Sashe 20
Rayuwar Rayhana Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Khalipha na kwance cikin leather seat din falonsa bakake, a gabansa ash-tray ne na silver wanda ke cike taf da guntattakin Marlboro, a wannan lokacin ma abin da yake ta yi kenan, wato gajimare da hayaki.
Ya yi baki ya bar kasumba ta cika masa fuska, wannan kwantaccen gashin nasa duk ya kanannade saboda rashin gyara. Falon kaca-kaca ga kuma kura da kayan wuta suka yi, don ya hana yaronsa Jibril shigo masa daki balle ya gyara masa sai idan shi ya kira shi a waya ya sayo masa abinci.
Kararrawar shigowa falon ta yi kara, ta yi ta sake yi yana kwance bai motsa ba. A zatonsa Jibril ne alhalin ya san ya hana shi zuwa inda yake in ba shi ya kira shi ba. Farar singilet ce a jikinshi da dogon bakin wandon DKNY.
A fusace ya mike ya bude don ya yi masa marin da uwarsa bata taba yi masa ba. Amma sai ya yi tozali da tashi uwar wacce ko cikin mafarkinsa bai zaci ganinta a nan ba.
Kallon shi kawai Mami ke yi, bayan mintuna uku ta bi gefenshi ta shige falon ba tare da ya bata damar hakan ba.
Sai ta fara kiran ‘Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un....... smoking ABDALLAH???”
Sai ta zube cikin kujera ta saka mishi kuka.
Jikinsa ya yi bala’in yin sanyi, ya zube a gabanta ya kwantar da kai a cinyoyinta cikin matsanancin tashin hankali; mahaifiyarsa na zub da hawaye a dalilinsa.
Ta kara dago ido ta dube shi, “Ashe addicted ka zama? Shi yasa baka nemanmu? Abdallah tun yaushe kake shaye-shaye ban sani ba? Me ya kawo ni ganin wannan bakin cikin? Me ya kawo ni, ni Asma’u???”
Sai ta mike za ta fice idanunta jage-jage da hawaye. Da hanzarin gaske ya cimmata ya rungume kafafunta.
“Wallahi Mami ki yarda dani, ban taba shan abin da zai fitar dani daga hankalina ba. Mami damuwa ce bana cikin sukunin da zan iya sarrafa kaina. Ina sha ne kurum don ta rage min damuwa. Marlboro ce kawai, wallahi Mami idan na taba shan wani abu bayan ita, Allah ya yi miki sakayya a kan tarbiyyar da kika bani”.
Ta tsaya da kukan, ta shiga nazarin falon baki dayansa cikin bakin-ciki marar misali, ta ce, “Mene ne haka? Me zan gani haka? Kazami kuma ka koma? Me kake yi yau a gida ranar aiki baka je office ba?”
Bai bata amsa ba, don bai san me zai ce mata ba.
Ta girgiza kai ta ce “ai Shi kenan, ni zan tafi, dama na zo in duba lafiyarka ne. Don na san haka kawai ba za ka ki gaishemu ba. To na gani lafiyarka kalau bamu isa bane kawai mu ji damuwar taka ka gwammace ka lalata rayuwarka”.
Da hanzari ta fita, bata barshi ya yi wani furuci ba. Kayan dake jikinsa kuwa ba za su barshi ya bita ba. Ko hutawa bata yi ba, ko ruwa ba ta sha ba ta dauko hanyar Kano.
Allah ne kawai ya kawo Mami gida, amma ba nutsuwar zuciya ba. Wai Dan da ta haifa ne yake shan taba bata taba sani ba. Ko tun tsahon yaushe yake sha?
Duk tsantseninta a kan ‘ya’yanta, duk jansu da take a jikinta don su zama abokan rayuwarta, a yau Khalipha ya nuna mata aikin banza take, ya nuna mata yana da wata damuwar da ba ta isa ya gaya mata ba, ya gwammace ya mutu a cikinta.
Da asubahin ranar ta ji Malam Dahiru ya bude get, ta daga labulen dakinta tana kallon shigowar motarshi, wannan ya tabbatar mata tafiyar dare yayo, sai ta ji tausayi ya tsirga a zuciyarta.
