Sashe 10
Rayuwar Rayhana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kasancewa ranar Lahadi ce, Dacta bai zuwa office don haka basu fito ba shi da Mami sai karfe goma na safe, cikin sassaukar shiga ta zaman gida. Mami doguwar riga ce kirar Kuwait ruwan toka a jikinta, ta kame jelunan kitsonta da ribom. Shi kuma Dacta shirt ce mara nauyi fara da shudin jeans a jikinsa.
Ibrahim suka tarar bisa tebir yana kalaci, shima ya yi wanka ya yi fes da shi cikin Hilfiger Jeans ruwan bula, gashin kansa da ya yiwa saisaye yana kwance bakikkirin da shi sai sheki yake. Ga turaren shi mai sanyin kamshi na tashi a hankali a falon.
A kujerar dake fuskantar shi Dacta da Mami suka zauna. Dacta ya dubi Mami ya ce, “Rayhanah ta karya ne?”
Ta ce, “Anya? Bari in dubo ta”. Ta mike.
Da ta shiga dakin gani ta yi kamar ba kowa, can ta jiyo shesshekar kukanta can a kusurwar gadon Jawahir.
Ta shiga ta tsugunna a gabanta ta kama hannunta ta ce, “Kuka Rayhanah? Me aka yi miki?”
Ta jata jikinta a hankali tana lallashinta. Dacta ma aje cokali ya yi ya nufo dakin don ya ga Mamin ta jima.
Shima durkuso ya yi a gabanta ya ce, “Mene ne Rayha? Me ya same ki?”
Cikin kuka ta ce, “Iya za ni”.
Ya ce, “Daina kuka Rayhanah, addu’a za ki dinga yiwa Iya a duk lokacin da kika tunata. Wanda ya riga ya mutu baya dawowa, sannan baya son kuka, addu’a yake bida.
Rayhanah kowa da kika gani yana yawo a doron kasa, wata rana za a wayi gari babu shi. Har mu din kuwa. Ba Iya kadai ba, duk jiran wa’adinmu muke. Duk sanda kika yi sallah ki karanta suratul Ikhlas kafa uku ki ce Allah ya kai mata ya fi ki dinga yi mata kuka. Addu’a take so kin ji”.
Ta daga kai. Ya ce, “Good! To taso muje ki ci abinci”.
Ya kamo hannunta har dining. Ai kuwa Ibraheem ya aje cokalinsa ya mike, don ba zai iya cin abinci tana wajen ba. She is ugly at all (mummuna ce), ga ciwuka ga dafaffiyar fatar kauye. Wannan abun haushi na Daddy da me ya yi kama?
Mami dake hadawa Rayhanah tea ta cira ido ta dube shi ta ce, “Ya ka tashi? Ka koshi ne?”
Tuni Daddy ya karance shi. Ya dauke fuska don baya son ganin ma inda yarinyar take kada ya yi amai, ya wuce yana cewa “Eh, Mami”.
Ta turawa Rahane kofin shayin, ta zuba plantain da dankali ta tura mata “Ci maza ki sha magani”.
Ta karba, amma sai ta dauko filet din da kofin ta zauna a kan marbles ta fara cin abinta.
Duk suka yi mata dariya, kuma basu ce da ita ta tashi ba. A wurin Rahane su suna kan kujera ita ma ta hau kujera, ai ya zama rashin kunya.
Da suka kammala Dacta ya bai wa Mami ‘master card’ dinsa na (First Bank) ya ce ko nawa ne ta cira ta sayawa Rahane sittiru da sauran kayan bukata.
Ta ce, “Ni wannan kan ma na fi damuwa da a wanke. Ba zai rasa dandruff da lices ba (amosani da kwarkwata). Dubi yadda take ta sosa shi”.
Haka tasa Rahane a gaba suka tafi saloon din, ita ke jan motar. Ai kuwa kwarkwata ba a magana. Haka ta yi ta biyo kumfar magani na musamman ana fidda ita.
Sai da suka tabbatar babu ko daya sannan suka gyara mata gashin. Ba ta da wata suma mai yawa, sumarta ba ta fi a kama a ribbon ba, mai karfi sosai ta asalin Kanawa.
Daga nan shagon (Well-Care) ta shiga ta yi mata sayayyar kayan sanyawa masu kyau da tsada. Dogayen riguna ne sai siket da riga, atamfa da les kuma ta ba da dinki a (Diallo) inda ake wa su Abida.
