Sashe 13
Rayuwar Rayhana Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Khalipha Mansur, zaune a ofishinsa yana shigar da wasu sakonni cikin kwamfuta zuwa Nigerian Embassy Accra (Ghana). A kan zuwan Ghanain President (Rawlings of Ghana), wanda zai zo Nigeria cikin satin ya haura Philippines daga Nigeria suka samu matsalar visa za su fito daga kasar Kenya.
Haka nan ya ji aikin ya gundireshi. A dan tsukin nan tunda ya dawo daga gida, ya rasa gane kansa, ya kasa gane me ke damunsa.
Gaba daya ya tattaro hankalinsa da tunaninsa wuri daya. Ya zubawa tafin hannunshi ido, a hankali kuma ya kai shi hancinsa, still kamshin Escada Sentiment yana nan bai gushe ba, domin ko da ya zo wanka bai yarda ya wanke hannun ba, kada ya daina kamshin turaren RAYHANAH.
Khalipha, duk da cewa yana kan gabar kuruciyarsa, kuma a kan matakin da babu macen da ba za ta so shi ba. To fa ba kowacce mace yake kallo da kima ba har ya taba yiwa kansa sha’awar aurenta, mata iri-iri kam ya yi mu’amala dasu tun zamanin yana karatu, anyi abokai cikinsu an kuma yi ‘yammata, sai dai kuma babu wacce mu’amalarsu ta kai labari tsahon shekara daya za ayi hannun riga, don shi bai yarda yana neman yarinya wani ma yana nemanta ba, daga ranar da ya gane hakan duk son da yake mata ya barta kenan har abada.
Hibba kuwa da Hakimi ke son ya aura, har ta gaji da jiransa ta kama dahir, yanzu haka har an sa mata rana. Saboda tamaula da hankalin da yake mata.
Da fari ya ce karatu, ta jira shi ya karasa, ya dawo ya ce Bautar Kasa. Nan ma ta jira shi. Sai kuma ya dawo ya ce sai ya fara aiki, ta jira shi har ya samu. To fa kuma tunda ya fara aikinsa, bai kara bi ta kanta ba, ita kuma ta ga ba rasa manema ta yi ba zai sa ta tsofe a gida alhalin kuma ba shi da niyyar auren ta. Don haka ta yiwa kanta ludufi ta dauki na damo, ta bar Nabilah da koshin wahala......
Yau shekara guda kenan da kammala karatunsu amma tana nan tana jiran Ya Himu, wanda tunda ya cilla kafa a Chicago ba a kara jin duriyarshi ba, ko waya ba sosai yake yi da jama’a ba, idan ya gaisa da Hakimi sai ya ce a gai da kowa.
Sannan ba shi da takamaimiyar lambar waya, wani zubin ma a bakin hanya zai tsaya ya sa (credit card) dinsa a commercial ya kira wanda ya ga dama ya zare abinsa.
Kowa na kokari a kan Nabilah ta yi hakuri da Ibraheem amma sai tasa musu kuka. Hajiya Karima kan ce, “Nabila ki yiwa kanki fada ki zabi daya cikin masu sonki ki aura tun tauraruwarki ba ta dishe ba.
Kuruciyar ‘ya mace ta dan lokaci ce, shekarunki ashirin da bakwai ga kwalin digiri ga na master, kina tunanin idan Ibrahim ya dawo yadda yake ji da kuruciyar nan zai aure ki? Wallahi shi a lokacin ne zai fara samartakarsa, Juma’ar da za ta yi kyau tun daga Laraba ake gane ta”.
Nabila sai dai ta hura hanci ta zumburi baki, ko me za a ce in dai a kan Himu ne ta bayan kunnenta yake wucewa.
Khalipha ya yi baya da lallausar kujerarsa, ya bi jikinta ya kwanta ya lumshe ido. Abubuwa da yawa ke sawa ya so mace, amma ba kyan fuska da kyale-kyale ba, dukiya ko zuzzurfan ilimi. Yana son mace wadda ta san kanta (mai tsare gida da rashin kula maza). Kuma yana son ta kasance mai aji ba kyakkyawar da kowanne karabiti zai biyota a dalleliyar mota ya ce yana sonta ba.