Har ya fito daga motar ya rufe ya ratayo bakar jakarshi ya shigo reception tana kallon shi. Ta koma bakin gadonta ta zauna, ko minti biyu ba ta yi da zama ba ta tsinkayi sassanyar sallamar sa a kofar dakinta. Babu kuzari sam a jikinta ta ce,
“Yes, come in”.
A yadda ya shigo din cikin kayan da ta baro shi ne, bakar rigar sanyi kawai ya dora a kai wadda ta iso har gwiwarsa, bakin glass da bakin cover takalmi.
Sai ta nuna mishi toilet dinta, tana daga zaune “Go take a wudu’ (alwala), a brush, a shave and a shower, then come to me….”. (Shiga ka yi wanka, ka yi brush, ka yi alwala, ka yi aski sannan ka zo gareni).
Maimakon ya shiga nata toilet din sai ya juya nashi dakin ya bi umarninta.
Ya idar da sallah ya yi addu’o’i masu yawa, yana rokon Allah yasa Mami ta fahimci ba shi ya dorawa kanshi damuwar ba, Allah ne ya dora mishi.
Sannan ba shi da karfin zuciyar da zai sarrafata ko ya boyeta. Su kuma ba za su iya yi masa maganinta a wannan lokacin ba. Don haka ba zai iya fada mata ba, don fadar bazata yi wani amfani ba.
Mami ta ji shiru-shiru Khalipha bai fito ba. Ta kasa hakuri ta biyo bayanshi har dakin nasu.
A lokacin shi yana shirya abin da zai gaya mata ne don ba zai iya gaya mata gaskiya yanzu ba. Ya san Mami da boko kamar Ibraheem, cewa za suyi Rayhanah ba ta isa aure ba ko su kushe zabin nasa. Ko suce ‘child abuse’.
Don haka tuni ya tattara abin da zai gaya mata. Dai-dai lokacin da ta zauna gefen ‘sofa’ dinsa. Ya shafa addu’a ya ce, “Mami kin zo lafiya?” Ta ce, “Da ban zo lafiyar ba za ka ganni ne har dakinka da kafafuna eyi?”
Ya yi murmushi, “Mami kin tayar min da hankali Allah, da baki tsaya kin ji uzirina ba balle damuwar dake damun nawa. Mami in kika yi fushi dani ina zan sa raina? Jahannama fa Mami, babu ni babu jin kamshin Aljannah. Mami don Allah kar ki kara yin fushi dani, kin ji Mami?”
Jikinta ya yi sanyi kalau, ta ce, “Mene ne ke damun naka?”
Ya ce, “Mami SOYAYYAH!”
Sai ta yi murmushi ta ce, “Alhakin Hibba ne, wace mai tsautsayin ce again?”
Ya ce, “Mami ban sameta ba, an kasa ni”.
Ta kara yin murmushin ta ce, “Ba ita kadai ce diya mace a duniya ba, Allah yasa hakan ya zama mafi alkhairi. Wani zubin in Allah ya tsara abu, sai ka ga na gaban ya fiye maka amfani. Ni tuni ai na yi maka mata Khalipha, jira nake ka zamo settled tukunna kafin in gabatar maka da zancen”.
Cikin Halifa ya karta ya bala’in kadawa. Da sauri ya ce, “Um-um Mami, bar zuciya da abin da take so. Har yau din dai da nake gaya miki ban fidda rai da samunta ba. Wani sanadi zai iya zuwa idan har matata ce Allah ya bani in aureta. Tunda an ce matar mutum kabarinsa”.
“Ya ya sunanta? A ina take Dattijo? Su waye iyayenta?”
Ya ce, “Mami tunda a yanzun bani da damar aurenta sanin wadannan amsoshin ba zai amfaneki da komai ba”.
Cikin rashin damuwa da lamarin ta mike tana fadin, “Toh! Allah ya maganta maka, ni na dauka wani muhimmin al’amari ne, zancen Radhiyyah kuwa na baka sati har biyu ka yi tunani a kai”.
