a kofar gidansu gabanta ya yi mugun faduwa. Hakan bai hanata fitowa daga motar ba a lokacin da Ibraheem ya bude mata, yana ta zabga mata harara kamar ya hankadata.
“Shiga ki karawo shi Rayhanah”. In ji Baba Dacta (kamar yadda take kiranshi)
Da addu’a tasa kai cikin gidansu. Ta yi sallama ba a amsa ba. Sai kawai tasa kai. Caraf! Ado ya cafke ta ya danneta a dakin Iya, nan ta ga babanta a makure a gefe daga shi sai gejeran wando, ko’ina a jikinsa shatin bulala ne, jini ya bisu ya kwanta.
Ado ya ce, “Munafiki! To gata ta dawo da kafafunta, auren ma na fasa a gabanka zan yi kaca-kaca da mutuncin ta in fanshe wahalata ta shekara da shekaru”.
Bai yi la’akari da halin ciwuwwukan da ke jikinta ba ya hadata da bango ya keta rigar jikinta tun daga sama har kasa.......!
Ihun da Rahane ta zabga ya amsa kuwwa har sauran gidajen da ke makwabtaka dasu suka jiyo. Dr. Mansur na waya, dansa Ibraheem ya yi saurin dagowa ya ce,
“Daddy.....yarinyar nan ihu fa take yi”.
Da sauri Dr. Mansur ya juyo, shima kunnuwansa suka jiyo masa kururuwar da Rahane ke zabgawa. Shi da Ibraheem suka runtuma cikin gidan ba tare da sunyi wata maganar ba.
A lokacin Ado ya kaita kasa, dan kamfai ne kawai a jikinta. Ga Malam Rashidu a gefe dunkule wuri daya yana ta kwararar da hawaye sai tsima yakeyi ko uffan bai ce ba.
Ibraheem ya danko kwalar rigarshi ya finciko shi ya hada shi da bango, ya dunkule hannu ya sauke a bakin Ado, sai ga hakora biyar sun zubo, jini ya biyo bayansu. Ya tankada shi tsakar gidan da doguwar kafarsa.
A lokacin jama’a makota har sun cika gidan, shi kuma Daddy waya ya yiwa ‘yan sanda nan da nan sai gasu a (shiga-ba-biya) suka danna Ado a ciki, jama’a na ta sallallami ganin Malam Rashidu daga shi sai gajeran wando gaba daya ya fita hayyacinsa ya zama dan tsurut. Jikinsa ba masaka tsinke da tambarin bulala. Rahane na gefe ta kankame jikinta tana ta kuka.
I.M Takai, ya ciro suit din dake jikinsa ya rufa mata, don ta kare tsaraicinta.
Nan Malam Rashidu ya matsa gaban Rahane ya saka kuka. Cewa yake
“Ina Iya Rahane?”
Cikin wadanda aka kwasa zuwa asibitin koyarwa na Kano, cikin masu hatsarin da suka tsira da numfashinsu har da Rahane. Cikin gawarwakin da aka kai mutuware kuma har da Iya Bilki.
A hankali Rahane ke bude idanunta tana kallon likitan da ke tsira mata allura cikin jijiyoyin hannunta.
Abubuwan suka soma dawowa Rahane tar-tar a idanunta. Da sauri ta juya gefenta inda Iya Bilki ke zaune, babu kowa. Kai dakin ma da take ciki ba ta taba ganin irinshi ba. Haka mutanen da take gani suna gilmawa ba ta saba ganin irinsu ba.
Wadannan fes-fes suke cikin fararen kaya masu tsabta, ba irin kalar jama’ar da ta saba gani bane.
Dr. Mansur, ya manyanta sosai, shine babban likita yau a emergency, yana daga zaune yake bai wa dalibansa dake tsaitsaye lacca na taimakon da za su yiwa Rahane, wadda goshinta ya fashe ko’ina kaca-kaca da jini a jikinta, ba za ka iya tantance iyakacin raunin da ta ji ba.
Dinke nan, like nan haka suka yi ta yi, yayin da kuka ya gagari Rahane saboda azabar da take ji a cikin gangar jikinta tayi azaba. Ta suma ya fi sau uku suna kakaba mata oxygen tare da bata taimakon duk da ya dace.
Washegari da ta farka karfe takwas na safe da dan sauki jikin nata. Don haka ta fara kuka a hankali. Dai-dai da shigowar Dr. Mansur da tawagar kananan likitoci dake binsa a baya.
Cikinsu har da photocopy na Dr. Mansur wato matashin likitan da ke (housemanship) mai amsa sunan I.M Takai, wato IBRAHIM MANSUR TAKAI.
