Sashe 2
Rayuwar Rayhana Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Sanda Rahane ta isa shiga makaranta lokaci ne da ya zo wa Rahane da karin hankali, ta lura mahaifinta bai damu da ita ba, sai ita kuma ta dage wajen kyautata masa da yi mishi hidima, gyaran dakinsa, wankin kayansa masu datti da zuba mishi ruwan wanka, rowan alwala a buta da sauransu.
Har kekensa take wankewa, sannan kullum ya dawo gida da gudu take taryo shi ta karbo kayan da ya zo dasu ta yi mishi shimfidar sallar magariba.
Tun baya kula har ya gane wata Yalwatin ce Allah ya bashi a matsayin diya. A hankali zuciyarshi ta soma kaunarta, da kanshi ya dauketa ya kaita makarantar firamare, sai dai mai nisa ce sosai da gidansu.
Don haka kullum yake goyata a bayan kekensa ya kaita, in sun tashi ta biyo kawayenta su dawo, don lokacin yana kasuwa.
Makarantar na karbar naira dari biyu da hamsin duk bayan watanni uku daga kowanne dalibi, haka yake kukkullawa ya biya, in bai bayar ba a koro ta, ta kwashe kwanaki a gida kamin ya samu ya biya.
Don lokacin Iya Bilki ta tsufa ainun ba ta sana’ar komai. Tun mutuwar Yalwati yau shekara tara kenan, Malam Rashidu ya ki yin aure, ba don komai ba sai don cewa ya san ba zai samu mai halin Yalwati ba da nagartarta.
Haka nan Iya Bilki ba ta fasa takura masa ba a kan ya yi auren, yana ta ba ta uziri. Don haka ba tare da yin shawara da shi ba ta nema mishi auren Zinaru kanwar Yalwati, uwa daya uba daya, da aurenta ya mutu tana da yara hudu tare da tsohon mijinta.
Shekarar Zinaru biyu tare da Malam Rashidu ta tada bala’in ba za ta zauna ba don talaucin ya isa. Ba haka ta saba a gidan tsohon mijinta ba. Dole ya sawwake mata tun da sauran mutunci, ya kuma roki Iya da ta yiwa Allah ta kyale shi da auren kowacce mace ba zai iya ba, sannan ba kowacce mace ba ce za ta iya zama da shi da talaucinsa irin Yalwati ba! Ta barshi ya raini diyar Yalwati kadai, ya inganta rayuwar ta, yayi mata aure in ta kai munzalin. Wannan ne kadai burin sa a rayuwa.
Bayan wannan ba shi da wani sauran buri, sai na gamawa da duniya lafiya, da cikawa da imani.
Iya ta share hawaye da habar zaninta saboda tuno Yalwati, da tijarar Zinaru, Allah daya gari bamban, kama da wane ba ta wane! Ita dama ta hada auren ne don tunanin Zinaru za ta yi halin Yalwati, ta rungumi diyar ‘yar’uwarta.
To ita Zinaru ma a tsayin shekaru biyu da ta yi a gidan, baiwa ta maida Rahane, suna ji suna gani basu isa suyi magana ba saboda tsoron bala’inta. Don haka rabuwarsu da ita, sai suka ji su sakayau.
Tun daga wannan lokaci Rashidu da mahaifiyarsa basu kara yin zancen ya yi aure ba. Kula da rayuwar Rahane ne a gabansu, da tarbiyyarta, lokacin shekarun Rahane goma sha daya tana firamare aji biyar.
Wata irin shakuwa ce tsakanin Rahane da kakarta, tamkar ta uwa da danta. Iya Bilki na da fada sosai, kuma ba ta daukar wargi. Duk wanda ya taba mata Rahane ko ya ya take da iyayensa ba ta kyalewa.
Idan samari suka aiko kiran Rahane da tabarya take korarsu, in har ka tsaya, ta rusa maka a baya. Wannan yasa duk samarin masu son Rahanen shakkarta, ba mai tare ta da zancen banza irin na sa’o’inta, don sun san karon da iyayensu za suyi da Iya Bilki.
Don haka Rahane ba ta da wani saurayi, amma sa’o’inta da yawa har an ba da su, wasu an sa musu rana. Iya kan ce da Rahane,
“Rabu da shashashai ki yi ta karatu, so nake ki zama malamar asibiti ki taimaki masu haihuwa a kauyen nan, kina dai ganin yadda duk auren wurin ya janyowa su Saude yoyon fitsari, ana ta fada a Radio a daina yiwa kananan yara aure amma basa ji”.