A cunkushe da zancen ya ce, “Radhiyyah kuma? Gaskiya Mami bana son ki sa ranki ga abin da ba zai yiwu ba. Matakin iliminta ya wuce wanda nake so a macen da zan aura kafin in aure ta. Nafison duk wani ilmi da mace zata yi bayan sakandire tayi shi a gida na. Kuma da kadan na girmeta, in zan iya tunawa shekara uku na bata.
Haba Mami, ai an dena irin wannan hadin auren yanzu a kauye ma ba a birni ba, gaskiya ta min tsufa.
A perception dinki ban zaci akwai irin wannan tunanin ba, na abubuwan da aka yi a can wani karni can da ya shude. Na soyayyar ma yaya aka kare da shi balle na hadi?
Ki barni kawai in na samu wadda za ta maye min gurbinta da kaina zan gaya miki. Amma don Allah Mami kada ki kara daga maganar nan, kada zumuncin da ke tsakaninku da Mamanta ya lalace a kan abin da ba zai yiwu ba”.
Cikin mamaki Mami ta ce, “Ni kake cewa haka Dattijo?”
Da sauri ya gyara kuskurensa da cewa, “Ba nufina baki da iko a kai bane Mami, kawai ina gaya miki abin da zuciyata ke gaya min a kan maganar. Ki yi hakuri idan kalamaina sun bata miki rai, I’m sorry Mamee! Ki yi hakuri don Allah”.
Ta yi ajiyar zuciya sannan ta fita. Allah kadai ya san abin da take sakawa da warwarewa a zuciyar nan tata. Mami na son ‘ya’yanta matuka, tana kishinsu irin kishin nan mara amfani, wanda ya kimsa mata tunanin cewa da akidar cewa ba za ta bari su auri wadanda suke mutuwar so ba, sai wadanda ke son su, don kar su rabata da su.
Irin ‘yan’uwansu su Hibbah, Nabila da Radhiyyah diyar aminiyarta Dacta Halima wadda ta ki auren minister saboda mahaukaciyar soyayyar da take yiwa Khalipha.
Mami na da wannan kudurin cikin ranta tuni, wanda kuma take da yakinin ko za ta yi yawo tsirara ne sai ta cika shi. Saboda masifar son da take wa ‘ya’yanta.
****
Ya yi baki ya bar kasumba ta cika masa fuska, wannan kwantaccen gashin nasa duk ya kanannade saboda rashin gyara. Falon kaca-kaca ga kuma kura da kayan wuta suka yi, don ya hana yaronsa Jibril shigo masa daki balle ya gyara masa sai idan shi ya kira shi a waya ya sayo masa abinci.
Kararrawar shigowa falon ta yi kara, ta yi ta sake yi yana kwance bai motsa ba. A zatonsa Jibril ne alhalin ya san ya hana shi zuwa inda yake in ba shi ya kira shi ba. Farar singilet ce a jikinshi da dogon bakin wandon DKNY.
A fusace ya mike ya bude don ya yi masa marin da uwarsa bata taba yi masa ba. Amma sai ya yi tozali da tashi uwar wacce ko cikin mafarkinsa bai zaci ganinta a nan ba.
Kallon shi kawai Mami ke yi, bayan mintuna uku ta bi gefenshi ta shige falon ba tare da ya bata damar hakan ba.
Sai ta fara kiran ‘Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un....... smoking ABDALLAH???”
Sai ta zube cikin kujera ta saka mishi kuka.
Jikinsa ya yi bala’in yin sanyi, ya zube a gabanta ya kwantar da kai a cinyoyinta cikin matsanancin tashin hankali; mahaifiyarsa na zub da hawaye a dalilinsa.
Ta kara dago ido ta dube shi, “Ashe addicted ka zama? Shi yasa baka nemanmu? Abdallah tun yaushe kake shaye-shaye ban sani ba? Me ya kawo ni ganin wannan bakin cikin? Me ya kawo ni, ni Asma’u???”
Sai ta mike za ta fice idanunta jage-jage da hawaye. Da hanzarin gaske ya cimmata ya rungume kafafunta.