Basu shigo gida ba sai bayan azahar. Tuni su Abida sun dawo har sunyi wanka, sai yanzu Rahane ta ga wanda yake kawo abinci ya aza a tebir. Wani kabila ne sanye da Apron fes da shi kamar ma’aikaci. Ta ji Azizah na ce masa Yohan.
Da gudu Jawahir ta rungumota ta zame dan kwalinta ta ce, “Rayha kin yi kyau, yau tunda na je makaranta nake tunaninki. Don Allah Mami a kai Rayha makarantarmu”.
Mami ta ce, “Ku wuce ku ci abinci ko sai Malam Umar ya zo yana jiranku?”
Jawahir ta makale hannun Rahane suka zauna tare, ta ce, “In ce ko kin cire ‘Aid’ din sanda za a yi wankin kan?”
Ta ce, “Eh, na cire”.
Abida sai cin magani take, ta yi tsaki ta debi abin da za ta iya ci ta yi daki, don ba za ta iya cin abinci gaban wannan kazamar yarinyar ba. Azizah cinyar Rahane ta dare tana ta Alifun Ba’un da A,B.C,D tana da son mutane.
Haushi bai kashe Abida ba sai da ta ga an karo musu gado, wato na Rahane ne. Ta zauna tana ta huci, da ta tuna kashedin babanta kuma sai ta fashe da kuka, don ta lura ba yadda za ta yi, kuma da gaske tare Daddy ke nufin suyi rayuwa.
Karfe hudu dai-dai Malam Umar ya zo. Yana koyar dasu kira’a ne da Tajweed, sannan suyi lesson a boko. Idan yana kwararo kira’a sai ka ce Ahmad Sulyman, haka idan yana baiwa kowanne harafin Alkur’ani hukuncinsa, kamar marigayi (Malam Datti Ahmad Galadanci) Allah ya yi masa rahama.
Rahane na zaune gefe tana sauraron wannan malami, ta ce a ranta ashe mu a Allo shirme muke yi. Ya ja aya ya kuma nuna Abida da ya lura hankalinta baya tare da ita tana ta sokawa Rahane tsinke, ya ce, “Abida, wane hukunci ne da wannan ta’areef?’
Ta zabura ta ce, “Eye? Na’am?”
Ya sake maimaitawa. Ta yi tsit! Ya kuwa daddage ya tsula mata dorinar dake hannunsa, bulalar ta shigeta sosai, ta zabura ta sa kuka.
Ya ce, “Ko ki rufe min baki ko in kara shauda miki”.
Ta toshe bakin da karfi tana kuka.
Ya ce, “Tun dazu ina lura dake babu karatun da kike sai tsokana, ko tausayin yarinyar nan ba kya ji. Dubi raunin dake jikinta amma kike son huda mata jiki”.
Da mamaki Jawahir ta dubi Abida, don da hankalinta baya kansu. Ya ci gaba da cewa, “To zan gayawa Dacta, don ke na lura fitinanniya ce”.
Tana kuka ta ce, “Don Allah Malam ka yi hakuri kada ka fadawa Daddy na daina”.
Ya ce, “To kin yi na karshe”.
Da haka karatun ya tashi.
[12/24/2019, 17:56] Takori: A rayuwar Ibraheem, bai taba damuwa da wani abu bayan iyayensa da karatunsa ba kamar RAYHANAH! Kankanuwar yarinyar da ko kirgar dangi bata fara ba, bata kuma da wani abu attractive da zai dau hankalin namiji ta fannin sura.......bai yarda da kansa ba, don haka ya dauki duk wani motsin da zuciyarsa da gangar jikinsa ke yi a kanta da KARYA........!
Jawahir ta Khalipha su suka taimakawa Rayha ta wanke kashin da Abida ta yaba mata, sannan ta yi wanka ta koma ta kudundune a bargonta ba ta ce komai ba. Sai ajiyar rai take.
Khalipha ya dora hannunsa a kan goshinta, zafi rau! Ya ce, “Tun yaushe kika fara ciwon kai Rayha?’
A sanyaye ta ce, “Tun jiya”.
Ya umarci Jawahir ta kawo ruwa da panadol. Ya ba ta da kansa ta koma ta kwanta.
