← Book details Nawaff Part 1 Complete Hausa Novel.txt Local reading mode
READING PART 7 OF 51

Sashe 7

Nawaff Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read

Abangaren samarin nan kuwa tunda suka fita suke santin k'yawu irin na yasmeen, ixiddin ya ce, "hisham gafa hanya mai sauk'i ta d'aukar fansa, dan maida murtani ga abokin dambe ba laifi bane.
Hashim ya ce, "gsk yarka iziddin, hisham yakamata ka rama abinda faisal yayi maka, dan wannan itace dama ta k'arshe dazaka iya samu, karka bari ta k'ub'uce maka.
Kuma tabbas idan muka aikata, munyi jihadi, dan na lura yarinyar kamilace, bata dace da d'an iska irin faisal ba.
Hisham ya dafa kafad'un abokan nasa, ya ce, "karku damu abokaina, kudai kusaka idanu kusha kallo, amma tabbas gsky kuka fad'a yasmeen kamilallaiyar mace ce, inhar ta airi faisal d'an giya manemin mata tofa tabbas ta cutu.
Dan haka ku biyoni domin kallon wasan, kud'auka nine zanyi wining, faisal zai samu game over, yafad'a yana wata dariyar mugunta.
Na ce, "tofa ana wata ga wata, to bamusan waye keda nasaraba saimunyi bulayiiiiiiiii........................✍🏻

©2016

💞Bilyn Abdul💞
💞Mrs Abdus'salam💞
💞LUV U OLL MY FAN's💞
[1/12, 8:54 PM] mrs bilkisu: ☆☆☆☆☆☆☆
🎾 NAWAFF 🎾
☆☆☆☆☆☆☆

NA BILKISA IBRAHIM💞

Page👉🏻13

.....A yaune aka kawo gagarumin lefen yasmeen, gsky su hajiya jummai sun taka rawar gani, dakaga lefen zakasan anyishine domin d'an gata.
Tunda lefen ya iso yasmeen tashige d'aki tana kwasar kuka, dukkan mutan gidan idan ka kallesu zaka gano basa cikin walwala, saidai suna iya bakin k'ok'arinsu wajen yin fara'a koda iya ta hak'orice.
Bayan masu kawo lefe sun tafi umma ta shiga d'akin yasmeen dan tasan tana cikin damuwa, cikin bargo ta tarar da ita kuwa tanata rawar sanyi da'alama bata cikin k'oshin lafiya.
Cikin hanzari umma ta k'arasa gareta ta yaye bargo, wani irin zafi taji ajikin yasmeen ga rawar sanyi.
Ba ab'ata lokaciba wajen kaita asibiti taga likita, da haka aka cigaba da hidimar biki, wanda gidansu faisalne kawai suke farinciki.
A yaune kuma faisal ya diro k'asarsa ta haihu, iya yensa sunyi farinciki da ganinsa, babu abinda ya canja arayuwarsa sai lalacewa daya k'ara yi, saidai zamu iyacewa ya k'ara girma da wayewa mara amfani.
Bayan ya huta da yamma ya aiki balarabe wai yaje ya d'akko masa yasmeen, lamarin yabama balarabe mamaki, ya za'ayi ace budurwa ce zatazo gidan saurayi???, haka dai yaja mota yatafi yana waswasi.
Yaro yasamu ya aika saboda gidan yau akwai mata dayawa, anata hada2r biki.
Yasmeen tafito dan taga wake kiranta, daka ganta zaka gano matsananciyar damuwar dake tare da ita.
Takarasa wajen balarabe suka gaisa, ta ce, "balarabe wayake nemana.
Ya ce, "dama ogane ya ce, "nazo nad'aukeki.
kad'aukeni kuma??, to kakaini ina??.
Wai na kaiki gidansu yanacan yana jiranki.
Wata uwar harara ta sakarma balarabe kamar shine da laifin, ta ce, "kaje kasanar masa na ce, "bazan zoba, tana gama fad'a tashige gida.
Balarabe baiga laifintaba dan hakan datayi shine dai2, ta burgeshi wlhy.
Amma dayaje saiya cema faisal ya je bata gida, wai sunfita da k'awayenta.
Hannu kawai yad'agama balarabe dan gsky yaso yasmeen tazo, wayarsa ya d'auka yakira wata number, ana d'agawa ya ce, "su had'u agidan daya nuna mata d'azu.
Tashi yayi ya shirya ya d'auki makullin mota ya fice, kai tsaye gidanshi yanufa inda za'akai yasmeen, babu k'arya gidan ya had'u, anzuba komai amarya kawai ake jira, anan ya tarar da wata kod'ad'iyar mace wadda bilicin yayma k'awanya. 😔lamarin yayi matuk'ar b'ata mini rai, lallai yasmeen taga takanta, dan nakula faisal bunsurune, inagama yasa ad'akko masa yasmeen d'inne dan ya........hummm shege d'an iska.
Tun afalo suka fara k'auce hanya, bak'in cikine yasani nabaro gidan dan bazan iya ganiba.