“Wallahi Mami ki yarda dani, ban taba shan abin da zai fitar dani daga hankalina ba. Mami damuwa ce bana cikin sukunin da zan iya sarrafa kaina. Ina sha ne kurum don ta rage min damuwa. Marlboro ce kawai, wallahi Mami idan na taba shan wani abu bayan ita, Allah ya yi miki sakayya a kan tarbiyyar da kika bani”.
Ta tsaya da kukan, ta shiga nazarin falon baki dayansa cikin bakin-ciki marar misali, ta ce, “Mene ne haka? Me zan gani haka? Kazami kuma ka koma? Me kake yi yau a gida ranar aiki baka je office ba?”
Bai bata amsa ba, don bai san me zai ce mata ba.
Ta girgiza kai ta ce “ai Shi kenan, ni zan tafi, dama na zo in duba lafiyarka ne. Don na san haka kawai ba za ka ki gaishemu ba. To na gani lafiyarka kalau bamu isa bane kawai mu ji damuwar taka ka gwammace ka lalata rayuwarka”.
Da hanzari ta fita, bata barshi ya yi wani furuci ba. Kayan dake jikinsa kuwa ba za su barshi ya bita ba. Ko hutawa bata yi ba, ko ruwa ba ta sha ba ta dauko hanyar Kano.
Allah ne kawai ya kawo Mami gida, amma ba nutsuwar zuciya ba. Wai Dan da ta haifa ne yake shan taba bata taba sani ba. Ko tun tsahon yaushe yake sha?
Duk tsantseninta a kan ‘ya’yanta, duk jansu da take a jikinta don su zama abokan rayuwarta, a yau Khalipha ya nuna mata aikin banza take, ya nuna mata yana da wata damuwar da ba ta isa ya gaya mata ba, ya gwammace ya mutu a cikinta.
Da asubahin ranar ta ji Malam Dahiru ya bude get, ta daga labulen dakinta tana kallon shigowar motarshi, wannan ya tabbatar mata tafiyar dare yayo, sai ta ji tausayi ya tsirga a zuciyarta.
Har ya fito daga motar ya rufe ya ratayo bakar jakarshi ya shigo reception tana kallon shi. Ta koma bakin gadonta ta zauna, ko minti biyu ba ta yi da zama ba ta tsinkayi sassanyar sallamar sa a kofar dakinta. Babu kuzari sam a jikinta ta ce,
“Yes, come in”.
A yadda ya shigo din cikin kayan da ta baro shi ne, bakar rigar sanyi kawai ya dora a kai wadda ta iso har gwiwarsa, bakin glass da bakin cover takalmi.
Sai ta nuna mishi toilet dinta, tana daga zaune “Go take a wudu’ (alwala), a brush, a shave and a shower, then come to me….”. (Shiga ka yi wanka, ka yi brush, ka yi alwala, ka yi aski sannan ka zo gareni).
Maimakon ya shiga nata toilet din sai ya juya nashi dakin ya bi umarninta.
Ya idar da sallah ya yi addu’o’i masu yawa, yana rokon Allah yasa Mami ta fahimci ba shi ya dorawa kanshi damuwar ba, Allah ne ya dora mishi.
Sannan ba shi da karfin zuciyar da zai sarrafata ko ya boyeta. Su kuma ba za su iya yi masa maganinta a wannan lokacin ba. Don haka ba zai iya fada mata ba, don fadar bazata yi wani amfani ba.
Mami ta ji shiru-shiru Khalipha bai fito ba. Ta kasa hakuri ta biyo bayanshi har dakin nasu.
A lokacin shi yana shirya abin da zai gaya mata ne don ba zai iya gaya mata gaskiya yanzu ba. Ya san Mami da boko kamar Ibraheem, cewa za suyi Rayhanah ba ta isa aure ba ko su kushe zabin nasa. Ko suce ‘child abuse’.
Don haka tuni ya tattara abin da zai gaya mata. Dai-dai lokacin da ta zauna gefen ‘sofa’ dinsa. Ya shafa addu’a ya ce, “Mami kin zo lafiya?” Ta ce, “Da ban zo lafiyar ba za ka ganni ne har dakinka da kafafuna eyi?”