Da gani babu tambaya ka ga uba da dansa. Duk da yanayin halayyarsu a fuska ya nuna ba daya bane, domin shi Dr. Mansur mutum ne mai sakin fuska sosai, sabanin Ibraheem da yake mutum mara walwala sam-sam. Duk abin da Dr. Mansur ke yiwa Rahane suna jotting ne.
Dr. Mansur ya matsa dai-dai kan Rahane ya dora hannunshi a kanta ya ce, “Daina kuka kin ji? Insha Allah za ki samu lafiya”.
Ta cira idanunta da suka kada suka yi jawur a hankali ta dube shi, bakinta na motsi amma ta kasa magana.
Ya dubi Ibraheem ya ce, “Dagata ta zauna”. Ya cirata ta zauna ya tusa mata filo a bayanta ta zauna sosai.
Dr. Mansur ya ce, “Me sunanki?” Bin shi ta yi da ido kawai ba ta yi magana ba. Ya ce, “Ku rabu da ita ta warware a hankali”.
Nurse din da suke tare ta mika mata kofin tea. Dr. Mansur ya ce, “Bata shayin ta sha Ibrahimu”.
Ya yi kamar bai ji ba, ya yi baya kadan ya dan tura Eric Ipatobe abokin karatunsa dake gabansa yayi baya. Shima Dr. Mansur sai ya yi kamar bai ga abin da ya yi din ba. Cikin girgiza kai ya karbi kofin ya matsa sosai ya soma bata da kansa. Yana fadi cikin ransa, dani kake zancen, wallahi sai na kwashe maka maki (marks).
Mamaki ya kama su dukkansu, Doctor Mansur da kansa! Da sauri Nurse din ta karba tana bata. Ya dan ja baya ya sarke hannun shi a kirjinsa bai kara kallon Ibrahim ba. Ya ci gaba da feso musu lacca kamar Obama ya diro Nijeriya.
Kwana uku Dr. Mansur na kula da Rahane, ta ji sauki sosai amma ta ki magana. Don haka ya soma tunanin akwai wani abu. “There must be something wrong beneath!” Ya fadawa su Ibraheem.
Ya girgiza kai ya juya gare su, “Tana bukatar ganin likitan kunne da makogaro yayi examining dinsu, wanda wannan ba shine darasin da muke a kanshi ba tukunna, muna neman lafiyar gangar jikinta ne gaba daya”.
Cikin sati biyu Dr. Mansur ya ba da hankalin shi da kwarewar shi gaba daya a kan Rahane da shi da Dr. Imam, kwararren likitan kunnen da ake ji da shi a AKTH. Duk wani taimako da ya kamata ya bata sun bata, amma Rahane sai da aka dangana da hearing test wanda ya nuna ta gamu da very unusual hearing issue, wanda ke bukatar ayi CT Scan da MRI Scan, dake bukatar kudi na fitar hankali wanda zai nuna hakikanin menene matsalarta daga inner and outer zones na kunne da kwakwalwarta, a dalilin rashin sanin daga inda ta bullo da kuma rashin sanin kowa nata, suka samar da occasional hearing Aid gareta, sannan ta ji abin da suke cewa. Amma idan aka cire bazata ji ba. Duka daga aljihun Dr. Mansur Takai, wanda Allah ya sakawa kaunar Rahane da tausayin ta,
Yau Asabar ba shine on call ba, Dr. Hashim ne, amma sai da ya shigo asibitin musamman don yaga jikin Rahane. ‘Yar shi karama AZiza na rike da hannun shi, caftan na shadda milk colour ne a jikinshi da hular da ta dace dasu ba suit da lab-coat ba.
Rahane na hangoshi ta soma murmushi, shima murmushin yake mata. Ganin ta zauna ras alamun lafiya na samuwa, ya ja kujerar dake gabanta ya zauna.
“Yar Doctor, lallai lafiya ta samu”.
A sanyaye ta ce, “Alhamdulillah!”
Lokaci na farko da ya ji furucin bakinta, tun ranar da su kai hatsarin.
Shima ya ce, “Alhamdulillah ‘yata ya ya sunanki?”
Ta ce, “Rahane”.
Ya bushe da dariya, “RAYHANAH kenan ko?’
“A’a, RAHANE!” Ta sake gyara masa.
“To na yarda Rayhanatu, ni ba zan iya fadar wancan din ba, saboda ba shi da ma’ana kwata-kwata”.
Dr. Hashim na jinsu yana dariya yana auna patient din gadon kusa da ita. Lokaci guda Rahane ta soma kuka. Duka likitocin suka tsaida dariyar suka yi kanta.
“Kuka Rayhanah? Daina kuka har gida zamu kai ki. Fatanmu shine Allah ya baki lafiya mu tambayeki ke da waye kuka taho? Kuma ina ne garinku?”
“Ni da Iya ne, kuma ban ganta ba tun ranar”.