Shi kuwa Malam Rashidu ba shi da buri irin ya ga ya aurar da Rahane dai-dai wannan lokacin ga managarcin miji kamar sauran tsararrakinta, amma tunda ya lura Iya ba ta ko son zancen sai ya tsahirta. Daga baya Ado direba mai gidan dasu Malam Rashidu keciki ya daina karbar kudin hayarsa, sabida wani kuduri nasa na daban.
***
[12/24/2019, 17:56] Takori: Rahane ta shigo da kayan da babanta ya shigo dasu ta aje a tsakar gida, ta yi maza ta kawo mishi ruwan alwala ya karba ya ce, “Sannu Rahane kin ji? Allah ya yi miki albarka”. Ya karbi butar ya yi waje domin ya samu jam’i.
Su ma Rahane da Iya alwalar suka yi, Iya na sallah a daki Rahane na yi a tsakar gida. Bayan sun idar Rahane ta karasa gaban murhu tana cire itacen dake cin wuta tana zakulo garwashin tana kashewa da ruwa, sannan ta soma kwashewa Iya tuwon, tana sakawa kowa a kwanonsa.
Ta jiyo gyaran muryar babanta na kira a tsakar gida, da sauri ta mike tana amsawa ta zo ta durkusa
“Ga ni Baba”.
Ya zaro sauran kudin aljihunsa naira dari biyu da hamsin ya ba ta ya ce ta kai makaranta gobe ta ci gaba da zuwa makaranta.
Farin ciki ya kama Rahane ta ce, “Na gode Baba, Baba Allah ya kara buda maka”.
Ya ce, “Ameen Rahane, Ni dai fatana ki ci gaba da bada himma, kin ji?”
Ta ce, “Insha Allah Baba”.
Washegari Rahane ta koma makaranta, bayan Malam Rashidu ya sauke ta ya juya ya nufi kasuwa. Suna hanyar dawowa ita da Dije ‘yar ajinsu suka ji karar Akori-kurar Ado a bayansu, duk suka matsa gefe.
Ado ya rage gudun motar yana washe katon bakinsa wai shi a wurin shi murmushi yake. Ya ce,
“A’a, ‘yan makaranta an taso ne?” Jajayen idanuwanshi a kan Rahane.
Ko amsa mishi ba ta yi ba ta ci gaba da tafiyarta. Dije ce ta ce da shi, “Eh, mun taso”.
Ya ce, “To ku shigo in karasa daku”.
Dije ta ce, “A’a, ai mun kusa”.
Har yanzu idanunshi a kan Rahane ya ce, “Wai haka Rahane?”
Ko juyawa ba ta yi ba ta yi banza da shi. Bai ji haushi ba ya ci gaba da washe bakinsa ya ce,
“Tunda bakya magana a kan hanya Rahane, to ina nan zuwa da dare kin ji?”
Bai tsammaci amsarta ba daman, ya tada Akori-kurar sa ya yi gaba, ya kasa rufe bakin.
Iya na daki tana kadin auduga, Rahane ta yi sallama ta aje jakar makarantarta, ta fada jikin Iya Bilki tana fadin “Wash! Iya na gaji sosai”.
Iya ta rungumeta tana cewa, “Sannu ‘yar Iya, Allah ya nuna min lokacin da za ki fara yiwa mutane allura”.
Dariya ta yi ta ce, “Iya Baba fa ba zai barni in yi irin karatun nan da kike so ba, shi kullum maganarshi ta aure ce Iya. Ni kam duk abin da zai rabani da ke da gidan nan Iya bana son shi ko da karatun ne, kuma kin san ba a yin babban karatu a nan kauye sai an dangana da birni, wa muke da shi a birni? Iya ki daina sama ranki abin da ba za ki samu ba”.
Jikin Iya ya yi sanyi amma ba ta karaya ba. Ta ce, “Gaskiyarki Rahane, nan Takai gaba daya ban da Ado direba ma wa yake zuwa birni? Shima da me ya tsira ban da shaye-shaye? Sai dai jikina da mafarkina suna bani ke wata ce Rahane, don haka kada ki karaya, ki sa a ranki kema kina da burin karatun da nake sonki da shi. Babu ta yadda Ubangiji baya shirya al’amarinsa”.
Rahane ta gyada kai ta mike ta nufi tsakar gida ta daura alwala ta gabatar da sallar azuhur, sannan ta shiga madafi ta dauko robar abincinta a karkashin turmi. Tubani ne da mai da yaji Iya ta yi musu mai silbi, sai wucewa yake silif-silif! A makogwaronta.