Yana son mace mai kunya, wadda ba ta iya hada ido da namiji in ba dole ba. Mai karancin magana, ba wadda za ta zauna cikin mutane ta yi ta zuba kamar ‘ya’yan kanya ba.
Baya son mai alfahari da son nuna iyawa, baya son mai gwalli da kwarkwasa, baya son wadda za ta cika fuska da jan baki, eye shadow da su maskara da hoda. Baya son wadda za ta rambada ‘yan kunnaye da sarkoki bula-bula (Barima da hudar hanci sun isa). Baya son mai hasken kanti, sai baka mai gogaggiyar fata tunda shi fari ne sol, wadda ba mai ne ya gogeta ba, irin yanayin da take ciki ne.
To amma ya hanga ya duba cikin mata bila adadin bai ga mai wadannan extraordinary characteristics din ba sai RAYHANAH, bai taba jin yana so ya yi aure ba sai yau. Ba kuma da kowa ba da ita kadai Rayhanan Baba Dacta. Hannunta kawai ya kama (by mistake) a ranar ya tuna cewa ashe shima NAMIJI ne mai bukatar mahadin rayuwa.
Lokaci daya kuma lalurar Rayhah ta fado mishi a rai LOVE HAS NO BARRIER ( soyayya bata da shinge). Hasali ma Ji ya yi lalurar tace tun farko ta dasa tausayin ta a zuciyarsa, wanda yayi ta rikida har yau daya bayyana ainahin kalarsa; daga tausayi zuwa kauna.
Lalurar ce kuma har ila yau, da tsantsar hakurin ta akanta da komai ma na rayuwa ta sa ya kara sonta da tausaya mata. Ya ji wani bangare na zuciyarsa na gaya masa kai kadai ne za ka aure ta ba tareda lalurar tat a dame ka ba, ka zauna da ita cikin kowanne hali. Tana da lafiya ko bata da lafiya.
Ka tallafi maraicinta, ka tallafi kanka ta hanyar samarwa zuciya abin da take so, in addition ka samawa ‘ya’yanka uwa ta gari, ka kuma mallaki ragamar rayuwarta da ita kanta Rayhanah.
Ya lumshe ido a hankali ya koma ya jingina da kujera.
****
Haka nan ya ji aikin ya gundireshi. A dan tsukin nan tunda ya dawo daga gida, ya rasa gane kansa, ya kasa gane me ke damunsa.
Gaba daya ya tattaro hankalinsa da tunaninsa wuri daya. Ya zubawa tafin hannunshi ido, a hankali kuma ya kai shi hancinsa, still kamshin Escada Sentiment yana nan bai gushe ba, domin ko da ya zo wanka bai yarda ya wanke hannun ba, kada ya daina kamshin turaren RAYHANAH.
Khalipha, duk da cewa yana kan gabar kuruciyarsa, kuma a kan matakin da babu macen da ba za ta so shi ba. To fa ba kowacce mace yake kallo da kima ba har ya taba yiwa kansa sha’awar aurenta, mata iri-iri kam ya yi mu’amala dasu tun zamanin yana karatu, anyi abokai cikinsu an kuma yi ‘yammata, sai dai kuma babu wacce mu’amalarsu ta kai labari tsahon shekara daya za ayi hannun riga, don shi bai yarda yana neman yarinya wani ma yana nemanta ba, daga ranar da ya gane hakan duk son da yake mata ya barta kenan har abada.
Hibba kuwa da Hakimi ke son ya aura, har ta gaji da jiransa ta kama dahir, yanzu haka har an sa mata rana. Saboda tamaula da hankalin da yake mata.
Da fari ya ce karatu, ta jira shi ya karasa, ya dawo ya ce Bautar Kasa. Nan ma ta jira shi. Sai kuma ya dawo ya ce sai ya fara aiki, ta jira shi har ya samu. To fa kuma tunda ya fara aikinsa, bai kara bi ta kanta ba, ita kuma ta ga ba rasa manema ta yi ba zai sa ta tsofe a gida alhalin kuma ba shi da niyyar auren ta. Don haka ta yiwa kanta ludufi ta dauki na damo, ta bar Nabilah da koshin wahala......