Abida na gefe tana ta kuka domin ta daku a hannun Khalipha ba kadan ba. Sai dai ko kadan hakan bai sa zuciyarta ta russuna ba daga kiyayyar da take yiwa Rayha. Zuciyarta ce ma ta kara tauri da kangarewa, don yarda da ta kara yi Rahane ta zame mata karfen-kafa.
Daddy ya daina shiri da ita saboda ita, yau ga Yaya Khalipha dan’uwanta da ba ta hada soyayyarshi da ta kowa a zuciyarta ya yi mata dukan kawo wuka a kan RAYHANAH!
Khalipha ya dago idonshi jajir da bacin ran da har zuwa lokacin bai ji ya ragu ba, duk da dukan da ya yiwa Abida.
Ya dube ta sosai tana ta kuka ya ce, “I’m warning you Abidah.... don’t repeat it! Don’t repeat it!! Don’t repeat it!!!”
Ta ce, “To Yaya Khalipha”. Ya mike ya fita ya ja musu kofar.
****
A yau duk gidan shiri suke yi domin halartar bikin kammala karatun su Ibrahim, karshen kure adaka ‘ya’yan Dr. Mansur sunyi. Duka sanye suke cikin English wears kowanne da design din sa, sunyi kyau kwarai. Aziza samfurin ‘george’ Abida da Rayha ‘Mclaren’, Jawahid kuma H&M ne duka riguna da wando domin zama da madaukin kanwa yau da gobe tilas ya koyar da Rahane saka wando. Don su a wurin su (casual wear) ne da babu inda bazasu iya shiga dashi ba. Dr. Mansur baya hana su shida kansa in ya fita waje yake sayo musu saidai ya kudure ya kusan dakatar da hakan da zarar sun shiga sakandire.
Kalar kayan kowanne daban, amma duka babu wadda ba yi kyau ba kamar ka lashe. Kai ka ce irin yaran nan ne dake rayuwa a Honolulu.
Rahane ta kara da farin hijabi, wanda ya sauka a kan kafadunta. A zahiri duka su Abida sun fita kyau, sun fita haske. Amma idan ka dubi Rahane a wannan lokacin sai ka kara marmarin maimaitawa, saboda kalar fatar jikinta baka mai duhu amma mai sulbi kamar Somali, da dirin jikinta da ya soma bayyana da wata irin kamala da nutsuwa hadi da kwarijini bayyananne daga indallahi.
Ibrahim suka tarar bisa tebir yana kalaci, shima ya yi wanka ya yi fes da shi cikin Hilfiger Jeans ruwan bula, gashin kansa da ya yiwa saisaye yana kwance bakikkirin da shi sai sheki yake. Ga turaren shi mai sanyin kamshi na tashi a hankali a falon.
A kujerar dake fuskantar shi Dacta da Mami suka zauna. Dacta ya dubi Mami ya ce, “Rayhanah ta karya ne?”
Ta ce, “Anya? Bari in dubo ta”. Ta mike.
Da ta shiga dakin gani ta yi kamar ba kowa, can ta jiyo shesshekar kukanta can a kusurwar gadon Jawahir.
Ta shiga ta tsugunna a gabanta ta kama hannunta ta ce, “Kuka Rayhanah? Me aka yi miki?”
Ta jata jikinta a hankali tana lallashinta. Dacta ma aje cokali ya yi ya nufo dakin don ya ga Mamin ta jima.
Shima durkuso ya yi a gabanta ya ce, “Mene ne Rayha? Me ya same ki?”
Cikin kuka ta ce, “Iya za ni”.
Ya ce, “Daina kuka Rayhanah, addu’a za ki dinga yiwa Iya a duk lokacin da kika tunata. Wanda ya riga ya mutu baya dawowa, sannan baya son kuka, addu’a yake bida.
Rayhanah kowa da kika gani yana yawo a doron kasa, wata rana za a wayi gari babu shi. Har mu din kuwa. Ba Iya kadai ba, duk jiran wa’adinmu muke. Duk sanda kika yi sallah ki karanta suratul Ikhlas kafa uku ki ce Allah ya kai mata ya fi ki dinga yi mata kuka. Addu’a take so kin ji”.
Ta daga kai. Ya ce, “Good! To taso muje ki ci abinci”.