Ta kammala ta share kejin zabbinta da na kajinta, ta share tsakar gidansu tas, ta debi ruwa ta yi wanka ta sanya kayan makarantar allo ta yamma da take zuwa, ta dau allonta ta yiwa Iya sallama ta tafi makaranta.
Wannan shine tsarin rayuwar Rahane a kullum.
Har kekensa take wankewa, sannan kullum ya dawo gida da gudu take taryo shi ta karbo kayan da ya zo dasu ta yi mishi shimfidar sallar magariba.
Tun baya kula har ya gane wata Yalwatin ce Allah ya bashi a matsayin diya. A hankali zuciyarshi ta soma kaunarta, da kanshi ya dauketa ya kaita makarantar firamare, sai dai mai nisa ce sosai da gidansu.
Don haka kullum yake goyata a bayan kekensa ya kaita, in sun tashi ta biyo kawayenta su dawo, don lokacin yana kasuwa.
Makarantar na karbar naira dari biyu da hamsin duk bayan watanni uku daga kowanne dalibi, haka yake kukkullawa ya biya, in bai bayar ba a koro ta, ta kwashe kwanaki a gida kamin ya samu ya biya.
Don lokacin Iya Bilki ta tsufa ainun ba ta sana’ar komai. Tun mutuwar Yalwati yau shekara tara kenan, Malam Rashidu ya ki yin aure, ba don komai ba sai don cewa ya san ba zai samu mai halin Yalwati ba da nagartarta.
Haka nan Iya Bilki ba ta fasa takura masa ba a kan ya yi auren, yana ta ba ta uziri. Don haka ba tare da yin shawara da shi ba ta nema mishi auren Zinaru kanwar Yalwati, uwa daya uba daya, da aurenta ya mutu tana da yara hudu tare da tsohon mijinta.
Shekarar Zinaru biyu tare da Malam Rashidu ta tada bala’in ba za ta zauna ba don talaucin ya isa. Ba haka ta saba a gidan tsohon mijinta ba. Dole ya sawwake mata tun da sauran mutunci, ya kuma roki Iya da ta yiwa Allah ta kyale shi da auren kowacce mace ba zai iya ba, sannan ba kowacce mace ba ce za ta iya zama da shi da talaucinsa irin Yalwati ba! Ta barshi ya raini diyar Yalwati kadai, ya inganta rayuwar ta, yayi mata aure in ta kai munzalin. Wannan ne kadai burin sa a rayuwa.
Bayan wannan ba shi da wani sauran buri, sai na gamawa da duniya lafiya, da cikawa da imani.
Iya ta share hawaye da habar zaninta saboda tuno Yalwati, da tijarar Zinaru, Allah daya gari bamban, kama da wane ba ta wane! Ita dama ta hada auren ne don tunanin Zinaru za ta yi halin Yalwati, ta rungumi diyar ‘yar’uwarta.
To ita Zinaru ma a tsayin shekaru biyu da ta yi a gidan, baiwa ta maida Rahane, suna ji suna gani basu isa suyi magana ba saboda tsoron bala’inta. Don haka rabuwarsu da ita, sai suka ji su sakayau.
Tun daga wannan lokaci Rashidu da mahaifiyarsa basu kara yin zancen ya yi aure ba. Kula da rayuwar Rahane ne a gabansu, da tarbiyyarta, lokacin shekarun Rahane goma sha daya tana firamare aji biyar.
Wata irin shakuwa ce tsakanin Rahane da kakarta, tamkar ta uwa da danta. Iya Bilki na da fada sosai, kuma ba ta daukar wargi. Duk wanda ya taba mata Rahane ko ya ya take da iyayensa ba ta kyalewa.
Idan samari suka aiko kiran Rahane da tabarya take korarsu, in har ka tsaya, ta rusa maka a baya. Wannan yasa duk samarin masu son Rahanen shakkarta, ba mai tare ta da zancen banza irin na sa’o’inta, don sun san karon da iyayensu za suyi da Iya Bilki.
Don haka Rahane ba ta da wani saurayi, amma sa’o’inta da yawa har an ba da su, wasu an sa musu rana. Iya kan ce da Rahane,
“Rabu da shashashai ki yi ta karatu, so nake ki zama malamar asibiti ki taimaki masu haihuwa a kauyen nan, kina dai ganin yadda duk auren wurin ya janyowa su Saude yoyon fitsari, ana ta fada a Radio a daina yiwa kananan yara aure amma basa ji”.
Shi kuwa Malam Rashidu ba shi da buri irin ya ga ya aurar da Rahane dai-dai wannan lokacin ga managarcin miji kamar sauran tsararrakinta, amma tunda ya lura Iya ba ta ko son zancen sai ya tsahirta. Daga baya Ado direba mai gidan dasu Malam Rashidu keciki ya daina karbar kudin hayarsa, sabida wani kuduri nasa na daban.