“Za ki iya gane ta cikin kowanne hali?”
Ta ce, “Eh”.
“Daga ina kuke?”
“Takai, zamu Tsangaya”.
“Takai? Ikon Allah”.
Ya yi dan shiru yana kallon ta. “Sunana Dr. Mansur Balarabe Takai....”
Ta dube shi da sauri. Ya gyada mata kai yana dariya. Dr. Hashim ya juyokadan ya ce, “Dr. Takai, ashe ‘yar taka ‘yar garinku ce, dole a bata extra kulawa, kyakkyawa da ita, ina kamu Doctor”.
Murmushi ya yi, ya ce da Nurse dake gefe a kawo Rahane ‘matuary”.
A kujerar daukar marassa lafiya nurses biyu suka turata zuwa mutuware.
Aka soma zarowa Rahane akwatunan gawarwaki abin babu kyawun gani. Rahane ba ta taba ganin gawa ba sai yau a idanunta. Iyakacin firgita ta firgita, amma da aka zaro Iya Bilki, ba ta san sanda ta fada kanta ta rungumeta ba. Kuka take na fitar hankali, domin Iya sumul take babu ko kwarzane a jikinta. Idanunta ne kurum a rufe kamar mai barci, kamar ta ce “Iya”. Ta bude ido ta amsa mata.
Da kyar Dr. Mansur ya janyeta, aka hada Iya cikin motar daukar gawarwaki na asibitin. Motar Dr. Mansur na biye dauke da Rahane da I.M a gidan gaba, suka dauki hanyar Takai.
Rahane na baya ta kankame jikinta tana kuka mai cin rai, sai dai daga Doctor har dansa Ibraheem babu mai jin ta sakamakon kira’ar Ahmad Sulaiman da Dr. Mansur ya saki a motar har suka isa garin Takai.
Rahane ke nuna musu hanya da aka shigo Takai har kofar gidansu. Tana hango Akori-Kurar Ado a kofar gidansu gabanta ya yi mugun faduwa. Hakan bai hanata fitowa daga motar ba a lokacin da Ibraheem ya bude mata, yana ta zabga mata harara kamar ya hankadata.
“Shiga ki karawo shi Rayhanah”. In ji Baba Dacta (kamar yadda take kiranshi)
Da addu’a tasa kai cikin gidansu. Ta yi sallama ba a amsa ba. Sai kawai tasa kai. Caraf! Ado ya cafke ta ya danneta a dakin Iya, nan ta ga babanta a makure a gefe daga shi sai gejeran wando, ko’ina a jikinsa shatin bulala ne, jini ya bisu ya kwanta.
Ado ya ce, “Munafiki! To gata ta dawo da kafafunta, auren ma na fasa a gabanka zan yi kaca-kaca da mutuncin ta in fanshe wahalata ta shekara da shekaru”.
Bai yi la’akari da halin ciwuwwukan da ke jikinta ba ya hadata da bango ya keta rigar jikinta tun daga sama har kasa.......!
Ihun da Rahane ta zabga ya amsa kuwwa har sauran gidajen da ke makwabtaka dasu suka jiyo. Dr. Mansur na waya, dansa Ibraheem ya yi saurin dagowa ya ce,
“Daddy.....yarinyar nan ihu fa take yi”.
Da sauri Dr. Mansur ya juyo, shima kunnuwansa suka jiyo masa kururuwar da Rahane ke zabgawa. Shi da Ibraheem suka runtuma cikin gidan ba tare da sunyi wata maganar ba.
A lokacin Ado ya kaita kasa, dan kamfai ne kawai a jikinta. Ga Malam Rashidu a gefe dunkule wuri daya yana ta kwararar da hawaye sai tsima yakeyi ko uffan bai ce ba.
Ibraheem ya danko kwalar rigarshi ya finciko shi ya hada shi da bango, ya dunkule hannu ya sauke a bakin Ado, sai ga hakora biyar sun zubo, jini ya biyo bayansu. Ya tankada shi tsakar gidan da doguwar kafarsa.
A lokacin jama’a makota har sun cika gidan, shi kuma Daddy waya ya yiwa ‘yan sanda nan da nan sai gasu a (shiga-ba-biya) suka danna Ado a ciki, jama’a na ta sallallami ganin Malam Rashidu daga shi sai gajeran wando gaba daya ya fita hayyacinsa ya zama dan tsurut. Jikinsa ba masaka tsinke da tambarin bulala. Rahane na gefe ta kankame jikinta tana ta kuka.
I.M Takai, ya ciro suit din dake jikinsa ya rufa mata, don ta kare tsaraicinta.
Nan Malam Rashidu ya matsa gaban Rahane ya saka kuka. Cewa yake
“Ina Iya Rahane?”