Haka biki yacigaba da gudana, yasmeen dai tak'i yarda faisal ya ganta, yabi duk hanyoyin dazai ganta amma ta rufe masa k'ofa, daga k'arshe abin ya b'ata masa rai ya tattarata ya watsar, dan yasan nanda wani d'an lokaci zata kasance agidansa dole, kuma duk wulak'ancin datake masa saiya rama.

NAWAFF
a yaune Nawaff ya sauka Najeria saboda kwallo dazasu bugama Najeria, wanda yakasance na Africa, kuma Najeria itace mai masaukin bak'i.
Mas'ud da Abdallah da Anwar ne sukaje tarbosa, sunyi farin cikin ganinsa, shima yayi farincikin ganinsu.
Mas'ud ya ce bro's kudai ba'a ganinku saida dalili, turai ta kwace mana kai gaba d'aya.
Nawaf yay dariya, su sun isa su kwace ni ahannunku, kawaidai nad'an lokacine, amma ni nakune.
Abdallah ya ce, "yaya watanka 6 fa kenan da barin k'asarnan, yanzuma badan zakuyi wasannan ba dabazamu gankaba fa sai hutun k'arshen shekara.
Nawaf yay murmushi kawai batarda ya ce komaiba.
sunata hirarsu har suka isa gida, momcy ta tarbi Nawaf cikin farinciki, Nawaf ya narke murya cikin shagwab'a ya ce, "momcy nayi missing naku wlhy, ina papa ko yana wajen aiki ne??.
Yana can momcy tafad'a, amma nasan yana hanyar dawowa, yakamata kadaina shagwab'a haka nan modeebbo, kagirma fa.
Su Anwar suka tuntsure da dariya, ya wurga musu harara, sannan yadawo da kallonsa wajen momcy ya ce, "momcy ni ban wani girmaba.
Momcy ta shafa kansa tana dariya, ta ce, "ina mas'ud wai?, Nawaf ya ce, "ya koma asibiti, dan yace yanada aiki sosai.
ALLAH sarki Mas'ud sarkin k'ok'ari kenan. momcy tafad'a.
Nawaf ya mik'e momcyna barinaje nayi wanka jikina duk yayi tsami, to abincin fa?, mom sainayi wanka sannan, yanzu zan dawo, dan nayi missing d'in girkinki.
Momcy tayi dariya to aii yau zakaci kamore.

YASMEEN.
rana bata k'arya inji masu iya magana, yaudai aka d'aura auren faisal da yasmeen, d'aurin auren yatara manyan mutane masu fad'a aji ak'asarnan, saka makon babansa sanannen mutumne, kuma d'an siyasa.
Sai dai abinda yabani mamaki duk d'unbin taron jama'ar nan babu ango awajen.
Ana cikin shafa addu'ar k'atshe saiga faisal tamkar mahaukaci dagashi sai wando iya guywa da riga mara hannu, kutsa kai yake kawai cikin jama'a, har ya isa gabn liman, ya tsaya k'erere👯yana wurga idanunsa dasukayi jajur.
Alhaji buba yamik"e da sauri yana tambayar d'an nasa lafiya???.
Faisal ya yamutse fuska ta reda fad'in abba and'aura aurennan kuwa??.
Alhaji buba ya ce, "emana faisal and'aura yanzu kazama ango.........hannu yad'aga wa mahaifinsa ya ce, "to abba awarwareshi yanzunnan.
😳Alhaji buba yazaro idanu faisal kamarya a warware??, cikin k'araji faisal ya ce, "kamar yanda aka d'aura narantse da sarkin dake busamin numfashi bazan zauna da karuwaba, dan haka sai an warware shi.
Gaba d'aya gurin yayi tsit ana kallon sarautar ubangiji.
🎤abin maganar dake hannun liman faisal ya kwace, yajuya yana kallon mutane, ya ce, "kamar yanda kuka shaida and'aura auren faisal da yasmeen, to haka nakeso ku shaida faisal ya saki yasmeen saki uku!!!!!!!!!!!!!!!!!.
Gaba d'aya wajen akad'au "INNALILAHI WA INNA ILAIHIRRAJI'UN....................✍🏻

Hummm nikaina dabana son wanga aure, saida na girgiza domin jin furicin faisal!!!.