***
[12/24/2019, 17:56] Takori: Rahane ta shigo da kayan da babanta ya shigo dasu ta aje a tsakar gida, ta yi maza ta kawo mishi ruwan alwala ya karba ya ce, “Sannu Rahane kin ji? Allah ya yi miki albarka”. Ya karbi butar ya yi waje domin ya samu jam’i.
Su ma Rahane da Iya alwalar suka yi, Iya na sallah a daki Rahane na yi a tsakar gida. Bayan sun idar Rahane ta karasa gaban murhu tana cire itacen dake cin wuta tana zakulo garwashin tana kashewa da ruwa, sannan ta soma kwashewa Iya tuwon, tana sakawa kowa a kwanonsa.
Ta jiyo gyaran muryar babanta na kira a tsakar gida, da sauri ta mike tana amsawa ta zo ta durkusa
“Ga ni Baba”.
Ya zaro sauran kudin aljihunsa naira dari biyu da hamsin ya ba ta ya ce ta kai makaranta gobe ta ci gaba da zuwa makaranta.
Farin ciki ya kama Rahane ta ce, “Na gode Baba, Baba Allah ya kara buda maka”.
Ya ce, “Ameen Rahane, Ni dai fatana ki ci gaba da bada himma, kin ji?”
Ta ce, “Insha Allah Baba”.
Washegari Rahane ta koma makaranta, bayan Malam Rashidu ya sauke ta ya juya ya nufi kasuwa. Suna hanyar dawowa ita da Dije ‘yar ajinsu suka ji karar Akori-kurar Ado a bayansu, duk suka matsa gefe.
Ado ya rage gudun motar yana washe katon bakinsa wai shi a wurin shi murmushi yake. Ya ce,
“A’a, ‘yan makaranta an taso ne?” Jajayen idanuwanshi a kan Rahane.
Ko amsa mishi ba ta yi ba ta ci gaba da tafiyarta. Dije ce ta ce da shi, “Eh, mun taso”.
Ya ce, “To ku shigo in karasa daku”.
Dije ta ce, “A’a, ai mun kusa”.
Har yanzu idanunshi a kan Rahane ya ce, “Wai haka Rahane?”
Ko juyawa ba ta yi ba ta yi banza da shi. Bai ji haushi ba ya ci gaba da washe bakinsa ya ce,
“Tunda bakya magana a kan hanya Rahane, to ina nan zuwa da dare kin ji?”
Bai tsammaci amsarta ba daman, ya tada Akori-kurar sa ya yi gaba, ya kasa rufe bakin.
Iya na daki tana kadin auduga, Rahane ta yi sallama ta aje jakar makarantarta, ta fada jikin Iya Bilki tana fadin “Wash! Iya na gaji sosai”.
Iya ta rungumeta tana cewa, “Sannu ‘yar Iya, Allah ya nuna min lokacin da za ki fara yiwa mutane allura”.
Dariya ta yi ta ce, “Iya Baba fa ba zai barni in yi irin karatun nan da kike so ba, shi kullum maganarshi ta aure ce Iya. Ni kam duk abin da zai rabani da ke da gidan nan Iya bana son shi ko da karatun ne, kuma kin san ba a yin babban karatu a nan kauye sai an dangana da birni, wa muke da shi a birni? Iya ki daina sama ranki abin da ba za ki samu ba”.
Jikin Iya ya yi sanyi amma ba ta karaya ba. Ta ce, “Gaskiyarki Rahane, nan Takai gaba daya ban da Ado direba ma wa yake zuwa birni? Shima da me ya tsira ban da shaye-shaye? Sai dai jikina da mafarkina suna bani ke wata ce Rahane, don haka kada ki karaya, ki sa a ranki kema kina da burin karatun da nake sonki da shi. Babu ta yadda Ubangiji baya shirya al’amarinsa”.
Rahane ta gyada kai ta mike ta nufi tsakar gida ta daura alwala ta gabatar da sallar azuhur, sannan ta shiga madafi ta dauko robar abincinta a karkashin turmi. Tubani ne da mai da yaji Iya ta yi musu mai silbi, sai wucewa yake silif-silif! A makogwaronta.
Ta kammala ta share kejin zabbinta da na kajinta, ta share tsakar gidansu tas, ta debi ruwa ta yi wanka ta sanya kayan makarantar allo ta yamma da take zuwa, ta dau allonta ta yiwa Iya sallama ta tafi makaranta.
Wannan shine tsarin rayuwar Rahane a kullum.