Ya yi murmushi, “Mami kin tayar min da hankali Allah, da baki tsaya kin ji uzirina ba balle damuwar dake damun nawa. Mami in kika yi fushi dani ina zan sa raina? Jahannama fa Mami, babu ni babu jin kamshin Aljannah. Mami don Allah kar ki kara yin fushi dani, kin ji Mami?”
Jikinta ya yi sanyi kalau, ta ce, “Mene ne ke damun naka?”
Ya ce, “Mami SOYAYYAH!”
Sai ta yi murmushi ta ce, “Alhakin Hibba ne, wace mai tsautsayin ce again?”
Ya ce, “Mami ban sameta ba, an kasa ni”.
Ta kara yin murmushin ta ce, “Ba ita kadai ce diya mace a duniya ba, Allah yasa hakan ya zama mafi alkhairi. Wani zubin in Allah ya tsara abu, sai ka ga na gaban ya fiye maka amfani. Ni tuni ai na yi maka mata Khalipha, jira nake ka zamo settled tukunna kafin in gabatar maka da zancen”.
Cikin Halifa ya karta ya bala’in kadawa. Da sauri ya ce, “Um-um Mami, bar zuciya da abin da take so. Har yau din dai da nake gaya miki ban fidda rai da samunta ba. Wani sanadi zai iya zuwa idan har matata ce Allah ya bani in aureta. Tunda an ce matar mutum kabarinsa”.
“Ya ya sunanta? A ina take Dattijo? Su waye iyayenta?”
Ya ce, “Mami tunda a yanzun bani da damar aurenta sanin wadannan amsoshin ba zai amfaneki da komai ba”.
Cikin rashin damuwa da lamarin ta mike tana fadin, “Toh! Allah ya maganta maka, ni na dauka wani muhimmin al’amari ne, zancen Radhiyyah kuwa na baka sati har biyu ka yi tunani a kai”.
A cunkushe da zancen ya ce, “Radhiyyah kuma? Gaskiya Mami bana son ki sa ranki ga abin da ba zai yiwu ba. Matakin iliminta ya wuce wanda nake so a macen da zan aura kafin in aure ta. Nafison duk wani ilmi da mace zata yi bayan sakandire tayi shi a gida na. Kuma da kadan na girmeta, in zan iya tunawa shekara uku na bata.
Haba Mami, ai an dena irin wannan hadin auren yanzu a kauye ma ba a birni ba, gaskiya ta min tsufa.
A perception dinki ban zaci akwai irin wannan tunanin ba, na abubuwan da aka yi a can wani karni can da ya shude. Na soyayyar ma yaya aka kare da shi balle na hadi?
Ki barni kawai in na samu wadda za ta maye min gurbinta da kaina zan gaya miki. Amma don Allah Mami kada ki kara daga maganar nan, kada zumuncin da ke tsakaninku da Mamanta ya lalace a kan abin da ba zai yiwu ba”.
Cikin mamaki Mami ta ce, “Ni kake cewa haka Dattijo?”
Da sauri ya gyara kuskurensa da cewa, “Ba nufina baki da iko a kai bane Mami, kawai ina gaya miki abin da zuciyata ke gaya min a kan maganar. Ki yi hakuri idan kalamaina sun bata miki rai, I’m sorry Mamee! Ki yi hakuri don Allah”.
Ta yi ajiyar zuciya sannan ta fita. Allah kadai ya san abin da take sakawa da warwarewa a zuciyar nan tata. Mami na son ‘ya’yanta matuka, tana kishinsu irin kishin nan mara amfani, wanda ya kimsa mata tunanin cewa da akidar cewa ba za ta bari su auri wadanda suke mutuwar so ba, sai wadanda ke son su, don kar su rabata da su.
Irin ‘yan’uwansu su Hibbah, Nabila da Radhiyyah diyar aminiyarta Dacta Halima wadda ta ki auren minister saboda mahaukaciyar soyayyar da take yiwa Khalipha.
Mami na da wannan kudurin cikin ranta tuni, wanda kuma take da yakinin ko za ta yi yawo tsirara ne sai ta cika shi. Saboda masifar son da take wa ‘ya’yanta.
****