💞Bilyn Abdul💞
💞Mrs Abdus'salam💞
💞 LUV U OLL MY FAN's💞
[1/12, 8:54 PM] mrs bilkisu: ☆☆☆☆☆☆☆
🎾 NAWAFF🎾
☆☆☆☆☆☆☆

NA BILKISA IBRAHIM💞

Page👉🏻14

.....Cikin b'acin rai Alhaji buba ya wankama faisal mari, faisal yadafe kumatu yana kallon baban nasa, mahaifin yasmeen kuwa fad'uwa yayi, dukda baya son auren abin yay masa matuk'ar ciwo.
Gurin ya rud'e da surutai, kowa yana fad'ar albarkacin bakinsa, zuwa sannan an yayyafama abban yasmeen ruwa ya farfad'o, ya fashe da kuka yana fad'in yanzunan irin cin mutuncin daza ayimin kenan saboda anganni talaka, banida komai bani da kowa.
Wani dattijo naga ya mik'e tareda dafa Abban yasmeen, ya ce, "kanada kowa malam, kuma ka kwantar da hankalinka, indai ka amince zan d'aurama d'ana aure da d'iyarka yanzunnan.
Abba yabi dattijon da kallo, gsky ne dattijon mutumne mai kamala da dattako, yatabbata bazayayi dana sani da tayinsaba.
Liman ya ce, "malam ka amince na tabbata bazaka tab'a dana sanin hakanba, Alhaji sa'eed mutumin kirkine, yakuma bama d'ansa cikkiyar tarbiya.
Abban yasmeen ya ce, "shikenan nabashi!!, ALLAH yasa haka yafi alkairi.
Liman da dattijo suka amsa da amin.
Har mutane sun fara tafiya akayi sanarwa adawo za'a sake d'aura aure, mutane kam sun amsa kira, dandanan gurin yay tsit aka nutsu ana jiran mizaije yadawo.
Nantake dattijo ya ajiye sadaki dubu hamsin, nakasa kunne naji dawa aka d"aura amma hayaniyar mata dake cikin gida yahanani, dole na hak'ura.
Bayan angama d'aurin aure komai ya natsa, zuwa sannan labari yashiga cikin gida, dafarko umma taji bak'inciki, amma da'aka sanar da ita k'arshen al'amarin saitaji farinciki mara musali, nutsuwa da annashuwa suka bayyana saman fuskarta.
Ammafa nakasa gano muku amarya bare nasan halin datake ciki.

GIDANSU NAWAFF.
papa yashiga gidan fuskarsa cikeda fara'a, momcy ta taryeshi, bayan yasha ruwa ta ce, "Alhaji lfy dai naganka cikin farinciki haka??.
Papa yay murmushi har wushiryarsa ta bayyana, ya ce, "ummul'khairi ina cikin farinciki yau, kuma kema idan kikaji nasan zaki tayani farin ciki, kamar yanda nagaya miki zanje d'aurin aure to daga can nake, bud'e kunnanki kisha labari.
Momcy tayi dariya tareda fad'in ina sauraraenka Alhaji.
Papa yagyara zama tareda zayyane mata abinda yafaru, yad'ora da fad'in wlhy mutumin yabani tausayi, dan idan nine akayima haka, to idan na suma bazan far fad'oba.
Dan haka atake agurin nabiya sadaki aka maida d'aurin auren akan MODEEBBO!!!!.
momcy tad'an zaro idanu, Alhaji modeebbofa kace??, papa ya gimtse fuska ya ce, "ashe kin jini!!.
Ta ce, "amma kana ganin baza'a samu matsala a wajen modeebbo ba??, papa ya kwantar da kansa ajikin kujera, ya ce, "aii bana fata na haifi d'an dazai bijirema umarnina, ko mas'ud nace na d'aurama aurennan dole ya amince bare NAWAF.
momcy ta ce, "kayi hak'uri Alhaji bahaka nake nufiba wlhy, ina farin ciki da umarninka, ALLAH kuma yasanya alkairi, wlhy tun kafin naga yarinyar ma tashiga raina, kuma ina k'aunarta tamkar yanda nakeson su modeebbo.
Papa yay murmushi yana tashi zaune, yakama hannun momcy yana murzawa, ngd ummul'khairi, ngd da had'in kan dakika bani, inaso ki taimaka mini wajen fahimtar da modeebbo.
Momcy ta zare hannunta daga nashi tana fad'in Alhaji kar yarannan su shigo su gammu.
Murmushi papa yayi batareda ya ce, "komaiba, waya ya d'auka yana kiran Nawaf!.
Nawaf yana kwance ad'akinsa yanaso yay barci, dan yau zaitafi abuja da yamma, ya mik'a hannunsa yana laluben wayarsa datake wringing, da sauri yamik'e zaune dan ganin papane yake kiransa.
Cikin ladabi ya ce, "papa barka da rana, barka kadai papa yafad'a, ya ce, "kana inane??, cikin ladabi ya ce, "ina d'akina papa!.
To kazo kasameni.
To Nawaf yafad'a tareda mik'ewa yafito domin amsa kiran papa.
Chapter 7 · 0% Book details