Ya kamo hannunta har dining. Ai kuwa Ibraheem ya aje cokalinsa ya mike, don ba zai iya cin abinci tana wajen ba. She is ugly at all (mummuna ce), ga ciwuka ga dafaffiyar fatar kauye. Wannan abun haushi na Daddy da me ya yi kama?
Mami dake hadawa Rayhanah tea ta cira ido ta dube shi ta ce, “Ya ka tashi? Ka koshi ne?”
Tuni Daddy ya karance shi. Ya dauke fuska don baya son ganin ma inda yarinyar take kada ya yi amai, ya wuce yana cewa “Eh, Mami”.
Ta turawa Rahane kofin shayin, ta zuba plantain da dankali ta tura mata “Ci maza ki sha magani”.
Ta karba, amma sai ta dauko filet din da kofin ta zauna a kan marbles ta fara cin abinta.
Duk suka yi mata dariya, kuma basu ce da ita ta tashi ba. A wurin Rahane su suna kan kujera ita ma ta hau kujera, ai ya zama rashin kunya.
Da suka kammala Dacta ya bai wa Mami ‘master card’ dinsa na (First Bank) ya ce ko nawa ne ta cira ta sayawa Rahane sittiru da sauran kayan bukata.
Ta ce, “Ni wannan kan ma na fi damuwa da a wanke. Ba zai rasa dandruff da lices ba (amosani da kwarkwata). Dubi yadda take ta sosa shi”.
Haka tasa Rahane a gaba suka tafi saloon din, ita ke jan motar. Ai kuwa kwarkwata ba a magana. Haka ta yi ta biyo kumfar magani na musamman ana fidda ita.
Sai da suka tabbatar babu ko daya sannan suka gyara mata gashin. Ba ta da wata suma mai yawa, sumarta ba ta fi a kama a ribbon ba, mai karfi sosai ta asalin Kanawa.
Daga nan shagon (Well-Care) ta shiga ta yi mata sayayyar kayan sanyawa masu kyau da tsada. Dogayen riguna ne sai siket da riga, atamfa da les kuma ta ba da dinki a (Diallo) inda ake wa su Abida.
Basu shigo gida ba sai bayan azahar. Tuni su Abida sun dawo har sunyi wanka, sai yanzu Rahane ta ga wanda yake kawo abinci ya aza a tebir. Wani kabila ne sanye da Apron fes da shi kamar ma’aikaci. Ta ji Azizah na ce masa Yohan.
Da gudu Jawahir ta rungumota ta zame dan kwalinta ta ce, “Rayha kin yi kyau, yau tunda na je makaranta nake tunaninki. Don Allah Mami a kai Rayha makarantarmu”.
Mami ta ce, “Ku wuce ku ci abinci ko sai Malam Umar ya zo yana jiranku?”
Jawahir ta makale hannun Rahane suka zauna tare, ta ce, “In ce ko kin cire ‘Aid’ din sanda za a yi wankin kan?”
Ta ce, “Eh, na cire”.
Abida sai cin magani take, ta yi tsaki ta debi abin da za ta iya ci ta yi daki, don ba za ta iya cin abinci gaban wannan kazamar yarinyar ba. Azizah cinyar Rahane ta dare tana ta Alifun Ba’un da A,B.C,D tana da son mutane.
Haushi bai kashe Abida ba sai da ta ga an karo musu gado, wato na Rahane ne. Ta zauna tana ta huci, da ta tuna kashedin babanta kuma sai ta fashe da kuka, don ta lura ba yadda za ta yi, kuma da gaske tare Daddy ke nufin suyi rayuwa.
Karfe hudu dai-dai Malam Umar ya zo. Yana koyar dasu kira’a ne da Tajweed, sannan suyi lesson a boko. Idan yana kwararo kira’a sai ka ce Ahmad Sulyman, haka idan yana baiwa kowanne harafin Alkur’ani hukuncinsa, kamar marigayi (Malam Datti Ahmad Galadanci) Allah ya yi masa rahama.
Rahane na zaune gefe tana sauraron wannan malami, ta ce a ranta ashe mu a Allo shirme muke yi. Ya ja aya ya kuma nuna Abida da ya lura hankalinta baya tare da ita tana ta sokawa Rahane tsinke, ya ce, “Abida, wane hukunci ne da wannan ta’areef?’
Ta zabura ta ce, “Eye? Na’am?”