Yau shekara guda kenan da kammala karatunsu amma tana nan tana jiran Ya Himu, wanda tunda ya cilla kafa a Chicago ba a kara jin duriyarshi ba, ko waya ba sosai yake yi da jama’a ba, idan ya gaisa da Hakimi sai ya ce a gai da kowa.
Sannan ba shi da takamaimiyar lambar waya, wani zubin ma a bakin hanya zai tsaya ya sa (credit card) dinsa a commercial ya kira wanda ya ga dama ya zare abinsa.
Kowa na kokari a kan Nabilah ta yi hakuri da Ibraheem amma sai tasa musu kuka. Hajiya Karima kan ce, “Nabila ki yiwa kanki fada ki zabi daya cikin masu sonki ki aura tun tauraruwarki ba ta dishe ba.
Kuruciyar ‘ya mace ta dan lokaci ce, shekarunki ashirin da bakwai ga kwalin digiri ga na master, kina tunanin idan Ibrahim ya dawo yadda yake ji da kuruciyar nan zai aure ki? Wallahi shi a lokacin ne zai fara samartakarsa, Juma’ar da za ta yi kyau tun daga Laraba ake gane ta”.
Nabila sai dai ta hura hanci ta zumburi baki, ko me za a ce in dai a kan Himu ne ta bayan kunnenta yake wucewa.
Khalipha ya yi baya da lallausar kujerarsa, ya bi jikinta ya kwanta ya lumshe ido. Abubuwa da yawa ke sawa ya so mace, amma ba kyan fuska da kyale-kyale ba, dukiya ko zuzzurfan ilimi. Yana son mace wadda ta san kanta (mai tsare gida da rashin kula maza). Kuma yana son ta kasance mai aji ba kyakkyawar da kowanne karabiti zai biyota a dalleliyar mota ya ce yana sonta ba.
Yana son mace mai kunya, wadda ba ta iya hada ido da namiji in ba dole ba. Mai karancin magana, ba wadda za ta zauna cikin mutane ta yi ta zuba kamar ‘ya’yan kanya ba.
Baya son mai alfahari da son nuna iyawa, baya son mai gwalli da kwarkwasa, baya son wadda za ta cika fuska da jan baki, eye shadow da su maskara da hoda. Baya son wadda za ta rambada ‘yan kunnaye da sarkoki bula-bula (Barima da hudar hanci sun isa). Baya son mai hasken kanti, sai baka mai gogaggiyar fata tunda shi fari ne sol, wadda ba mai ne ya gogeta ba, irin yanayin da take ciki ne.
To amma ya hanga ya duba cikin mata bila adadin bai ga mai wadannan extraordinary characteristics din ba sai RAYHANAH, bai taba jin yana so ya yi aure ba sai yau. Ba kuma da kowa ba da ita kadai Rayhanan Baba Dacta. Hannunta kawai ya kama (by mistake) a ranar ya tuna cewa ashe shima NAMIJI ne mai bukatar mahadin rayuwa.
Lokaci daya kuma lalurar Rayhah ta fado mishi a rai LOVE HAS NO BARRIER ( soyayya bata da shinge). Hasali ma Ji ya yi lalurar tace tun farko ta dasa tausayin ta a zuciyarsa, wanda yayi ta rikida har yau daya bayyana ainahin kalarsa; daga tausayi zuwa kauna.
Lalurar ce kuma har ila yau, da tsantsar hakurin ta akanta da komai ma na rayuwa ta sa ya kara sonta da tausaya mata. Ya ji wani bangare na zuciyarsa na gaya masa kai kadai ne za ka aure ta ba tareda lalurar tat a dame ka ba, ka zauna da ita cikin kowanne hali. Tana da lafiya ko bata da lafiya.
Ka tallafi maraicinta, ka tallafi kanka ta hanyar samarwa zuciya abin da take so, in addition ka samawa ‘ya’yanka uwa ta gari, ka kuma mallaki ragamar rayuwarta da ita kanta Rayhanah.
Ya lumshe ido a hankali ya koma ya jingina da kujera.
****