Ya sake maimaitawa. Ta yi tsit! Ya kuwa daddage ya tsula mata dorinar dake hannunsa, bulalar ta shigeta sosai, ta zabura ta sa kuka.
Ya ce, “Ko ki rufe min baki ko in kara shauda miki”.
Ta toshe bakin da karfi tana kuka.
Ya ce, “Tun dazu ina lura dake babu karatun da kike sai tsokana, ko tausayin yarinyar nan ba kya ji. Dubi raunin dake jikinta amma kike son huda mata jiki”.
Da mamaki Jawahir ta dubi Abida, don da hankalinta baya kansu. Ya ci gaba da cewa, “To zan gayawa Dacta, don ke na lura fitinanniya ce”.
Tana kuka ta ce, “Don Allah Malam ka yi hakuri kada ka fadawa Daddy na daina”.
Ya ce, “To kin yi na karshe”.
Da haka karatun ya tashi.
[12/24/2019, 17:56] Takori: A rayuwar Ibraheem, bai taba damuwa da wani abu bayan iyayensa da karatunsa ba kamar RAYHANAH! Kankanuwar yarinyar da ko kirgar dangi bata fara ba, bata kuma da wani abu attractive da zai dau hankalin namiji ta fannin sura.......bai yarda da kansa ba, don haka ya dauki duk wani motsin da zuciyarsa da gangar jikinsa ke yi a kanta da KARYA........!
Jawahir ta Khalipha su suka taimakawa Rayha ta wanke kashin da Abida ta yaba mata, sannan ta yi wanka ta koma ta kudundune a bargonta ba ta ce komai ba. Sai ajiyar rai take.
Khalipha ya dora hannunsa a kan goshinta, zafi rau! Ya ce, “Tun yaushe kika fara ciwon kai Rayha?’
A sanyaye ta ce, “Tun jiya”.
Ya umarci Jawahir ta kawo ruwa da panadol. Ya ba ta da kansa ta koma ta kwanta.
Abida na gefe tana ta kuka domin ta daku a hannun Khalipha ba kadan ba. Sai dai ko kadan hakan bai sa zuciyarta ta russuna ba daga kiyayyar da take yiwa Rayha. Zuciyarta ce ma ta kara tauri da kangarewa, don yarda da ta kara yi Rahane ta zame mata karfen-kafa.
Daddy ya daina shiri da ita saboda ita, yau ga Yaya Khalipha dan’uwanta da ba ta hada soyayyarshi da ta kowa a zuciyarta ya yi mata dukan kawo wuka a kan RAYHANAH!
Khalipha ya dago idonshi jajir da bacin ran da har zuwa lokacin bai ji ya ragu ba, duk da dukan da ya yiwa Abida.
Ya dube ta sosai tana ta kuka ya ce, “I’m warning you Abidah.... don’t repeat it! Don’t repeat it!! Don’t repeat it!!!”
Ta ce, “To Yaya Khalipha”. Ya mike ya fita ya ja musu kofar.
****
A yau duk gidan shiri suke yi domin halartar bikin kammala karatun su Ibrahim, karshen kure adaka ‘ya’yan Dr. Mansur sunyi. Duka sanye suke cikin English wears kowanne da design din sa, sunyi kyau kwarai. Aziza samfurin ‘george’ Abida da Rayha ‘Mclaren’, Jawahid kuma H&M ne duka riguna da wando domin zama da madaukin kanwa yau da gobe tilas ya koyar da Rahane saka wando. Don su a wurin su (casual wear) ne da babu inda bazasu iya shiga dashi ba. Dr. Mansur baya hana su shida kansa in ya fita waje yake sayo musu saidai ya kudure ya kusan dakatar da hakan da zarar sun shiga sakandire.
Kalar kayan kowanne daban, amma duka babu wadda ba yi kyau ba kamar ka lashe. Kai ka ce irin yaran nan ne dake rayuwa a Honolulu.
Rahane ta kara da farin hijabi, wanda ya sauka a kan kafadunta. A zahiri duka su Abida sun fita kyau, sun fita haske. Amma idan ka dubi Rahane a wannan lokacin sai ka kara marmarin maimaitawa, saboda kalar fatar jikinta baka mai duhu amma mai sulbi kamar Somali, da dirin jikinta da ya soma bayyana da wata irin kamala da nutsuwa hadi da kwarijini bayyananne daga indallahi.